Saturday, 31 March 2018

HIKAYAR WASU TSUNTSAYE

HIKAYAR MACIJI DA TSUNTSAYE


Sadiq Tukur Gwarzo, RN.

Wannan hikayar shahararra ce acikin littafin hikayoyi na 'Kalila wa Dhimma', musamman yadda aka rinka amfani da ita wajen koyar da yara masu jiran sarauta hikimomin kuɓuta daga zaluncin duk wani azzalumi.
  Hikayar tace:-
  A saman wata babbar bishiyar Kuka, anyi wasu tsuntsaye guda biyu waɗanda ke rayuwa acikin shekarsu dake saman wannan bishiya.
  Sai dai kuma akwai wata damuwa tattare da waɗannan tsuntsaye.
  Damuwar itace, duk sanda suka kyankyashe kwayayensu sai wani maciji ya zo ya shanyesu, shikuwa a kasan bishiyar yake rayuwa cikin  wani kogo.
  Kullum haka, kullum haka.
  Rannan sai sukayi shawarar suje su sanar da Mallam Dila domin ya basu shawarar hanyar kuɓuta daga wannan kunchi da suke ciki.
  Bayan sun same shi suke shaida masa irin zaluncin da maciji keyi musu gashi sun rasa yadda zasuyi.
  Dila yayi ajiyar zuciya, sannan yace "kada ku damu, komai karfin azzalumi, kaskantaccen abu yana iya cin galaba akansa cikin hikima"
  Yaci gaba da cewa "saboda haka, shawara ɗaya dazan baku shine, ku shiga cikin gari kuyi duba ga gidan dayafi kowanne arziki da kuma dakaru, sannan ku lura da abu mafi daraja wanda akayi sakaci dashi, sai ku ɗauko shi kurinka tafiya a hankali a hankali, da kunzo bakin kogon maciji sai ku wurgar dashi kuyi naku wuri.
  Tsuntsaye sukayi godiya sannan suka tashi firrr! zuwa cikin gari domin aiwatar da shawarar mallam Dila.
   Ai kuwa suna ta zagaya gari, sai suka hango 'yar sarkin garin tana wanka a cikin wani karamin tafki, ga abin wuyanta yana ta walwali ta ajiyeshi a gefe saman kayan sanyawarta, sai kuma dakaru suna ta shige da fice.
  Kwatsam sai gani akayi tsuntsuwa ɗaya tayi kasa-kasa tare da wuftar wannan abin wuya da bakinta, sannan ta tashi sama a hankali tana mai karkaɗa fuka-fukanta.
   Koda faruwar haka sai hankalin 'yar sarki da dakaru yakai gareta. Yar sarki ta daka musu tsawa da cewar subi bayanta su karɓo mata abin wuyanta.
  Ai kuwa a haka tsuntsuwar nan ta rinka janyo dakaru, ta sauka acan, da zarar sun runtumo gareta sai ta tashi, ta sake sauka a wani wurin, a haka har tazo bakin kogo sannan ta wurgar dashi.
  A wannan lokaci maciji nata sharar bacci abinsa, yaci abinci yayi hani'an, jira yakeyi dare yayi yahau sama don kara farauto kwan tsuntsaye kamar yadda ya saba.
   Karar wurgar da abin wuya kuwa sai ya tashe shi.
  Koda ya hango abu mai walwali sai yayi sha'awar zuwa don ganin ko menene.
  Yana daf da fitowa dakaru suka iso wurin suna ta haki, ɗaya daga cikinsu ya mika hannu zai ɗauki abin wuya amma sai ya jiyo motsi, dubawarsa keda wuya sai yaga maciji na fitowa gareshi.
  Nan take kuwa waɗannan dakaru suka rufar masa da duka da sanduna har sai da suka halaka shi, sannan suka ɗauki abin wuyan gimbiya suka tafi abinsu.
  Tun daga wannan rana tsuntsaye suka samu kwanciyar hankali, domin babu mai hanasu sakewa.

HIKAYAR SARKIN HINDU BHOJ

GA KOWANNE MA'ABOCIN ILIMI, AKWAI NAGABA DASHI: HIKAYAR SARKI BHOJ NA HINDU

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO, RN.

