TARIHIN BIRNIN RANO
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
08060869978
Saɓanin abinda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya kawo a littafinsa 'Tarihin Kano kafin Jihadi' cewa asalin garin Rano daga wani mai suna Ranau ne da yazo ƙasar Hausa daga ƙasar Habasha tare da ƴanuwansa Maguzawa masu suna Gayya da Dala tun kafin haihuwar Annabi Isa A.S, bayani daga Rano ya kawo wata mahangar wadda ta saɓawa haka.
A littafin da Maigirma Barayan Kano Hakimin Bunkure Tafida Abubakar Ila ya wallafa mai suna Tarihin Rano, ya kawo cewa ƙabilar Kwararrafawa da suka zo daga Kwararrafa ta cikin ƙasar Riruwai sune asalin kafa Rano.
A cewarsa waɗannan ƙabila mafarauta ne, kuma wasu daga cikinsu ne suka baro garinsu tare da riskar yankin da Rano take ayau, suka ganshi cike da albarkatu da tsaunika, don haka sai suka yanke shawarar zama akan duwatsun suna noma da kiwo.
Basaraken ya faɗa cewar Asalin sunan Rano yazo ne daga wani sarkin Rano mai suna Ranau, wanda wata rana aka kawo yaƙi ƙasar sa har kuma aka hallaka shi a wajen yaƙi, aka binne shi a gefen wani dutse mai suna Tajika.
Yace kasancewar akwai ƙorama da mutane ke zuwa domin samo ruwan sha, sai mutane ke cewa mun tafi gurin Rauno ɗebo ruwa, daga baya aka koma kiran yankin da suna Rano.
Waɗannan Kwararrafawa sun jima suna mulkin Rano a tsakaninsu, sun zauna da fadojinsu akan waɗannan manyan tsaunika na Rano misalin Dutsen Damishi, dutsen Kurgun da dutsen Mairama, kuma har yanzu akwai sawun wanzuwarsu a wurare mabanbanta, misalin wasu mashigai da sawun gine-ginen duwatsu da koguna masu duhu da aka samu wsɗanda akace mutanen sukan ɓoye acikinsu idan an kawo musu hari, waɗanda kuna zuwa yanzu sai jarumin gaske ne kaɗai zai iya cusa kansa ciki, daga baya sai Hausawan Haɓe suka zo suka ƙwace mulkin yankin baki ɗaya.
Dangane da sarkin farko a zuriyar Haɓe daya fara mulkin Rano, kusan dukkanin maruwaita sun haɗu akan cewa Autan Bawo, ƙani ga Sarkin Kano Bagauda, kuma jikan Bayajidda shine ya soma mulkin Rano. Sai dai akwai saɓani akan ainihin sunansa da kuma dalilin zuwansa Rano.
Barayan Kano ya faɗa a littafinsa cewar Zamna Kogo shine sunan Sarkin Rano na farko da Haɓe suka ɗora. Kuma ya nuna kamar yaƙi ne Haɓe suka kawo Rano har suka cita da yaƙi gami da ɗora nasu a mulki a wajajen shekara ta 1082 miladiyya.
Amma Maje Ahmad Gwangwazo ya tafi akan cewa Hamza Zimango ne sunan wannan sarki, kuma shi ƙani ne ga Bagauda sarkin Kano na farko.
A cewarsa Zimango yazo ne daga Daura da iyalansa, ya sauka a wurin yayansa Bagauda, har kuma yayan nasa ya labarta masa dabarun da yabi ya zamo sarkin Kano, watau ta hanyar Jarumtarsa da kuma alƙalanci na adalci daya rinƙa yi tsakanin mutanen Kano, sai shima Zimango ya tashi daga Kano yayi kudu, har ya riski Rano, anan ya zauna tare da maguzawan yankin, har kuma daga baya suka naɗa shi sarkin su.
Don haka, Rano ta shahara da mayaƙa gami da ɗaukaka gagaruma a zamanin baya, kuma ko a lokacin Jihadi, itace ƙasa ta ƙarshe da Fulani suka ci da yaƙi a zamanin Sarkin Kano Sulaimanu, lokacin da Sarki Alwali ya gudu daga Kano sai ya zauna a Rano sannan ya tafi Zariya, bayan shekara ɗaya ya baro Zariya ya sauka a Rano, ya wuce burum burum, kafin daga bisani rundunar mayaƙan fulani ta kawo musu yaƙi wanda yayi sanadiyyar mutuwar shi kansa Sarki Alwalin da kuma Sarkin Rano Jatau na lokacin. Suka naɗa sarki Dikko bafulani na farko a tarihi..
