Thursday, 30 January 2020

WANENE SADIQ TUKUR GWARZO?

TARIHIN SADIQ TUKUR GWARZO
(Global Goodwill Ambassador)
  Shi bafillatani ne, an haife shi a garin Gwarzo, ya fito ne daga zuriyar Mallam Isah wanda Ɗan Gwarzo Baba ya gaiyato daga Sokoto domin tseratar da garin bisa wani mummunan hari da Ɗan baskore, sarkin Maraɗi na zamanin ke shirin kawowa wannan gari a ƙarni na goma sha takwas.
  Sadiq Gwarzo ya yi karatun addini dana boko a garin Gwarzo, sai a shekarar 2005 ya bar garin zuwa kwalejin fasaha mai suna GTC BAGAUDA domin kammala karatun sakandare, inda ya karanci fannin 'Carpentry and Joinery'. ya kammala karatun a shekarar 2008.
  A shekarar 2009 Sadiq Gwarzo ya yi karamar Diploma akan 'Computer Networking and Maintenance' a cibiyar koyar da karatun Kwamfuta ta Himma dake Gadon kaya a garin Kano, daga nan sai ya koma Gwarzo ya sake yin karatun karamar Diploma a 'School of Environmetal Studies' wadda ke ƙarƙashin 'Kano state Polytechnique', inda ya karanci 'Painting and Decoration'.
  Bayan ya kammala a shekarar 2011, sai kuma ya samu shiga 'School of Nursing kano' a shekarar 2012, ya kammala kwalejin a shekarar 2015 a matsayin cikakken majinyaci.
   Sannan yabsake komawa makarantar School of Hygiene a shekarar 2017 tare da karantar babbar diploma watau 'HND Public Health Nursing', inda ya kammala a 2019.
  Haka kuma yayi kwasa-kwasai da yawa ta yanar gizo daga  jami'ar buɗe ta ƙasar Australia, daga ciki akwai:-
-Anthropology: Becoming Human
-Origin of Crime
-Asronomy: Discovering the Universe
- Midwifery Education
-World Music
Da wasun su.
  Sadiq Gwarzo ya soma rubuta littafi tun yana firamare, kasancewar sa ya tashi a matsayin makaranci. Amma dai littafin sa na farko shine 'Nasara a Tafin Hannu' wanda ya wallafa a shekarar 2010. Daga nan sai 'Hikimar Allah Na Da yawa' a 2012, da 'Ilimin Kasuwanci' a 2015, sai kuma ' The Art OF Talking cure' a 2016.
Sauran littattafan da ya wallafa sune:
-Sabuwar Fuskar Ilimin Falsafanci
-Sirrin Rayuwa a cikin ilimin Lambobi
-Tarihin Tsohuwar Daular Baƙin mutum
-Kula da Lafiyar Mata masu ciki da kananun yara
-Asalin Hausawa daga kaɗe-kaɗen su
-Tarihin Daulolin Musulunci
-Magana Hausa
-Madubin Sarakuna
-Tarihin Jihadin Danfodio a Kasar Hausa
 Sadiq Gwarzo ya fi karkata akan rubututtukan da suka shafi 'tarihi', shiyasa wasu marubutan kan yi masa laƙabi da suna 'Gwarzon Tarihi', amma duk da haka ya yayi rubututtuka da dama akan fannikan siyasa, kasuwanci da zamantakewar rayuwa. Akan haka, ya rubuta muƙalu sama da 250 waɗanda ya taskance a turakar sa ta yanar gizo  http://sadiqtukurgwarzo.blogspot.com. Haka kuma ya taya Mallam Salisu Durmin Iya gabatar da shirin 'Hausa Rigar Siliki' a gidan Radiyon Guarantee na kusan tsawon shekara ɗaya a inda suka rinƙa tattaunawa akan tarihi da kafuwar ƙasashen Hausa. Baya da haka, Sadiq Gwarzo da taimakon masana kuma marubuta irin su Farfesa Yusuf Adamu, da wasun sa, sun kafa wata cibiya mai rajin bincike akan tarihin hausa da hausawa wadda suka sanyawa suna 'Center for the study of Hausa Civilisation', Ƙari akan haka, Sadiq Gwarzo na gabatar da ayyukan fassara ga kamfanoni na gida dana waje, da rubututtuka na tarihin ɗai-ɗaikun al'umma da kuma jaridu irin su Leadership Hausa, Manuniya da wasun su na yanar gizo. 
