Thursday, 30 January 2020

WANENE SADIQ TUKUR GWARZO?

TARIHIN SADIQ TUKUR GWARZO
(Global Goodwill Ambassador)
  Shi bafillatani ne, an haife shi a garin Gwarzo, ya fito ne daga zuriyar Mallam Isah wanda Ɗan Gwarzo Baba ya gaiyato daga Sokoto domin tseratar da garin bisa wani mummunan hari da Ɗan baskore, sarkin Maraɗi na zamanin ke shirin kawowa wannan gari a ƙarni na goma sha takwas.
  Sadiq Gwarzo ya yi karatun addini dana boko a garin Gwarzo, sai a shekarar 2005 ya bar garin zuwa kwalejin fasaha mai suna GTC BAGAUDA domin kammala karatun sakandare, inda ya karanci fannin 'Carpentry and Joinery'. ya kammala karatun a shekarar 2008.
  A shekarar 2009 Sadiq Gwarzo ya yi karamar Diploma akan 'Computer Networking and Maintenance' a cibiyar koyar da karatun Kwamfuta ta Himma dake Gadon kaya a garin Kano, daga nan sai ya koma Gwarzo ya sake yin karatun karamar Diploma a 'School of Environmetal Studies' wadda ke ƙarƙashin 'Kano state Polytechnique', inda ya karanci 'Painting and Decoration'.
  Bayan ya kammala a shekarar 2011, sai kuma ya samu shiga 'School of Nursing kano' a shekarar 2012, ya kammala kwalejin a shekarar 2015 a matsayin cikakken majinyaci.
   Sannan yabsake komawa makarantar School of Hygiene a shekarar 2017 tare da karantar babbar diploma watau 'HND Public Health Nursing', inda ya kammala a 2019.
  Haka kuma yayi kwasa-kwasai da yawa ta yanar gizo daga  jami'ar buɗe ta ƙasar Australia, daga ciki akwai:-
-Anthropology: Becoming Human
-Origin of Crime
-Asronomy: Discovering the Universe
- Midwifery Education
-World Music
Da wasun su.
  Sadiq Gwarzo ya soma rubuta littafi tun yana firamare, kasancewar sa ya tashi a matsayin makaranci. Amma dai littafin sa na farko shine 'Nasara a Tafin Hannu' wanda ya wallafa a shekarar 2010. Daga nan sai 'Hikimar Allah Na Da yawa' a 2012, da 'Ilimin Kasuwanci' a 2015, sai kuma ' The Art OF Talking cure' a 2016.
Sauran littattafan da ya wallafa sune:
-Sabuwar Fuskar Ilimin Falsafanci
-Sirrin Rayuwa a cikin ilimin Lambobi
-Tarihin Tsohuwar Daular Baƙin mutum
-Kula da Lafiyar Mata masu ciki da kananun yara
-Asalin Hausawa daga kaɗe-kaɗen su
-Tarihin Daulolin Musulunci
-Magana Hausa
-Madubin Sarakuna
-Tarihin Jihadin Danfodio a Kasar Hausa
 Sadiq Gwarzo ya fi karkata akan rubututtukan da suka shafi 'tarihi', shiyasa wasu marubutan kan yi masa laƙabi da suna 'Gwarzon Tarihi', amma duk da haka ya yayi rubututtuka da dama akan fannikan siyasa, kasuwanci da zamantakewar rayuwa. Akan haka, ya rubuta muƙalu sama da 250 waɗanda ya taskance a turakar sa ta yanar gizo  http://sadiqtukurgwarzo.blogspot.com. Haka kuma ya taya Mallam Salisu Durmin Iya gabatar da shirin 'Hausa Rigar Siliki' a gidan Radiyon Guarantee na kusan tsawon shekara ɗaya a inda suka rinƙa tattaunawa akan tarihi da kafuwar ƙasashen Hausa. Baya da haka, Sadiq Gwarzo da taimakon masana kuma marubuta irin su Farfesa Yusuf Adamu, da wasun sa, sun kafa wata cibiya mai rajin bincike akan tarihin hausa da hausawa wadda suka sanyawa suna 'Center for the study of Hausa Civilisation', Ƙari akan haka, Sadiq Gwarzo na gabatar da ayyukan fassara ga kamfanoni na gida dana waje, da rubututtuka na tarihin ɗai-ɗaikun al'umma da kuma jaridu irin su Leadership Hausa, Manuniya da wasun su na yanar gizo. 
   A shekarar 2019 kungiyar duniya mai rajin tallafawa al'umma mai suna 'Global Goodwill Ambassadors' suka baiwa Sadiq Tukur Gwarzo lamba da sahalewar zama mamban su bisa ayyukan alheri da yake yi a fannonin taimakon al'umma. Tun kafin wannan lokacin, ya kasance a gaba-gaba wajen yaƙi da cututtuka masu damun al'umma misalin HIV, da Malaria  ga ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa.
    Zuwa yanzu, Sadiq Gwarzo na gabatar da ayyukan sa na rubuce-rubuce, da na ƙungiyoyi tare kuma da kasuwanci. Sannan tare da haɗin guiwar marubuci Ɗanladi Haruna, ya kafa kwalejin farko ta yanar gizo wadda ake koyar da ilimai da harshen Hausa. Babban burin sa shine Hausawa su sami ilimi a sauƙaƙe, su kuma soma gogayya da sauran al'ummar duniya akan haka. Dalili kenan da ya samar da kwalejin domin share fage ga duk wani son koyo da koyarwa. Kuma ana sa ran kwalejin zata fassara manyan ilimai da ake taƙama dasu a zamance anan duniya domin koyar da al'ummar Hausawa.
   Zuwa yanzu, Sadiq Gwarzo na da mata ɗaya, da ɗa ɗaya.
   