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
08060869978
Saɓanin abinda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya kawo a littafinsa 'Tarihin Kano kafin Jihadi' cewa asalin garin Rano daga wani mai suna Ranau ne da yazo ƙasar Hausa daga ƙasar Habasha tare da ƴanuwansa Maguzawa masu suna Gayya da Dala tun kafin haihuwar Annabi Isa A.S, bayani daga Rano ya kawo wata mahangar wadda ta saɓawa haka.
A littafin da Maigirma Barayan Kano Hakimin Bunkure Tafida Abubakar Ila ya wallafa mai suna Tarihin Rano, ya kawo cewa ƙabilar Kwararrafawa da suka zo daga Kwararrafa ta cikin ƙasar Riruwai sune asalin kafa Rano.
A cewarsa waɗannan ƙabila mafarauta ne, kuma wasu daga cikinsu ne suka baro garinsu tare da riskar yankin da Rano take ayau, suka ganshi cike da albarkatu da tsaunika, don haka sai suka yanke shawarar zama akan duwatsun suna noma da kiwo.
Basaraken ya faɗa cewar Asalin sunan Rano yazo ne daga wani sarkin Rano mai suna Ranau, wanda wata rana aka kawo yaƙi ƙasar sa har kuma aka hallaka shi a wajen yaƙi, aka binne shi a gefen wani dutse mai suna Tajika.
Yace kasancewar akwai ƙorama da mutane ke zuwa domin samo ruwan sha, sai mutane ke cewa mun tafi gurin Rauno ɗebo ruwa, daga baya aka koma kiran yankin da suna Rano.
Waɗannan Kwararrafawa sun jima suna mulkin Rano a tsakaninsu, sun zauna da fadojinsu akan waɗannan manyan tsaunika na Rano misalin Dutsen Damishi, dutsen Kurgun da dutsen Mairama, kuma har yanzu akwai sawun wanzuwarsu a wurare mabanbanta, misalin wasu mashigai da sawun gine-ginen duwatsu da koguna masu duhu da aka samu wsɗanda akace mutanen sukan ɓoye acikinsu idan an kawo musu hari, waɗanda kuna zuwa yanzu sai jarumin gaske ne kaɗai zai iya cusa kansa ciki, daga baya sai Hausawan Haɓe suka zo suka ƙwace mulkin yankin baki ɗaya.
Dangane da sarkin farko a zuriyar Haɓe daya fara mulkin Rano, kusan dukkanin maruwaita sun haɗu akan cewa Autan Bawo, ƙani ga Sarkin Kano Bagauda, kuma jikan Bayajidda shine ya soma mulkin Rano. Sai dai akwai saɓani akan ainihin sunansa da kuma dalilin zuwansa Rano.
Barayan Kano ya faɗa a littafinsa cewar Zamna Kogo shine sunan Sarkin Rano na farko da Haɓe suka ɗora. Kuma ya nuna kamar yaƙi ne Haɓe suka kawo Rano har suka cita da yaƙi gami da ɗora nasu a mulki a wajajen shekara ta 1082 miladiyya.
Amma Maje Ahmad Gwangwazo ya tafi akan cewa Hamza Zimango ne sunan wannan sarki, kuma shi ƙani ne ga Bagauda sarkin Kano na farko.
A cewarsa Zimango yazo ne daga Daura da iyalansa, ya sauka a wurin yayansa Bagauda, har kuma yayan nasa ya labarta masa dabarun da yabi ya zamo sarkin Kano, watau ta hanyar Jarumtarsa da kuma alƙalanci na adalci daya rinƙa yi tsakanin mutanen Kano, sai shima Zimango ya tashi daga Kano yayi kudu, har ya riski Rano, anan ya zauna tare da maguzawan yankin, har kuma daga baya suka naɗa shi sarkin su.
Don haka, Rano ta shahara da mayaƙa gami da ɗaukaka gagaruma a zamanin baya, kuma ko a lokacin Jihadi, itace ƙasa ta ƙarshe da Fulani suka ci da yaƙi a zamanin Sarkin Kano Sulaimanu, lokacin da Sarki Alwali ya gudu daga Kano sai ya zauna a Rano sannan ya tafi Zariya, bayan shekara ɗaya ya baro Zariya ya sauka a Rano, ya wuce burum burum, kafin daga bisani rundunar mayaƙan fulani ta kawo musu yaƙi wanda yayi sanadiyyar mutuwar shi kansa Sarki Alwalin da kuma Sarkin Rano Jatau na lokacin. Suka naɗa sarki Dikko bafulani na farko a tarihi..
No comments:
Post a Comment