Kasar Indiya nada mutane masu karancin ilimi matuka a yanzu. Wannan ne yasa 'yan siyasa da sauran masu kumbar susa suke abinda suke so, saboda yawan mabiyansu basu san abinda doka tayi tanaji akan hakkokin su na 'yan kasa ba.
   Sai dai kuma, an taɓa yin wani lokaci da jimawa a tarihin kasar Indiya wanda sai an sha matukar wahalar bincike kafin a samu mutum kwalli ɗaya wanda bai iya rubutu da karatu ba, bai kuma kiyaye hikimomi a kirjin saba.
   Anyi wannan zamanin ne a lokacin mulkin sarki Bhoj na daular Malwa dake tsakiyar Indiya a wuraren shekara ta 1010-1055 miladiyya.
   Ance a wancan lokaci, duk talaucin mutum, zaka sameshi yana iya karanta littafin addininsu mai sun Sanskrit.
   Sarki Bhoj ya kasance mai bauta ne ga ubangiji Saraswati, kuma shi mutum ne mai matukar ilimi, da kuma son ilimi.
 Shi gwanin karance-karance ne, da rubuce-rubuce, musamman a fannonin falsafanci, kimiyya, fasaha, wake-wake, tarihi da sauransu.
  Sarki Bhoj ya wallafa littatafai kimanin 35 waɗanda har zuwa yau ana amfani dasu a kasar ta Indiya. A ciki akwai misalin 'Champu Ramayan' wanda yake kunshe da tarihi cikin wake, da kuma Rajniti Shastra mai ɗauke da ilimin kere-kere da Shringar Prakash mai ɗauke da kayatattun wakoki..
   Wata rana sai wani mai ilimi yazo ziyara ga Sarki Bhoj a fadarsa dake birnin Dhar, to amma kamar yadda kasar hausa ta kasance abaya, babu otal na saukar baki, don haka sai sarkin ya umarci wani bafadensa mai suna Amatya akan ya zagaya cikin gari ya nemi mutum jahili ya umarceshi daya fita daga gidansa dashi da iyalinsa domin baiwa wannan bako masauki.
   Amatya ya shiga gari yana ta lalube, kwatsam sai gashi gaban wani mutum masaki, yana ta saka a kofar gidansa.
  "da ganin wannan bagidaje ne", Amatya ya raya a ransa. Sannan ya gabata gareshi yana muzurai tare da faɗa masa umarnin sarki Bhoj.
  Koda wannan masaki yaji haka, sai baicewa ɗan aike uffan ba, ya kamo hanya zuwa fada.
 Da zuwansa ya faɗi gaban sarki yayi gaisuwa sannan ya fara rero wasu baitoci daya haddace a cikin littafin addininsu Sanskrit.
  Bayan ya gama, sai kuma ya shiga rera wata wakar, yana mai cewa:-
  Ya Sarki! ni kaina na wallafa wakoki, amma basu yi kyawu ba.
  Na tabbata, da himmatuwata, sam bazan rasa baiti ba.
  Ya kai Shugaba, takalman wanene aka yiwa ado da kambun tsoffin sarakuna?
  Ina mai jiran umarninka, shin rubutun wakoki ne ya zamar mini wajibi, ko saka tufafi, ko kuwa barin gidana da masarautar ka baki ɗaya..?
  Sarki da duk wanda ke wannan fada ya tsinkayu da hikimar wannan mutumi, musamman duba da cewar sigar dake gareshi ta kidahuman mutane ne marasa ilimi. Don haka sarki ya sauya shawara akan saukar bakonsa, yasa a nema masa wuri acikin gidansa ya kwana, masaki kuma yayi masa kyauta ya sallame shi.
(Ana lissafa wannan a matsayin yadda indiyawa ke fafutikar kwatar 'yancinsu tun a karni na goma sha ɗaya, da kuma yadda sarakuna ke baiwa mabiyansu damar shigar da koke a kodayaushe).
  Rannan kuma har ila yau, sarki Bhoj ya sake yin wani bakon mai Ilimi daga wata masarauta, sai suka fita kilisa bisa dokuna suna masu tattauna mas'alolin ilimi, basu ankara ba har sukayi nisa da gida.
  Don haka sai suka juyo da nufin komowa gida, amma sai hanyar da sukabi tun da fari ta ɓace musu.