TARIHIN ZUWAN TURAWA AFIRKA TA YAMMA

TARIHI ABIN TUNAWA: ASALIN YADDA TURAWA SUKA BINCIKO AFRIKA TA YAMMA
Daga SADIQ TUKUR GWARZO
Tun da jimawa, Labarai masu ƙayatarwa suka cika kasashen Yammacin Turai dangane da yankin Afirka ta yamma. Tatsuniyoyi sun shahara akan haka. Labarin Attajiri Mansa Musa mai kyautar gwala-gwalai ya zamo abin jimami a Ingila, haka kuma labarin shaharar Kogin Kwara ba zai misaltu ba.
A wancan lokacin dai, turawa na ɗaukar birnin Tambuktu a matsayin birnin Gwal, domin haka ma suke yiwa garin laƙabi da suna 'birnin gwal', suna kuma da ƙarancin sani game da kogin Kwara.
A kan hakane aka kafa wata kungiya a birnin landan mai suna 'Association for promoting the discovery of the interior parts of africa' a shekarar 1788, wadda a taƙaice ake ambatar ta da 'African association'. Kungiyar, wadda sir joseph Banks ke jagoranta, ta ƙunshi manyan mutane, masana da attajirai, kuma tana da burin binciko zance mafi gaskiya dangane da Birnin Tambuktu, da kuma kogin Kwara. Wannan yunkuri shine asalin fara laluben turawa a kasashen Afirka ta yamma.
Akan haka, an rinƙa sauraron matafiya da sauran masu binciken tarihin duniya dangane da abinda suka sani game da Tambuktu da kuma kogin kwara. Ga misalin abubuwan da aka samo;
I. Bayani yazo daga James Bruce dan Kasar scotland, wanda a shekarar 1769AD ya isa kasar Habasha cewa "daular Tambuktu karkashin mulkin Muhammadu Askia I, tayi matukar karfi a wajajen ƙarni na 13 zuwa na 15, kuma itace ta mamaye mafi yawan ƙasashen yammacin Africa, tun daga yankin Gambiya da senegal, har zuwa sokoto dake ƙasar Hausa. A gabashi kuma sai da ta dangane da kogin kwara. Garin Timbuktu kuwa, yana dauke da baƙi masu yawa, kuma gari ne mai cike da arzikin gwal.
ii. An samu labari daga wani masani mai suna Al Hassan Bin muhammad al-Wazziniz zayyati wanda akewa Laƙabi da Leo Africanus (ma'ana zakin Afrika) wanda kuma akace kakannin sa na cikin gungun musulman da sukayi gudun hijira izuwa sassan duniya daga birnin Andaluz a shekarar 1492 sa'ar da Sarki Ferdinand da Sarauniya Isabella suka cinye garin da yaki, ga abinda ya  faɗa bayan ya samu damar ziyartar Timbuktu "ana kawo hatsi, shanu, madara da man shanu mai tarin yawa izuwa garin Timbuktu duk kuwa da kasancewar garin cikin sahara inda babu ƙoramu da lambuna. Babban abinda mutanen garin ke musayar kasuwanci dashi shine gishiri''.
Ya ƙara da cewa ''Sarkin Timbuktu attajiri ne na gaske, wanda ya mallaki sulalla na zinare marasa adadi. A koda yaushe kuma idan yana tafiya zaka samu kimanin dawakai 3000 suna rufa masa baya. Sannan yana da tarin likitoci, alƙalai, malamai masu wa'azi da sauran masana zazzaune a fadar sa''.
Daga wajen Leo Africanus ne kuma turawan ingila suka fahimci cewa Gishiri yana da matuƙar daraja a Timbuktu, saboda ya ayyana cewa zuwa akeyi dashi daga wani gari mai suna Tangaza, wanda yake da nisan Mil ɗari biyar daga Timbuktun. Har ma yake cewa "na taɓa kasancewa a Timbuktu a lokacin da farashin mangalar gishiri yake dai-dai da farashin sisin gwal tamanin".
iii. Wani bayanin ma ya samu daga hannun wani mai suna Asseed El hage Abd Salam Shabeeniy, wanda akewa laƙabi da Shebani, a wajajen shekara ta 1788. Shebani ya rayu a timbuktu tsawon shekara uku, inda har ya leƙa kasar hausa, ga kuma abinda ya naƙalto " Adadin mutanen garin timbuktu zai cimma dubu 40, banda bayi da kuma baƙi mazauna garin. Duk al'ummar garin baƙaƙen fata ne, sannan kuma kusan duk baƙon da zaije garin sai ya auri 'yar garin saboda kyawun matayen su. Kallo daya tak zai sa ka faɗa so da ƙaunar su"
Ƙari akan haka shine labarin Attajirin Sarkin Timbuktu Mansa Musa wanda ya baza duniya. Ance yayi zamani a wajajen ƙarni na 12, shine kuma ya taɓa ziyartar Saudiyya da ɗumbin bayi gami da ɗumbin gwala-gwalai.
Sai dai duk labaran nan, babu abinda akeji game da Kogin Kwara, kuma har izuwa lokacin kafuwar kungiyar, ba a samu wani bature farar fata ba wanda yayi ikirarin yaga Kogin kwara da idanuwansa.
