HIKAYAR WANI BAKO GA SARKI MAI SUNA 'DUNIYA'
Tare da SADIQ TUKUR GWARZO
Akwai wani Babban bafaden Sarki a wani garin Hausawa, yana da wata mata kyakkyawar gaske, wadda ake yawan sanar dashi cewa tana tara maza a gidansa, amma sam baya yadda.
Watarana sai wata Tsohuwa ta kirawo bafaden nan, tace masa "kullum idan ka tafi fada, matarka maza take tarawa. Amma idan kanason ka gane hakan, sai kace mata zakaje unguwa kauye, acan zaka kwana, inyaso sai ka dawo kafin lokacin don ka ganewa kanka abinda ke faruwa".
Sai kuwa bafade yace da tsohuwa, "haka nan za'ayi". Daga nan ya tafi ya samu mai ɗakinsa ya sheda mata cewa zai tafi unguwa sarki ya aikeshi kauye, bazai dawo ba sai gobe.
Bafade yahau dokin sa, ya bar gida abinsa.
Matar gida kuwa ta samu abinda takeso.
Mai gida ya tafi bazai dawo ba, don haka ta yanke shawarar aikewa masu nemanta cewa yau gida a buɗe yake.
Daga cikin waɗanda ta aikewa akwai Wazirin gari, da Galadiman gari, da kuma wani babban bako na Sarki mai suna Duniya, dukkansu suna nemanta.
Nan da nan waziri ya aiko da kaɓakai na nama da shinkafa, yace wa matar gida ta gyarasu yana nan tafe zuwa dare.
Dare nayi kuwa sai ga waziri fagan-fagan, ya karaso gidan bafade. Matar bafade ta taryeshi da abinci da nama wanda ya aiko dasu.
Ya zauna yana ci kenan, sai ya jiyo sawun takalma, nan fa hankalinsa ya tashi, tsammaninsa Maigida ne yake zuwa. Sai yayi wuf ya shige karkashin gado.
Ashe galadima ne ya samu karasowa.
Nan ma sai matar gida ta tarbeshi da kissa, ta gabatar masa da abincin da waziri ya bari. Galadima ya zauna ya fara cin abinci ana fira, sai shima ya jiwo sawun takalma.
Hankalinsa ya tashi, tsammaninsa Maigida ne, ya tambayi matar gida ina mafita, ita kuma sai ta nuna masa karkashin gado, inda waziri yake, nan take kuwa yayi wuf ya auka. Ashe bakon sarki mai suna Duniya ne ya shigo.
Koda Galadima ya shiga karkashin gado, sai ya fahimci akwai wani bayan shi aciki. Daya duba sosai sai ya gane ai waziri ne.
Galadima yace Waziri me kakeyi anan? Waziri yace Kaga Galadima, abinda ya kawoka shi ya kawo ni, saboda haka mu rufawa kanmu asiri.
Galadima yace aikuwa haka nan ne.
Suna nan suka jiyo muryar Duniya da matar gida suna taɗi, shima an bashi abinci kamar yadda aka basu. Daga nan su waziri suka gane ashe ba Maigida bane, Duniya ne.
Ba'a jima ba sai suka jiwo karar kofatan dawaki, alamar Maigida ya dawo kenan. Nan da nan Duniya yayi wurgi da kwanon abinci, ya tashi tsaye yana dube-duben mafita, can ya hango karkashin gado, sai kuwa yayi wuf ya auka.
Da shigar sa shima sai yayi arba da mutane biyu a ciki. Ya kalle su a tsanaki ya ganesu, yace Waziri!! Galadima!! Me ya kawo ku nan? Sukace muna gama ka da Allah mu rufawa juna asiri. Duniya yace to shikenan. Sai kowa cikin su yayi tsit kamar ruwa yaci su.
Maigida ya sauko daga kan dokinsa sannan ya daure shi, yace mai ɗakinsa ta bashi ruwa ya wanke jikinsa, da ta kawo masa ya gama kimtsawa, suka suka shiga cikin ɗakin tare, ya zauna a gefen gado.
Maigida yana cike da mamakin Kazafin da ake yiwa matarsa, tunda ance idan yayi haka zai kama matarsa da maza, gashi kuma yayi bai kama ta ɗin ba. Shine yake fadin "duniya.. duniya,, duniya"
Matar gida tace "Maigida me ya faru ne kake kiran duniya?"
Maigida yaci gaba da cewa "Duniya, duniya, duniya ba gaskiya"
Shikuma Duniya dake karkashin gado sai hankalin sa ya tashi, abinka da bako, tsammanin sa Maigida sunan sa yake kira. Sai yayi wuf ya ce "Haba maigida, yanzu sunana kaɗai kake kira alhali ga Waziri ga kuma Galadima?"
Maigida ya tashi zumbur, yana fafutikar neman madoki, kafin kace haka tuni galadima da waziri da Duniya sun fara kacaniyar fitowa daga karkashin gado domin arcewa a na kare...