   A shekarar 2019 kungiyar duniya mai rajin tallafawa al'umma mai suna 'Global Goodwill Ambassadors' suka baiwa Sadiq Tukur Gwarzo lamba da sahalewar zama mamban su bisa ayyukan alheri da yake yi a fannonin taimakon al'umma. Tun kafin wannan lokacin, ya kasance a gaba-gaba wajen yaƙi da cututtuka masu damun al'umma misalin HIV, da Malaria  ga ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa.
    Zuwa yanzu, Sadiq Gwarzo na gabatar da ayyukan sa na rubuce-rubuce, da na ƙungiyoyi tare kuma da kasuwanci. Sannan tare da haɗin guiwar marubuci Ɗanladi Haruna, ya kafa kwalejin farko ta yanar gizo wadda ake koyar da ilimai da harshen Hausa. Babban burin sa shine Hausawa su sami ilimi a sauƙaƙe, su kuma soma gogayya da sauran al'ummar duniya akan haka. Dalili kenan da ya samar da kwalejin domin share fage ga duk wani son koyo da koyarwa. Kuma ana sa ran kwalejin zata fassara manyan ilimai da ake taƙama dasu a zamance anan duniya domin koyar da al'ummar Hausawa.
   Zuwa yanzu, Sadiq Gwarzo na da mata ɗaya, da ɗa ɗaya.
   

TARIHIN ZUWAN TURAWA AFIRKA TA YAMMA

TARIHI ABIN TUNAWA: ASALIN YADDA TURAWA SUKA BINCIKO AFRIKA TA YAMMA
Daga SADIQ TUKUR GWARZO
Tun da jimawa, Labarai masu ƙayatarwa suka cika kasashen Yammacin Turai dangane da yankin Afirka ta yamma. Tatsuniyoyi sun shahara akan haka. Labarin Attajiri Mansa Musa mai kyautar gwala-gwalai ya zamo abin jimami a Ingila, haka kuma labarin shaharar Kogin Kwara ba zai misaltu ba.
A wancan lokacin dai, turawa na ɗaukar birnin Tambuktu a matsayin birnin Gwal, domin haka ma suke yiwa garin laƙabi da suna 'birnin gwal', suna kuma da ƙarancin sani game da kogin Kwara.
A kan hakane aka kafa wata kungiya a birnin landan mai suna 'Association for promoting the discovery of the interior parts of africa' a shekarar 1788, wadda a taƙaice ake ambatar ta da 'African association'. Kungiyar, wadda sir joseph Banks ke jagoranta, ta ƙunshi manyan mutane, masana da attajirai, kuma tana da burin binciko zance mafi gaskiya dangane da Birnin Tambuktu, da kuma kogin Kwara. Wannan yunkuri shine asalin fara laluben turawa a kasashen Afirka ta yamma.
Akan haka, an rinƙa sauraron matafiya da sauran masu binciken tarihin duniya dangane da abinda suka sani game da Tambuktu da kuma kogin kwara. Ga misalin abubuwan da aka samo;
I. Bayani yazo daga James Bruce dan Kasar scotland, wanda a shekarar 1769AD ya isa kasar Habasha cewa "daular Tambuktu karkashin mulkin Muhammadu Askia I, tayi matukar karfi a wajajen ƙarni na 13 zuwa na 15, kuma itace ta mamaye mafi yawan ƙasashen yammacin Africa, tun daga yankin Gambiya da senegal, har zuwa sokoto dake ƙasar Hausa. A gabashi kuma sai da ta dangane da kogin kwara. Garin Timbuktu kuwa, yana dauke da baƙi masu yawa, kuma gari ne mai cike da arzikin gwal.