A shekarar 1790, wani tsohon soja mai suna Daniel Houghton ya tunkari wannan kungiya ta 'African Association', da nufin amsar kwantiragen zuwa Africa ta yamma da ƙafa don gani da ido.
  Nan take kuwa kungiyar ta amince masa, ta kuma ɗora masa nauyin ziyartar Tafkin Barra kunda (wani gari dake ƙasar Gambiya) da kuma ƙasar Hausa tare da binciko ainihin inda garin Timbuktu yake, sannan ya ƙarƙare tafiyar a gaɓar kogin Kwara.
 Da yin haka, sai ya shiga kokarin koyon harshen Larabci tare da wani yare na ƙasar senegal mai suna 'Mandingo' ta yadda zai samu damar mu'amala da mutane.
Sannan ya sanya ranar fara tafiya.
A watan Oktoba na shekarar 1790, Hougton ya shigo jirgin ruwa, inda bayan wasu kwanaki ya sauka a gabar Kogin Gambia a wani gari da ake kira Barra. Ya tafi tiryan-tiryan har wani gari mai suna Pisania, daga nan ya risƙi wani gari da ake kira Jonkakonda, daga bisani kuma ya ƙaraso masarautar Wuli a farkon shekarar 1791.
A wannan wuri, ance Sarkin Masarautar Wuli ya karɓi Houghton da girmamawa, har ma ya bashi mazauni a garin sa mai suna Medina. Sai dai ba a jima ba abokan hamayyar Sarkin suka kawowa garin hari, inda kuma sukaci nasarar kone garin, har ma kayyayakin Houghton na yaƙi da wasu abubuwa masu amfani suka ƙone ƙurmus. Wannan abu yayi masa ciwo matuƙa.
Duk da haka, Houghton baiyi ƙasa a guiwa ba, inda yaci gaba da tafiyar sa yana neman garin Timbuktu.
  Ance a wajajen watan Mayu na shekarar 1791, Houghton ya bar gaɓar tekun Barra, sannan ya kutsa kai don tunkarar Timbuktu. A lokacin ne kuma ya tura da saƙo zuwa Ingila mai ɗauke da labarin yadda tafiyar sa take kasancewa. Saƙon ya isa birnin Landan cikin nasara.
Daga nan, Houton ya samu damar gewayawa ta kogin Senegal, shine ma sarkin wani gari yaci mutuncinsa, da ƙyar ya samu kuɓuta ya isa masarautar Ferbanna dake yankin Bambu na ƙasar ta senegal acikin damuna ta wannan shekara.
Daga nan ne kuma ya hadu da wani Matafiyi mai suna Madegammo, wanda yayi alƙawarin zai yiwa Houghton jagoranci izuwa birnin Timbuktu a kyauta. Sun fara wannan tafiya ne a watan yulin 1791, shine har Houghton ya ƙara turawa da saƙo gida yana mai labarta yarjejeniyar da sukayi da matafiyin, ya aika saƙon ne ta hanyar matafiya, kuma sannu-a hankali ya isa birnin landan.
  Wannan saƙon shine ya zamo na ƙarshe, domin daga nan ba a ƙara jin ɗuriyar sa ba.
A shekara ta 1793, labari mai tushe ya riski Landan cewar Houghton ya samu kansa cikin mawuyacin hali yayin tafiyarsa zuwa Tambuktu, wannan ne yasa tafiyar ta sire masa, abokan tafiyar sa kuma suka ribace shi, inda suka sauya akalar tafiyar izuwa wani gari mai suna Tisheet (wanda yake a ƙasar Mouritania a yanzu). Amma kwana biyu da yin haka, sai Houghton ya fuskanci cewa abokan tafiyar sa na yunƙurin hallaka shi, wannan yasa ya tsere musu, ya shiga cikin sahara ba ruwa ba abinci a tare dashi, a daddafe ya isa wani gari mai suna Tarra, inda kuma cikin rashin sa'a, mutanen garin suka hanashi ruwa da abinci, wannan yasa yunwa ta halaka shi.
  Ance ko gawar Houghton mutanen garin ƙin binne ta sukayi, a ƙarshe tsuntsaye ne suka yagalgalata a banza.
Wannan labari yayi matuƙar ɓatawa Ingila Rai, sannan ya dakushe guiwar masu son jin labarin africa ta yamma da yawa.
   Amma ba'a fi shekaru biyu ba, sai ga takarda daga hannun wani baturen ƙasar scotland mai suna MUNGO PARK, yana neman sahalewar ƙarasa aikin da Houghton ya fara..
Tafiyar mungo park (wadda tarihin ta yazo a littafin Mungopark Mabuɗin Kwara) tana ƙunshe da darasi mai tarin yawa. A cikin ta ne mukaji yadda iyaye da kakanni suka rayu a wancan zamani, da kuma yadda Mungopark ya rinƙa bibiyar matsalolin da marigayi Houton ya fuskanta, har ma da laifuffukan da ya yiwa sarakunan africa ta yamma, dalilin dayasa suka tsaneshi kuma kenan har abin ya kai shi ga halaka!

