TARIHIN MANIN MAKWALLA
Sunan Mahaifin Manin Makwalla Mallam Isah, shi Bafillatani ne Batoranke, kuma malami masanin asararu, a sokoto yake da zama.
Wata rana a wuraren ƙarni na goma sha takwas kafin zuwan turawan mulkin mallaka, watau jim kaɗan da yin jihadin fulani a ƙasar Hausa, sai wani sarki ya aiko da goron yaƙi zuwa garin Gwarzo.
Garin Gwarzo an sani cewa Bamaguje Gwarzo ne ya kafa shi, amma daga baya wani Bafillatani mai suna Baba ya karɓe iko da garin, har kuma ya kasance fulanin ke gadon mulkinsa, amma kuma ana kiran sarkin garin da suna 'Ɗan Gwarzo', don haka an samu cewa a lokacin jihadi, fulani basu yaƙi garin ba, har ma ana cewa Shehu Abdullahi Gwandu watau ƙani ga Mujaddadi Usman Ɗan Fodio, ya sauka a garin yayin da ya taho daga sokoto zai je Birnin Kano.
Don haka, bisa labarin zuwan wannan yaƙi, sai ake ganin duk da kasancewar garin Gwarzo a lokacin zagaye yake da ganuwa domin kariya daga mahara, amma lalle an tabbatar zuwan wannan sarkin bala'i ne ga garin. Don haka sai Ɗan Gwarzo na lokacin ya shiga shawarwarin mafita.
Akan haka wani bafaden sa ya bashi labarin wani malami mai suna Mallam Isah dake sokoto, tare da shawarar aje azo dashi domin samun kuɓuta daga wannan ƙangi.
Ɗan Gwarzo ya amince da wannan shawara, sannan ya tashi fadawa da abin alheri zuwa sokoto da hanzari. Da isar su suka gabatar wa da Mallam Isah saƙon Ɗan Gwarzo tare da buƙatar su ta ya biyo su zuwa garin Gwarzo domin taimakawa da adduar samun kariyar musibar dake tunkaro garin.
Abun da akayi kenan, Mallam Isah ya taso tare da fadawa suka nufo Gwarzo. Kwanci tashi sai ga su a garin. Ɗan Gwarzo yayi masa marhaban lale tare da sake gabatar masa da halin ƙuncin dake gaban su.
Mallam Isah yace masa kada ya damu, insha Allahu Allah zai yi maganin wannan fargaba. Sannan ya nemi a samu wani da zai yi masa jagoranci wajen kewaya ganuwar garin Gwarzo.
Ance Mallam Isah carbi ya ɗauka a hannunsa yana ja, yana lazimi, yana bin ganuwar data zagaye garin Gwarzo yana addua, bai gushe ba har sai da ya kewaye garin baki ɗaya, sannan ya koma masaukin sa ya zauna.
Aikuwa Allah da ikonsa, koda waɗannan maharan suka zo, sai garin ya ɓace musu, ance daga cikin Gwarzo ana jiyo sautin kiɗe kiɗen su da haniniyar dawakansu, amma kuma Allah ya hana su ganin garin balle su durfafe shinda yaƙi. A haka sukaƙaraci zaman su suka koma inda suka fito.
Jim kaɗan da faruwar haka sai Mallam Isah yace da Ɗan Gwarzo zai koma gida wajen ahalinsa, sai kuwa Ɗan Gwarzo ya shiga lallami da magiyar kada ayi haka, domin yana fargabar kada bayan tafiyar sa maharan su sake dawowa.
Babu yadda Mallam Isah ya iya, sai ya aike aka taho masa da ahalin sa daga Sokoto zuwa Gwarzo.. Kunji asalin yadda Manin Makwalla ya tashi a Gwarzo.
Sunan Mahaifin Manin Makwalla Mallam Isah, shi Bafillatani ne Batoranke, kuma malami masanin asararu, a sokoto yake da zama.
Wata rana a wuraren ƙarni na goma sha takwas kafin zuwan turawan mulkin mallaka, watau jim kaɗan da yin jihadin fulani a ƙasar Hausa, sai wani sarki ya aiko da goron yaƙi zuwa garin Gwarzo.
Garin Gwarzo an sani cewa Bamaguje Gwarzo ne ya kafa shi, amma daga baya wani Bafillatani mai suna Baba ya karɓe iko da garin, har kuma ya kasance fulanin ke gadon mulkinsa, amma kuma ana kiran sarkin garin da suna 'Ɗan Gwarzo', don haka an samu cewa a lokacin jihadi, fulani basu yaƙi garin ba, har ma ana cewa Shehu Abdullahi Gwandu watau ƙani ga Mujaddadi Usman Ɗan Fodio, ya sauka a garin yayin da ya taho daga sokoto zai je Birnin Kano.
Don haka, bisa labarin zuwan wannan yaƙi, sai ake ganin duk da kasancewar garin Gwarzo a lokacin zagaye yake da ganuwa domin kariya daga mahara, amma lalle an tabbatar zuwan wannan sarkin bala'i ne ga garin. Don haka sai Ɗan Gwarzo na lokacin ya shiga shawarwarin mafita.
Akan haka wani bafaden sa ya bashi labarin wani malami mai suna Mallam Isah dake sokoto, tare da shawarar aje azo dashi domin samun kuɓuta daga wannan ƙangi.
Ɗan Gwarzo ya amince da wannan shawara, sannan ya tashi fadawa da abin alheri zuwa sokoto da hanzari. Da isar su suka gabatar wa da Mallam Isah saƙon Ɗan Gwarzo tare da buƙatar su ta ya biyo su zuwa garin Gwarzo domin taimakawa da adduar samun kariyar musibar dake tunkaro garin.
Abun da akayi kenan, Mallam Isah ya taso tare da fadawa suka nufo Gwarzo. Kwanci tashi sai ga su a garin. Ɗan Gwarzo yayi masa marhaban lale tare da sake gabatar masa da halin ƙuncin dake gaban su.
Mallam Isah yace masa kada ya damu, insha Allahu Allah zai yi maganin wannan fargaba. Sannan ya nemi a samu wani da zai yi masa jagoranci wajen kewaya ganuwar garin Gwarzo.
Ance Mallam Isah carbi ya ɗauka a hannunsa yana ja, yana lazimi, yana bin ganuwar data zagaye garin Gwarzo yana addua, bai gushe ba har sai da ya kewaye garin baki ɗaya, sannan ya koma masaukin sa ya zauna.
Aikuwa Allah da ikonsa, koda waɗannan maharan suka zo, sai garin ya ɓace musu, ance daga cikin Gwarzo ana jiyo sautin kiɗe kiɗen su da haniniyar dawakansu, amma kuma Allah ya hana su ganin garin balle su durfafe shinda yaƙi. A haka sukaƙaraci zaman su suka koma inda suka fito.
Jim kaɗan da faruwar haka sai Mallam Isah yace da Ɗan Gwarzo zai koma gida wajen ahalinsa, sai kuwa Ɗan Gwarzo ya shiga lallami da magiyar kada ayi haka, domin yana fargabar kada bayan tafiyar sa maharan su sake dawowa.
Babu yadda Mallam Isah ya iya, sai ya aike aka taho masa da ahalin sa daga Sokoto zuwa Gwarzo.. Kunji asalin yadda Manin Makwalla ya tashi a Gwarzo.
No comments:
Post a Comment