ii. An samu labari daga wani masani mai suna Al Hassan Bin muhammad al-Wazziniz zayyati wanda akewa Laƙabi da Leo Africanus (ma'ana zakin Afrika) wanda kuma akace kakannin sa na cikin gungun musulman da sukayi gudun hijira izuwa sassan duniya daga birnin Andaluz a shekarar 1492 sa'ar da Sarki Ferdinand da Sarauniya Isabella suka cinye garin da yaki, ga abinda ya  faɗa bayan ya samu damar ziyartar Timbuktu "ana kawo hatsi, shanu, madara da man shanu mai tarin yawa izuwa garin Timbuktu duk kuwa da kasancewar garin cikin sahara inda babu ƙoramu da lambuna. Babban abinda mutanen garin ke musayar kasuwanci dashi shine gishiri''.
Ya ƙara da cewa ''Sarkin Timbuktu attajiri ne na gaske, wanda ya mallaki sulalla na zinare marasa adadi. A koda yaushe kuma idan yana tafiya zaka samu kimanin dawakai 3000 suna rufa masa baya. Sannan yana da tarin likitoci, alƙalai, malamai masu wa'azi da sauran masana zazzaune a fadar sa''.
Daga wajen Leo Africanus ne kuma turawan ingila suka fahimci cewa Gishiri yana da matuƙar daraja a Timbuktu, saboda ya ayyana cewa zuwa akeyi dashi daga wani gari mai suna Tangaza, wanda yake da nisan Mil ɗari biyar daga Timbuktun. Har ma yake cewa "na taɓa kasancewa a Timbuktu a lokacin da farashin mangalar gishiri yake dai-dai da farashin sisin gwal tamanin".
iii. Wani bayanin ma ya samu daga hannun wani mai suna Asseed El hage Abd Salam Shabeeniy, wanda akewa laƙabi da Shebani, a wajajen shekara ta 1788. Shebani ya rayu a timbuktu tsawon shekara uku, inda har ya leƙa kasar hausa, ga kuma abinda ya naƙalto " Adadin mutanen garin timbuktu zai cimma dubu 40, banda bayi da kuma baƙi mazauna garin. Duk al'ummar garin baƙaƙen fata ne, sannan kuma kusan duk baƙon da zaije garin sai ya auri 'yar garin saboda kyawun matayen su. Kallo daya tak zai sa ka faɗa so da ƙaunar su"
Ƙari akan haka shine labarin Attajirin Sarkin Timbuktu Mansa Musa wanda ya baza duniya. Ance yayi zamani a wajajen ƙarni na 12, shine kuma ya taɓa ziyartar Saudiyya da ɗumbin bayi gami da ɗumbin gwala-gwalai.
Sai dai duk labaran nan, babu abinda akeji game da Kogin Kwara, kuma har izuwa lokacin kafuwar kungiyar, ba a samu wani bature farar fata ba wanda yayi ikirarin yaga Kogin kwara da idanuwansa.
A shekarar 1790, wani tsohon soja mai suna Daniel Houghton ya tunkari wannan kungiya ta 'African Association', da nufin amsar kwantiragen zuwa Africa ta yamma da ƙafa don gani da ido.
  Nan take kuwa kungiyar ta amince masa, ta kuma ɗora masa nauyin ziyartar Tafkin Barra kunda (wani gari dake ƙasar Gambiya) da kuma ƙasar Hausa tare da binciko ainihin inda garin Timbuktu yake, sannan ya ƙarƙare tafiyar a gaɓar kogin Kwara.
 Da yin haka, sai ya shiga kokarin koyon harshen Larabci tare da wani yare na ƙasar senegal mai suna 'Mandingo' ta yadda zai samu damar mu'amala da mutane.
Sannan ya sanya ranar fara tafiya.