TARIHIN MAHAIFIN MANI MAKWALLA DA YADDA YA KUƁUTAR DA GARIN GWARZO

TARIHIN MANIN MAKWALLA
Sunan Mahaifin Manin Makwalla Mallam Isah, shi Bafillatani ne Batoranke, kuma malami masanin asararu, a sokoto yake da zama.
  Wata rana a wuraren ƙarni na goma sha takwas kafin zuwan turawan mulkin mallaka, watau jim kaɗan da yin jihadin fulani a ƙasar Hausa, sai wani sarki ya aiko da goron yaƙi zuwa garin Gwarzo.
  Garin Gwarzo an sani cewa Bamaguje Gwarzo ne ya kafa shi, amma daga baya wani Bafillatani mai suna Baba ya karɓe iko da garin, har kuma ya kasance fulanin ke gadon mulkinsa, amma kuma ana kiran sarkin garin da suna 'Ɗan Gwarzo', don haka an samu cewa a lokacin jihadi, fulani basu yaƙi garin ba, har ma ana cewa Shehu Abdullahi Gwandu watau ƙani ga Mujaddadi Usman Ɗan Fodio, ya sauka a garin yayin da ya taho daga sokoto zai je Birnin Kano.
   Don haka, bisa labarin zuwan wannan yaƙi, sai ake ganin duk da kasancewar garin Gwarzo a lokacin zagaye yake da ganuwa domin kariya daga mahara, amma lalle an tabbatar zuwan wannan sarkin bala'i ne ga garin. Don haka sai Ɗan Gwarzo na lokacin ya shiga shawarwarin mafita.
   Akan haka wani bafaden sa ya bashi labarin wani malami mai suna Mallam Isah dake sokoto, tare da shawarar aje azo dashi domin samun kuɓuta daga wannan ƙangi.
  Ɗan Gwarzo ya amince da wannan shawara, sannan ya tashi fadawa da abin alheri zuwa sokoto da hanzari. Da isar su suka gabatar wa da Mallam Isah saƙon Ɗan Gwarzo tare da buƙatar su ta ya biyo su zuwa garin Gwarzo domin taimakawa da adduar samun kariyar musibar dake tunkaro garin.
Abun da akayi kenan, Mallam Isah ya taso tare da fadawa suka nufo Gwarzo. Kwanci tashi sai ga su a garin. Ɗan Gwarzo yayi masa marhaban lale tare da sake gabatar masa da halin ƙuncin dake gaban su.
Mallam Isah yace masa kada ya damu, insha Allahu Allah zai yi maganin wannan fargaba. Sannan ya nemi a samu wani da zai yi masa jagoranci wajen kewaya ganuwar garin Gwarzo.
Ance Mallam Isah carbi ya ɗauka a hannunsa yana ja, yana lazimi, yana bin ganuwar data zagaye garin Gwarzo yana addua, bai gushe ba har sai da ya kewaye garin baki ɗaya, sannan ya koma masaukin sa ya zauna.
Aikuwa Allah da ikonsa, koda waɗannan maharan suka zo, sai garin ya ɓace musu, ance daga cikin Gwarzo ana jiyo sautin kiɗe kiɗen su da haniniyar dawakansu, amma kuma Allah ya hana su ganin garin balle su durfafe shinda yaƙi. A haka sukaƙaraci zaman su suka koma inda suka fito.
Jim kaɗan da faruwar haka sai Mallam Isah yace da Ɗan Gwarzo zai koma gida wajen ahalinsa, sai kuwa Ɗan Gwarzo ya shiga lallami da magiyar kada ayi haka, domin yana fargabar kada bayan tafiyar sa maharan su sake dawowa.
Babu yadda Mallam Isah ya iya, sai ya aike aka taho masa da ahalin sa daga Sokoto zuwa Gwarzo.. Kunji asalin yadda Manin Makwalla ya tashi a Gwarzo.