  Suna dai ta tafiya basu san inda suke dosa ba, sai gasu kusa da wani ɗan kauye.
  Tun kafin su shiga ciki sukaci karo da wata tsohuwa, da alama tana cikin matalautan mutane duba da tufafin jikinta.
  Sai suka tsayar da ita suka tambayeta da cewa "Ya wannan tsohuwa, shin ina wannan hanyar take tafiya ne?"
  Tsohuwa tace "Wannan hanyar babu inda take tafiya, anan wurin kurum take a kwance, amma mutanen da suke tafiya akanta sune ke riskar wani wuri. Don haka sai ku faɗa mini su wanene ku?"
  "Mu matafiya ne" inji sarki Bhoj cikin kaɗuwa.
  "Ai matafiya biyu ne kaɗai anan duniya, daga Rana sai wata" inji tsohuwa. "Shin su wanene ku aciki?"
  Abokin Sarki Bhoj yayi farat yace " 'yar uwa, mufa baki ne"
  Tsohuwa tace "baki guda biyu ne kachal a duniya. Na ɗaya sunansa dukiya, na biyunsa kuwa sunansa Samartaka"
  "To mu sarakuna ne" inji Sarki Bhoj.
  "Ai kuwa sarakuna biyu garemu a duniyar nan, daga sarkin sarakuna Indra, sai allan mutuwa Tama. Shin waɗanne ne ku daga ciki?" tsohuwa ta sake jefa musu tambaya.
  Sukayi shiru suna kallonta cikin mamaki, sannan sai sukace "mu.. Mutane kurum masu juriya"
   Tsohuwa tace "ai kuwa anan duniya abubuwa biyu ne kaɗai masu juriya, daga ita duniyar kanta, sai kuma mace. Ni kuwa ban ganku da lulluɓi ba"
  Sarki Bhoj yace "yar uwa, munan da kike ganin mu waliyyai ne"
  Tsohuwa tace "waliyyai biyu ne fa a duniya, daga mutumci sai hakuri."
   Sarki Bhoj da abokinsa sukayi shiru suna nazarin abinda zasu ce, domin sun ɗauki abin a matsayin farmaki ga iliminsu, don haka suka kudurci aniyar lallai sai sun kure tsohuwa.
  Abokin sarki Bhoj yace "yar uwa, mufa masu balaguro ne"
  Tsohuwa tace "sam bakuyi kama da masu balaguro ba" tana mai girgiza kanta alamar rashin amincewa.
  Sannan ta kara da cewa "ai ruhi da ganyen bishiya ne kaɗai masu yin balaguro.. Ko akwai ɗaya a cikinku?"
  "to munan mun kasance talakawa ne" inji sarki Bhoj.
  "matalauta biyu ne a duniya. Na ɗaya shine ɗan marakin da akayiwa reno yana jiran yanka, na biyunsu kuwa itace budurwar da aka sanya a lalle" inji tsohuwa.
   Abokin sarki Bhoj yace "Haka ne, amma a zahiri mu fasihai ne"
  Tsohuwa tace "ai fasihai biyu garemu duk duniya, daga Hatsi sai Ruwa, shin a wanne babin kuke?"
  Ran sarki Bhoj ya sosu, amma dai ya kanne, yace " to munji, kinyi nasara akanmu, mun kuma karɓi faɗuwa"
  Sai tsohuwa ta sake kada baki tace "mutanen da akayi nasara akansu biyu ne anan duniya. Na ɗaya shine wanda yayi rance, har ya zamana bashi yayi masa katutu. Na biyu kuwa shine mahaifin budurwa maras ɗa'a. Shin meya hanaku tun da fari ku sanar mini gaskiyar ko su wanene ku?"
  Sarki Bhoj da abokinsa sukace "to me kike son muce ne? Ai ya kasance kamar bamu san komai ba, kece mafi sanin mu duka"
  Tsohuwa tayi murmushi, sannan tace "dukkan ku na lura kuna takama da dukiya gami da ilimi, ni kuwa nayi muku haka ne domin na nuna muku akwai abubuwan da kuka rasa sani na daga ilimi, amma tunda fari na gane cewar wannan Sarki Bhoj ne, wannan kuma bakon sane.."
  Daga nan sai ta nuna musu hanyar da zata kaisu birnin Dhar.
  Sarki Bhoj da abokinsa sukayi godiya ga wannan tsohuwa mai ilimi bisa darasin data koya musu, lallai sun gamsu da cewar akwai mutanen da suke kallo a matsayin kaskantattu amma sun ɗarasu sanin hikimomi, don haka har suka isa gida firarta kurum sukeyi.
 