A watan Oktoba na shekarar 1790, Hougton ya shigo jirgin ruwa, inda bayan wasu kwanaki ya sauka a gabar Kogin Gambia a wani gari da ake kira Barra. Ya tafi tiryan-tiryan har wani gari mai suna Pisania, daga nan ya risƙi wani gari da ake kira Jonkakonda, daga bisani kuma ya ƙaraso masarautar Wuli a farkon shekarar 1791.
A wannan wuri, ance Sarkin Masarautar Wuli ya karɓi Houghton da girmamawa, har ma ya bashi mazauni a garin sa mai suna Medina. Sai dai ba a jima ba abokan hamayyar Sarkin suka kawowa garin hari, inda kuma sukaci nasarar kone garin, har ma kayyayakin Houghton na yaƙi da wasu abubuwa masu amfani suka ƙone ƙurmus. Wannan abu yayi masa ciwo matuƙa.
Duk da haka, Houghton baiyi ƙasa a guiwa ba, inda yaci gaba da tafiyar sa yana neman garin Timbuktu.
  Ance a wajajen watan Mayu na shekarar 1791, Houghton ya bar gaɓar tekun Barra, sannan ya kutsa kai don tunkarar Timbuktu. A lokacin ne kuma ya tura da saƙo zuwa Ingila mai ɗauke da labarin yadda tafiyar sa take kasancewa. Saƙon ya isa birnin Landan cikin nasara.
Daga nan, Houton ya samu damar gewayawa ta kogin Senegal, shine ma sarkin wani gari yaci mutuncinsa, da ƙyar ya samu kuɓuta ya isa masarautar Ferbanna dake yankin Bambu na ƙasar ta senegal acikin damuna ta wannan shekara.
Daga nan ne kuma ya hadu da wani Matafiyi mai suna Madegammo, wanda yayi alƙawarin zai yiwa Houghton jagoranci izuwa birnin Timbuktu a kyauta. Sun fara wannan tafiya ne a watan yulin 1791, shine har Houghton ya ƙara turawa da saƙo gida yana mai labarta yarjejeniyar da sukayi da matafiyin, ya aika saƙon ne ta hanyar matafiya, kuma sannu-a hankali ya isa birnin landan.
  Wannan saƙon shine ya zamo na ƙarshe, domin daga nan ba a ƙara jin ɗuriyar sa ba.
A shekara ta 1793, labari mai tushe ya riski Landan cewar Houghton ya samu kansa cikin mawuyacin hali yayin tafiyarsa zuwa Tambuktu, wannan ne yasa tafiyar ta sire masa, abokan tafiyar sa kuma suka ribace shi, inda suka sauya akalar tafiyar izuwa wani gari mai suna Tisheet (wanda yake a ƙasar Mouritania a yanzu). Amma kwana biyu da yin haka, sai Houghton ya fuskanci cewa abokan tafiyar sa na yunƙurin hallaka shi, wannan yasa ya tsere musu, ya shiga cikin sahara ba ruwa ba abinci a tare dashi, a daddafe ya isa wani gari mai suna Tarra, inda kuma cikin rashin sa'a, mutanen garin suka hanashi ruwa da abinci, wannan yasa yunwa ta halaka shi.
  Ance ko gawar Houghton mutanen garin ƙin binne ta sukayi, a ƙarshe tsuntsaye ne suka yagalgalata a banza.
Wannan labari yayi matuƙar ɓatawa Ingila Rai, sannan ya dakushe guiwar masu son jin labarin africa ta yamma da yawa.
   Amma ba'a fi shekaru biyu ba, sai ga takarda daga hannun wani baturen ƙasar scotland mai suna MUNGO PARK, yana neman sahalewar ƙarasa aikin da Houghton ya fara..
Tafiyar mungo park (wadda tarihin ta yazo a littafin Mungopark Mabuɗin Kwara) tana ƙunshe da darasi mai tarin yawa. A cikin ta ne mukaji yadda iyaye da kakanni suka rayu a wancan zamani, da kuma yadda Mungopark ya rinƙa bibiyar matsalolin da marigayi Houton ya fuskanta, har ma da laifuffukan da ya yiwa sarakunan africa ta yamma, dalilin dayasa suka tsaneshi kuma kenan har abin ya kai shi ga halaka!