Wednesday, 11 December 2019

TARIHIN GARIN WUDIL

TARIHIN GARIN WUDIL

Sadiq Tukur Gwarzo
Garin Wudil na ɗaya daga manyan garuruwa a jihar kano kuma gari ne mai ɗauke da tarihi, don haka muka ga dacewar taskance kaɗan daga ɗumbin tarihin wannan gari.
  Ance wani maharbi ne ya sari garin, shikuwa daga Katsina ya taso. Tana iya yiwuwa Muhammadu sunansa, ko kuma Daudu, amma dai an tabbatar shine na farko da yazo ya zauna a wannan wuri inda garin wudil yake a halin yanzu.
   Ko da yake, da fari ance acan tsallaken ruwa ya soma zama, amma sai yayi tunanin yin amfani da ruwa wajen kare kansa da garin da zai kafa daga mahara kasancewar wancan lokaci ana cike da yake-yake da kamen bayi, don haka ya tsallaka ruwa sannan ya kafa Bukkar sa yana mai cigaba da sana'ar sa ta farauta a dajin dake kewayen kogin wudil.
  Sannu a hankali mutane matafiya masu zuwa neman ruwa suka rinka sauka a kusa dashi. Tun wasu na sauka su ɗanyi kwanaki sannan su tashi izuwa inda suka dosa, har kuma aka samu waɗanda suka mayar da wajen kachokan wajen zama tamkar shi. Akan haka akace gungun wasu fulan Joɓawa suka riski wannan maharbin tare da zama kusa dashi. Daga baya kuma sai shugabancin garin ma ya koma hannun su.
Sunan wudil ya samo asali ne daga wata Aljanna da aka tabbatar tana zaune a gidanta dake cikin tsakiyar wannan ruwa na Wudil. Ana kiranta da suna 'Uwar Wudil'.
Babu tabbacin lokacin da aljannar ta soma zama acikin ruwan, amma dai an tabbatar da cewa har yanzu tana nan tare da ahalinta.
  Ance ita fara ce doguwa mai siffar balarabiya, gashinta har gadon baya yake, kuma bata cutar da mutane, domin abaya takan shiga cikin garin Wudil ta yadda har mutane kanci karo da ita ba tare da ta razanar dasu ba. Ansha kuma ganinta a sauran garuruwa dake jikin wannan kogi na wudil.
Aljannar Wudil tana da tsohuwar alaka da mutanen garin wudil. Domin an samu cewar tana taimakon garin wajen samun kariya daga dukkan sharri tare kuma da yin galaba a yakunan da duk garin zai tunkara. Ance abaya, manyan gari na zuwa bakin kogi su yanka shanu, raguna ko tumaki sannan su sanar mata da abinda ya tasowa garin misalin yaƙi sannan sai azo a tafi. Ita kuma aikinta ne tayi duk mai yiwuwa wajen ganin buƙata ta biya.
  Wannan abu yana daga abinda Mallam Bakatsine ya ƙyamata tare da riƙa a matsayin hujjar yin jihadi a  zamanin Shehu Usman Danfodio. Don haka ance da lokacin hijira yayi, sai mabiya Shehu Usmanu dake kano suka tafi wani waje da ake kira Kwazazzabon Ƴarkwando, amma shi Mallam Bakatsine sai ya fita kano ta gabas yaje garinsu Utai ya ɗauki iyalinsa sannan ya ƙarasa garin wudil, inda ya yada zango a wani wuri da ake kira Nagge, anan ya tara runduna tare da zuwa buga yaƙi da garin Gaya inda ya ƙwace iko dashi.
 Duk da kasancewar a lokacin Garin Wudil zagaye yake da ganuwa da kuma ɗumbin jarumai, kuma karkashi Sarkin Kano Alwali amma babu labari mai nuna cewa sarakunan wudil sun yaƙi Mallam Bakatsine, ance hakan baya rasa nasaba da kasancewar a zamanin Fulani ke mulkin garin kuma suna da alaƙa dashi, don haka suka mara masa baya har ya cimma burinsa.
  Ana kiran sarautar wudil da suna Ɗan Daudu, kuma garin yana can gabas da garin kano da misalin tazarar mil talatin. 