SUBHANAKA LA ILMA LANA ILLA MA ALLAMTANA..

Thursday, 15 March 2018

HIKAYAR SARKI BHOJ NA HINDU

GA KOWANNE MA'ABOCIN ILIMI, AKWAI NAGABA DASHI: HIKAYAR SARKI BHOJ NA HINDU

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO, RN.

Kasar Indiya nada mutane masu karancin ilimi matuka a yanzu. Wannan ne yasa 'yan siyasa da sauran masu kumbar susa suke abinda suke so, saboda yawan mabiyansu basu san abinda doka tayi tanaji akan hakkokin su na 'yan kasa ba.
   Sai dai kuma, an taɓa yin wani lokaci da jimawa a tarihin kasar Indiya wanda sai an sha matukar wahalar bincike kafin a samu mutum kwalli ɗaya wanda bai iya rubutu da karatu ba, bai kuma kiyaye hikimomi a kirjin saba.
   Anyi wannan zamanin ne a lokacin mulkin sarki Bhoj na daular Malwa dake tsakiyar Indiya a wuraren shekara ta 1010-1055 miladiyya.
   Ance a wancan lokaci, duk talaucin mutum, zaka sameshi yana iya karanta littafin addininsu mai sun Sanskrit.
   Sarki Bhoj ya kasance mai bauta ne ga ubangiji Saraswati, kuma shi mutum ne mai matukar ilimi, da kuma son ilimi.
 Shi gwanin karance-karance ne, da rubuce-rubuce, musamman a fannonin falsafanci, kimiyya, fasaha, wake-wake, tarihi da sauransu.
  Sarki Bhoj ya wallafa littatafai kimanin 35 waɗanda har zuwa yau ana amfani dasu a kasar ta Indiya. A ciki akwai misalin 'Champu Ramayan' wanda yake kunshe da tarihi cikin wake, da kuma Rajniti Shastra mai ɗauke da ilimin kere-kere da Shringar Prakash mai ɗauke da kayatattun wakoki..
   Wata rana sai wani mai ilimi yazo ziyara ga Sarki Bhoj a fadarsa dake birnin Dhar, to amma kamar yadda kasar hausa ta kasance abaya, babu otal na saukar baki, don haka sai sarkin ya umarci wani bafadensa mai suna Amatya akan ya zagaya cikin gari ya nemi mutum jahili ya umarceshi daya fita daga gidansa dashi da iyalinsa domin baiwa wannan bako masauki.
   Amatya ya shiga gari yana ta lalube, kwatsam sai gashi gaban wani mutum masaki, yana ta saka a kofar gidansa.
  "da ganin wannan bagidaje ne", Amatya ya raya a ransa. Sannan ya gabata gareshi yana muzurai tare da faɗa masa umarnin sarki Bhoj.
  Koda wannan masaki yaji haka, sai baicewa ɗan aike uffan ba, ya kamo hanya zuwa fada.
 Da zuwansa ya faɗi gaban sarki yayi gaisuwa sannan ya fara rero wasu baitoci daya haddace a cikin littafin addininsu Sanskrit.
  Bayan ya gama, sai kuma ya shiga rera wata wakar, yana mai cewa:-
  Ya Sarki! ni kaina na wallafa wakoki, amma basu yi kyawu ba.
  Na tabbata, da himmatuwata, sam bazan rasa baiti ba.
  Ya kai Shugaba, takalman wanene aka yiwa ado da kambun tsoffin sarakuna?
  Ina mai jiran umarninka, shin rubutun wakoki ne ya zamar mini wajibi, ko saka tufafi, ko kuwa barin gidana da masarautar ka baki ɗaya..?
  Sarki da duk wanda ke wannan fada ya tsinkayu da hikimar wannan mutumi, musamman duba da cewar sigar dake gareshi ta kidahuman mutane ne marasa ilimi. Don haka sarki ya sauya shawara akan saukar bakonsa, yasa a nema masa wuri acikin gidansa ya kwana, masaki kuma yayi masa kyauta ya sallame shi.
(Ana lissafa wannan a matsayin yadda indiyawa ke fafutikar kwatar 'yancinsu tun a karni na goma sha ɗaya, da kuma yadda sarakuna ke baiwa mabiyansu damar shigar da koke a kodayaushe).
  Rannan kuma har ila yau, sarki Bhoj ya sake yin wani bakon mai Ilimi daga wata masarauta, sai suka fita kilisa bisa dokuna suna masu tattauna mas'alolin ilimi, basu ankara ba har sukayi nisa da gida.