TARIHIN MAHAIFIN MANI MAKWALLA DA YADDA YA KUƁUTAR DA GARIN GWARZO

TARIHIN MANIN MAKWALLA
Sunan Mahaifin Manin Makwalla Mallam Isah, shi Bafillatani ne Batoranke, kuma malami masanin asararu, a sokoto yake da zama.
  Wata rana a wuraren ƙarni na goma sha takwas kafin zuwan turawan mulkin mallaka, watau jim kaɗan da yin jihadin fulani a ƙasar Hausa, sai wani sarki ya aiko da goron yaƙi zuwa garin Gwarzo.
  Garin Gwarzo an sani cewa Bamaguje Gwarzo ne ya kafa shi, amma daga baya wani Bafillatani mai suna Baba ya karɓe iko da garin, har kuma ya kasance fulanin ke gadon mulkinsa, amma kuma ana kiran sarkin garin da suna 'Ɗan Gwarzo', don haka an samu cewa a lokacin jihadi, fulani basu yaƙi garin ba, har ma ana cewa Shehu Abdullahi Gwandu watau ƙani ga Mujaddadi Usman Ɗan Fodio, ya sauka a garin yayin da ya taho daga sokoto zai je Birnin Kano.
   Don haka, bisa labarin zuwan wannan yaƙi, sai ake ganin duk da kasancewar garin Gwarzo a lokacin zagaye yake da ganuwa domin kariya daga mahara, amma lalle an tabbatar zuwan wannan sarkin bala'i ne ga garin. Don haka sai Ɗan Gwarzo na lokacin ya shiga shawarwarin mafita.
   Akan haka wani bafaden sa ya bashi labarin wani malami mai suna Mallam Isah dake sokoto, tare da shawarar aje azo dashi domin samun kuɓuta daga wannan ƙangi.
  Ɗan Gwarzo ya amince da wannan shawara, sannan ya tashi fadawa da abin alheri zuwa sokoto da hanzari. Da isar su suka gabatar wa da Mallam Isah saƙon Ɗan Gwarzo tare da buƙatar su ta ya biyo su zuwa garin Gwarzo domin taimakawa da adduar samun kariyar musibar dake tunkaro garin.
Abun da akayi kenan, Mallam Isah ya taso tare da fadawa suka nufo Gwarzo. Kwanci tashi sai ga su a garin. Ɗan Gwarzo yayi masa marhaban lale tare da sake gabatar masa da halin ƙuncin dake gaban su.
Mallam Isah yace masa kada ya damu, insha Allahu Allah zai yi maganin wannan fargaba. Sannan ya nemi a samu wani da zai yi masa jagoranci wajen kewaya ganuwar garin Gwarzo.
Ance Mallam Isah carbi ya ɗauka a hannunsa yana ja, yana lazimi, yana bin ganuwar data zagaye garin Gwarzo yana addua, bai gushe ba har sai da ya kewaye garin baki ɗaya, sannan ya koma masaukin sa ya zauna.
Aikuwa Allah da ikonsa, koda waɗannan maharan suka zo, sai garin ya ɓace musu, ance daga cikin Gwarzo ana jiyo sautin kiɗe kiɗen su da haniniyar dawakansu, amma kuma Allah ya hana su ganin garin balle su durfafe shinda yaƙi. A haka sukaƙaraci zaman su suka koma inda suka fito.
Jim kaɗan da faruwar haka sai Mallam Isah yace da Ɗan Gwarzo zai koma gida wajen ahalinsa, sai kuwa Ɗan Gwarzo ya shiga lallami da magiyar kada ayi haka, domin yana fargabar kada bayan tafiyar sa maharan su sake dawowa.
Babu yadda Mallam Isah ya iya, sai ya aike aka taho masa da ahalin sa daga Sokoto zuwa Gwarzo.. Kunji asalin yadda Manin Makwalla ya tashi a Gwarzo.