Wednesday, 9 October 2019

TARIHIN TSOHON BIRNIN HAUSAWA; KAFIN DABGA

TARIHIN TSOHON BIRNIN HAUSAWA; KAFIN DABGA

SADIQ TUKUR GWARZO, GGA

  Daga cikin tsoffin biranen da Maguzawa suka kafa waɗanda kuma suka shahara a ƙasar Kano tun kafin zuwan jihadin Fulani akwai wannan tsohon garin mai suna 'Kafin Dabga'.
   Wani mashahurin mayaƙi bamaguje mai Suna 'Dabga' ne ya sari garin, shine kuma yayi masa kafi gagarumi domin kuɓuta daga dukkan harin mayaƙan wancan zamani, don haka ake kiran garin da suna Kafin Dabga.
   Garin ya haɓaka, ya shahara, kuma ya samu ɗaukaka. A baya ance zagaye yake da ganuwa, wadda aka yiwa ƙofofi guda huɗu. A kowacce kofa mace da namiji ne suka tsaya aka yaɓe su da ransu saboda surkulle, sannan da wata ƙaya sarƙaƙiya ake rufe kofar shiga birnin ba da ƙofa ba. Don hakangarin ya kasanxe mai tsananin uytsaro.
Idan yaƙi yazo, daka ake sanyawa ayi da dare, sai mayaƙa su shirya da hanzari. Masu kwari da baka su hau saman ganuwa, masu masu da takubba su shige surƙuƙi suna sauraron ko-ta-kwana.
Daga cikin sarakunan da ake iya tuna sunayen su a wannan gari, ance sunan Sarkin Kafin Dabga na farko Dugaji, Bamaguje ne, yayi wannan sarauta kimanin shekaru 400 da suka gabata, ko da yake tsufan kukokin garin da marinar garin na iya kaiwa sama da waɗannan shekarun. Amma dai kwatancin shekarun da ake tsammanin an soma sarauta a garin kenan.
Bayan mutuwar sa sai shi Dabga yayi mulki, wanda asali ance ya zamo tamkar uba ne mai ɗora wanda yake so shugabanci a garin.
 Daga shi sai Also, sannan sai Abdullahi ya fara mulki a zamanin da Fulani suka karɓe sarauta.
Akwai manyan gidajen da har yanzu ake ambata a garin, waɗanda sukayi gadon shugabancin garin, da kuma jarumta tun kafin jihadin fulani, misalin su shine; Gidan Nazundumi, Gidan Dankali, Gidan Butsatsa, da Gidan Gigo.
KUKAR ƳAR FULANI
Akwai wata kuka mai tarihi a wannan gari mai suna kukar ƴarfulani. Ita ƴar fulanin aljanna ce wadda ake da yaƙinin akan wannan kuka gidan ta yake.
Ance a zamanin baya, tana taimakon garin lokacin da yaƙi ya taso, ko kuma wani mugun abu ya nufo garin, inda take sanya sarƙa ta kanan-naɗe mahara.
Ance kuma a zamanin mulkin sarki Abdullahi na garin, yana sanyawa a kai mata ƙwaryar nono da farin goro duk ranar juma'a, ita kuma takan yin shewa da godiya yadda duk wanda ke garin sai ya ji.
TARWATSEWAR KAFIN DABGA
Kafin garin kafin Dabga ya samu raguwar mazauna, ya kasance shahararre mai cike da mutane wanda ya kasance daga gari-gari akan zo masa don yin fatauci.
Sannan garin yayi yaƙe-yaƙe da biranen dake kusanci da ma na nesa misalin Gammo da Ƙiru, har ma ana cewa ba a taɓa cin garin da yaƙi ba.
Sai dai wata annoba da ta faɗawa garin ce tayi sanadiyyar ɗaiɗaicewar sa.
Ance wata baƙar aljana ce ta rinƙa halaka mutane.
Idan dare yayi sai tayi shewa, tace 'Kun Taru?', to fa duk wanda yayi ko da gyaran murya a wannan daren ba zai wayi gari ba. Daga nan aka sanyawa annobar suna 'Kun-Taru'.