  Don haka sai suka juyo da nufin komowa gida, amma sai hanyar da sukabi tun da fari ta ɓace musu.
  Suna dai ta tafiya basu san inda suke dosa ba, sai gasu kusa da wani ɗan kauye.
  Tun kafin su shiga ciki sukaci karo da wata tsohuwa, da alama tana cikin matalautan mutane duba da tufafin jikinta.
  Sai suka tsayar da ita suka tambayeta da cewa "Ya wannan tsohuwa, shin ina wannan hanyar take tafiya ne?"
  Tsohuwa tace "Wannan hanyar babu inda take tafiya, anan wurin kurum take a kwance, amma mutanen da suke tafiya akanta sune ke riskar wani wuri. Don haka sai ku faɗa mini su wanene ku?"
  "Mu matafiya ne" inji sarki Bhoj cikin kaɗuwa.
  "Ai matafiya biyu ne kaɗai anan duniya, daga Rana sai wata" inji tsohuwa. "Shin su wanene ku aciki?"
  Abokin Sarki Bhoj yayi farat yace " 'yar uwa, mufa baki ne"
  Tsohuwa tace "baki guda biyu ne kachal a duniya. Na ɗaya sunansa dukiya, na biyunsa kuwa sunansa Samartaka"
  "To mu sarakuna ne" inji Sarki Bhoj.
  "Ai kuwa sarakuna biyu garemu a duniyar nan, daga sarkin sarakuna Indra, sai allan mutuwa Tama. Shin waɗanne ne ku daga ciki?" tsohuwa ta sake jefa musu tambaya.
  Sukayi shiru suna kallonta cikin mamaki, sannan sai sukace "mu.. Mutane kurum masu juriya"
   Tsohuwa tace "ai kuwa anan duniya abubuwa biyu ne kaɗai masu juriya, daga ita duniyar kanta, sai kuma mace. Ni kuwa ban ganku da lulluɓi ba"
  Sarki Bhoj yace "yar uwa, munan da kike ganin mu waliyyai ne"
  Tsohuwa tace "waliyyai biyu ne fa a duniya, daga mutumci sai hakuri."
   Sarki Bhoj da abokinsa sukayi shiru suna nazarin abinda zasu ce, domin sun ɗauki abin a matsayin farmaki ga iliminsu, don haka suka kudurci aniyar lallai sai sun kure tsohuwa.
  Abokin sarki Bhoj yace "yar uwa, mufa masu balaguro ne"
  Tsohuwa tace "sam bakuyi kama da masu balaguro ba" tana mai girgiza kanta alamar rashin amincewa.
  Sannan ta kara da cewa "ai ruhi da ganyen bishiya ne kaɗai masu yin balaguro.. Ko akwai ɗaya a cikinku?"
  "to munan mun kasance talakawa ne" inji sarki Bhoj.
  "matalauta biyu ne a duniya. Na ɗaya shine ɗan marakin da akayiwa reno yana jiran yanka, na biyunsu kuwa itace budurwar da aka sanya a lalle" inji tsohuwa.
   Abokin sarki Bhoj yace "Haka ne, amma a zahiri mu fasihai ne"
  Tsohuwa tace "ai fasihai biyu garemu duk duniya, daga Hatsi sai Ruwa, shin a wanne babin kuke?"
  Ran sarki Bhoj ya sosu, amma dai ya kanne, yace " to munji, kinyi nasara akanmu, mun kuma karɓi faɗuwa"
  Sai tsohuwa ta sake kada baki tace "mutanen da akayi nasara akansu biyu ne anan duniya. Na ɗaya shine wanda yayi rance, har ya zamana bashi yayi masa katutu. Na biyu kuwa shine mahaifin budurwa maras ɗa'a. Shin meya hanaku tun da fari ku sanar mini gaskiyar ko su wanene ku?"
  Sarki Bhoj da abokinsa sukace "to me kike son muce ne? Ai ya kasance kamar bamu san komai ba, kece mafi sanin mu duka"
  Tsohuwa tayi murmushi, sannan tace "dukkan ku na lura kuna takama da dukiya gami da ilimi, ni kuwa nayi muku haka ne domin na nuna muku akwai abubuwan da kuka rasa sani na daga ilimi, amma tunda fari na gane cewar wannan Sarki Bhoj ne, wannan kuma bakon sane.."
  Daga nan sai ta nuna musu hanyar da zata kaisu birnin Dhar.
  Sarki Bhoj da abokinsa sukayi godiya ga wannan tsohuwa mai ilimi bisa darasin data koya musu, lallai sun gamsu da cewar akwai mutanen da suke kallo a matsayin kaskantattu amma sun ɗarasu sanin hikimomi, don haka har suka isa gida firarta kurum sukeyi.
 
SUBHANAKA LA ILMA LANA ILLA MA ALLAMTANA..