Tare da SADIQ TUKUR GWARZO
Akwai wani Babban bafaden Sarki a wani garin Hausawa, yana da wata mata kyakkyawar gaske, wadda ake yawan sanar dashi cewa tana tara maza a gidansa, amma sam baya yadda.
Watarana sai wata Tsohuwa ta kirawo bafaden nan, tace masa "kullum idan ka tafi fada, matarka maza take tarawa. Amma idan kanason ka gane hakan, sai kace mata zakaje unguwa kauye, acan zaka kwana, inyaso sai ka dawo kafin lokacin don ka ganewa kanka abinda ke faruwa".
Sai kuwa bafade yace da tsohuwa, "haka nan za'ayi". Daga nan ya tafi ya samu mai ɗakinsa ya sheda mata cewa zai tafi unguwa sarki ya aikeshi kauye, bazai dawo ba sai gobe.
Bafade yahau dokin sa, ya bar gida abinsa.
Matar gida kuwa ta samu abinda takeso.
Mai gida ya tafi bazai dawo ba, don haka ta yanke shawarar aikewa masu nemanta cewa yau gida a buɗe yake.
Daga cikin waɗanda ta aikewa akwai Wazirin gari, da Galadiman gari, da kuma wani babban bako na Sarki mai suna Duniya, dukkansu suna nemanta.
Nan da nan waziri ya aiko da kaɓakai na nama da shinkafa, yace wa matar gida ta gyarasu yana nan tafe zuwa dare.
Dare nayi kuwa sai ga waziri fagan-fagan, ya karaso gidan bafade. Matar bafade ta taryeshi da abinci da nama wanda ya aiko dasu.
Ya zauna yana ci kenan, sai ya jiyo sawun takalma, nan fa hankalinsa ya tashi, tsammaninsa Maigida ne yake zuwa. Sai yayi wuf ya shige karkashin gado.
Ashe galadima ne ya samu karasowa.
Nan ma sai matar gida ta tarbeshi da kissa, ta gabatar masa da abincin da waziri ya bari. Galadima ya zauna ya fara cin abinci ana fira, sai shima ya jiwo sawun takalma.
Hankalinsa ya tashi, tsammaninsa Maigida ne, ya tambayi matar gida ina mafita, ita kuma sai ta nuna masa karkashin gado, inda waziri yake, nan take kuwa yayi wuf ya auka. Ashe bakon sarki mai suna Duniya ne ya shigo.
Koda Galadima ya shiga karkashin gado, sai ya fahimci akwai wani bayan shi aciki. Daya duba sosai sai ya gane ai waziri ne.
Galadima yace Waziri me kakeyi anan? Waziri yace Kaga Galadima, abinda ya kawoka shi ya kawo ni, saboda haka mu rufawa kanmu asiri.
Galadima yace aikuwa haka nan ne.
Suna nan suka jiyo muryar Duniya da matar gida suna taɗi, shima an bashi abinci kamar yadda aka basu. Daga nan su waziri suka gane ashe ba Maigida bane, Duniya ne.
Ba'a jima ba sai suka jiwo karar kofatan dawaki, alamar Maigida ya dawo kenan. Nan da nan Duniya yayi wurgi da kwanon abinci, ya tashi tsaye yana dube-duben mafita, can ya hango karkashin gado, sai kuwa yayi wuf ya auka.
Da shigar sa shima sai yayi arba da mutane biyu a ciki. Ya kalle su a tsanaki ya ganesu, yace Waziri!! Galadima!! Me ya kawo ku nan? Sukace muna gama ka da Allah mu rufawa juna asiri. Duniya yace to shikenan. Sai kowa cikin su yayi tsit kamar ruwa yaci su.
Maigida ya sauko daga kan dokinsa sannan ya daure shi, yace mai ɗakinsa ta bashi ruwa ya wanke jikinsa, da ta kawo masa ya gama kimtsawa, suka suka shiga cikin ɗakin tare, ya zauna a gefen gado.
Maigida yana cike da mamakin Kazafin da ake yiwa matarsa, tunda ance idan yayi haka zai kama matarsa da maza, gashi kuma yayi bai kama ta ɗin ba. Shine yake fadin "duniya.. duniya,, duniya"
Matar gida tace "Maigida me ya faru ne kake kiran duniya?"
Maigida yaci gaba da cewa "Duniya, duniya, duniya ba gaskiya"
Shikuma Duniya dake karkashin gado sai hankalin sa ya tashi, abinka da bako, tsammanin sa Maigida sunan sa yake kira. Sai yayi wuf ya ce "Haba maigida, yanzu sunana kaɗai kake kira alhali ga Waziri ga kuma Galadima?"
Maigida ya tashi zumbur, yana fafutikar neman madoki, kafin kace haka tuni galadima da waziri da Duniya sun fara kacaniyar fitowa daga karkashin gado domin arcewa a na kare...