Don haka aka rinƙa wayar gari da gawarwakin mutane burjik waɗanda ta halaka, hakan yasa mutanen garin da dama suka ƙaurace masa.
A yanzu dai, garin Kafin Dabga yana nan ƙarƙashin garin Karaye, a jihar kano.

Monday, 12 August 2019

TARIHIN NUFE: KAFUWAR ƘASAR NUFE Kashi na huɗu

TARIHIN NUFE: KAFUWAR ƘASAR NUFE
Kashi na huɗu
SADIQ TUKUR GWARZO
    Marubuci Buhari Daure ya ruwaito a littafinsa 'Tarihi da Al'adun Mutanen Najeriya' cewa kafuwar ƙasar Nufe ya wanzu a wajajen ƙarni na goma sha shidda ne. Inda yace asalin Nufe dana Igala ɗaya ne, sai wani ɗan sarkin masarautar Idah mai suna Tsoede yayi gudun hijira tare da kafa masarautar Nupe wadda ta haɗe ƙauyukan Beni, Bidda, Benu, Debo, Tafiya, Doka, Gaba, Dibo da Kupa.
Amma binciken Dr. Sidi Tiwugu Shehi ya kawo ra'ayoyin masana da yawa  saɓani da wannan.
Daga ciki akwai masu cewa asalin Nufawa zuriyar wani balarabe ne mai suna Uqba bn Nafiu wanda ya baro ƙasar su ta larabci tare da zama a ƙasar Nupe.
Wasu kuma suka ce Nufawa sun fito ne daga wani Mafarauci balaraben Misira mai suna Abdulaziz wanda ya gudo daga ƙasar sa ya sauka a Doko Dazi cikin ƙasar Nufe dashi da ahalinsa. Daga nan aka sanya musu suna 'Nefiu' da yaren ƙabilar Beni daya tarar, wanda ke nufin 'wanda ya gudo daga wani wuri' .
Sannu a hankali sai sunan ya sauya zuwa Nufe ko Nupe.
Wasu kuma sunce Asalin Nufawa daga ƙasashen Katsina, Kano da wasu makusanta suke. Har ma Clapperton yace sunan Sarkin su Tsoede, kuma sun zo ƙasar Nupe ne daga wani birni da ake kira Attah Gara.
   Shikuwa Ndagi Abdullahi ya tafi akan cewa Nufawa suna kakannin Hausawa, Yarabawa da Inyamirai. Inda yace zuriyar Nufawan ce ta fantsama tare da samar da waɗannan yaruka (ko ace ƙabilu)
Amma dai masani S.F Nadel ya raba Nufawa gida huɗu daga abinda ya kawo a littafinsa mai suna 'Social Symbiosis and Tribal Organisation'. Ga rukunan kamar haka:-
Rukuni na ɗaya sune Ndachezhi, watau Mafarauta kuma asalin mazauna ƙasar Nupe waɗanda akace suna zazzaune a ƙauyuka sama da shekaru dubu da suka gabata.
Rukuni na biyu sune Esozhi, suma asalin Nufawa ne waɗanda suka jima a ƙasar Nufe har ma suka  kafa birnin Kutigi.
Rukuni na uku sune Benu, waɗanda suka yo hijira daga ƙasar Bornu. Su kuwa da yawansu malaman addinin Islama ne da masu fatauci, daga baya ne suka samu ikon wasu yankunan Kutigi.
Sai Rukuni na huɗu waɗanda ake kira Konu, waɗanda asalinsu bayi ne da aka kamo wurin yaƙi daga ƙasashen Yarabawa, daga baya aka ƴantar dasu tare da basu mazaunai a ƙasar Nupe.
Sannan binciken masana kimiyya da aka gudanar a yankunan Jebba, Giragu, Tada, Oyo-ile, Esie-oba da wasun su ya nuna cewar ƙasar Nupe tana ɗauke da mutane tun sama da shekaru 3000 zuwa dubu 10,000 kafin haihuwar Annabi Isah A.S.
Wannan yasa ake hasashen cewar asalin ƙabilun da suka rayu a wannan yanki wanda ya mamaye yankin Abuja da wasu yankunan tsakiyar Nigeria, sune suka haifar da ƙabilun Yarabawa, Inyamirai, Nupawa, Igala, Idoma, Ebira da Gbayi.

