BAUTAR JAKARA
Ga abinda ya zo a littafin Tarihin Kano game da Bautar Kurmin Baƙin ruwa ko ace kurmin Jakara.
'Ma'abutan wannan ƙasa (Kano) waɗanda Bagauda ya same su a cikinta suna muljin garinsu, ba su bin kowa sai Tsumburbura da duhuwa tasa JAKARA. Ana ambatonta (duhuwar) da KURMIN BAƘIN RUWA, domin shi ruwa ne baƙi, duhuwa ta kewaye shi, ana kiyaye dukan musiba da ita da gunkinsu, mafarinta kuwa daga Gurgumasa har zuwa Dausara. Kiraranta da zartakenta ba su motsi sai idan musiba ta gabato wannan gari ta yi kuruwa sau uju, hayaƙi ya riƙa fitowa daga cikin Tsumburbura, wanda ke cikin tsakiyar ruwa. Sai su nemi baƙin kare su yanka a ƙarƴashin Tsumburbura, kuma su yanka baƙin bunsuru a cikin duhuwar.
Idan hayaƙi da kururuwan sun daɗu, to babu makawa sai musibar dɗta sadu dasu. Idan kuwa ba su daɗu ba, babu masiba. Sunan duhuwan nan kuwa MADAMA. Kuma sunan Tsumburbura RANDAYA'.
Ƙarin Bayani game da KURMIN JAKARA
Ita Jakara ana kiranta da suna KURMIN-BAƘIN-RUWA saboda ruwan tafkin baƙi ne, kuma kewaye take da bishiyoyi masu yawa. A cikin bishiyoyin ne akwai guda ɗaya da aljani yake kanta, wadda suke yin tsafinsu a kanta, kuma wadda take yin hayaƙi idan musiba ta tunkaro Kano. Ita wannan bishiyar a tsakiyar ruwan take. Wannan daji mai yawan bishiyu sunansa MATSAMA, Bishiyar Tsafin kuma itace RANDAYA. Ɗaukacin wajen shine Jakara har zuwa inda Kasuwar Kurmi take a yanzu.
Daga Littafin KANO TA DABO TUMBIN GIWA na Alhaji Ahmad Bahago