Monday, 10 June 2019

MAHANGA TA 8: HAUSA DAGA YANKIN ASIA

MAHANGA TA 8: HAUSA DAGA YANKIN ASIA
SADIQ TUKUR GWARZO

Wannan mahanga ta kalli kachokan ɗin harshen Hausa ne wanda Hausawa ke amfani dashi tare da yanke hukuncin cewa asalin Hausawa daga yankin Asia suke.
  Harshen Hausa dai ɗaya ne daga rukunin harsuna kimanin 250 masu suna 'Afro-Asiatic languages',  (Semito-Hamitic), waɗanda aka fi samu  a Arewaci da yammacin Afirka, Kasashen Larabawa da wasu tsibirai na yankunan Yammacin Asia.
  Asalin wannan suna dai na 'AFRO-ASIA' wanda ya haɗa kalmomin Africa da Asia watau ya fito ne daga wani   Ba Amurke masanin Harsuna  mai sunaJoseph H. Greenberg.
  Sannam dashi da wasu Masanan  sun yi hasashen cewa dukkan waɗannan harsuna kimanin 250 sun fito ne daga wani harshe guda ɗaya wanda akayi hasashen ya wanzu a duniya kimanin shekaru 15,000 kafin haihuwar Annabi Isah A.S.
  Ance mutanen yankin Urheimat da suke zaune a Asia tun a wancan taohon zamami ne suke amfami da harshen, kafin daga bisani wasu dalilai suka rinka sanya mutanen yin hijira gami da bazama cikin duniya, ta yadda har bayan shekaru kimanin dubu 17 harsuna 250 sun fita daga jikin yaren nasu.
Masana sun yi hasashen cakuɗuwar ƙabilu da harasa a kusan ɗaukacin yankunan duniya, don haka aka tsammaci wasu daga waɗancan zuriya ne suka keto bahar Maliya zuwa yankin Afirka da zama tare da barbazuwa a tsawon lokaci, inda zuwa yau harshen ya rarrabu zuwa gidaje 5.
 1. Egyptian ( Yankin Tekun Nilu)
2. Amazigh (Berber; Arewacin Africa da Tsakiyar Sahara)
3. Chadic (Tsakiyar Africa, da yankin Tafkin Chadi. Harshen Hausa na ciki).
4. Cushitic (Yankin da ake kira Horn of Africa), da
5. Omotic (Kudu maso yammacin kasar Ethiopia).
  Daga abubuwan da masana suka kalla wajen danganta waɗannan harsuna da juna akwai yanayin fatar masu amfani da harsunan, da kuma falsafar harasan kansu, ko ace wasu jigogi dake tattare da harussan baki ɗaya.
   Misali, harshen Hausa daya fito daga gidan Chadic, an kalli abubuwa da dama kamar kalmar 'Mashi', da yadda jam'in ta ke komawa zuwa  'Masu' wajen sauyawar 'h' da 'i' zuwa 's' da 'u'. Haka kuma an kalli yadda a harshen ake amfani da kalmar 'ka' wajen danganta mallakin Namiji da kuma kalmar 'Ki' wajen danganta mallakin mace, abinda kusan yazo ɗaya a dukkan rukunin harussa aka sanya su a gida ɗaya.
  A karshe, mahangar tana nuni da cewa Asalin masu harshen Hausa mutane ne jikokin wasu ƙabilu da suka rayu a yankin Asia dubunnan shekaru da suka gabata.
Farfesa Ibrahim Malumfashi, da Marubuci Ado Ahmad gidan Dabino MON na daga marubutan da suka yi rubutu akan mahangar.