Saturday, 13 July 2019

TARIHIN HAUSANDA HAUSAWA: MAHANGA TA 7

TARIHIN HAUSA DA HAUSAWA: MAHANGA TA 7
Sadiq Tukur Gwarzo

Littafin 'Hausawa da Maƙwabtan su' wanda turawan mulkin mallaka da haɗin guiwar wasu hausawa suka samar mai ƙunshe da tarin zantuka  game da tarihin Hausawa da maƙwabtan su ya danganta asalin Hausawa ga Borno.
   Aka ce Sarkin Borno na da wani bawa mai suna Bawo, babu wanda ya san asalin sa, ko dangin sa. Amma abinda aka sani shine Sarkin Borno ya jiɓanta shi a kan biranen Hausa guda bakwai da ake kira Hausa bakwai yana mai riƙe dasu yana tattara haraji tare da kula da lamurorin su, har ya haifi ƴaƴa bakwai.
   A zamanin da ya ga alamun mutuwa sai ya sarautar da waɗannan garuruwa ga ƴaƴayen nasa. Kowannen su ya bashi birni guda.
  Har aka ce wanda ya sa a Daura ba namiji bane, mace ce mai suna Daura. Saboda haka ake ambaton garin da sunanta.
   Haka kuwa itace babba a cikin ƴaƴansa, itace ƴaruwar sarkin katsina da sarkin Kano da sarkin Gobir, domin dukkan su uwarsu ɗaya.
   Kuma sarkin Burmi da Sarkin Zazzau uwarsu ɗaya. Sarkin Rano kuwa shi kaɗai ne wurin uwarsa.
Saboda haka sai ya zamana ƴaƴayen sun cigaba da bayar da harajin ƙasashen su zuwa Daura, daga nan kuma ana aikawa Borno zuwa ga Sarkin ta.
Sarkin Gobir Bawa kaɗai ne ya ƙi bada harajin nan, sai kuwa yaƙoƙi suka rinƙa aukuwa tsakanin garuruwan da Borno, daga bisani ya ƴamtar da ƙasashen Hausa daga Borno.
Wannan abu tabbatacce ne a cikin labarun da aka faɗe su, haƙiƙa asalin su ƴaƴa ne, su ne ragowar Kibɗawa. Su kuma Kibɗawa sune jama'ar Fir'auna da suka tafo daga Misira suka cika garuruwan Ahira har suka tafi Gobir suka fitad da waɗanda suke cikinta, sune waɗanda suka mallake ta daga ƴaƴan Bawo suka karɓe sarauta daga hannun mutanen wajen. Suka rinƙa yin aiki daga abinda suka iske ƴaƴan Bawo suna yi, suna masu biyan haraji har zuwa lokacin da Bawo ya hana biya.