Monday, 13 July 2020

ƘABILAR MAASAI: DALILIN SHAN JINI DA KIWON SHANU

ƘABILAR MAASAI: DALILIN SHAN JINI DA KIWON SHANU
Sadiq Tukur Gwarzo, GGA
Maasinta,  shine ake ɗauka Uba kuma wanda ya samar da tsatson ƙabilar Maasai, ance ya samu kyautar shanu ne daga Ngai – Ubangijin sama- wanda ya sauko da shanun daga sama zuwa ƙasa acikin salkar fata.
  Tun daga wannan lokacin suke kallon shanu a matsayin tsarkakku,  kuma darajar su tana kaiwa kafaɗa da kafaɗa data ƴaƴansu. Hakika yawan yara da yawan shanu ke nuni da tumbatsar mutumin ƙabilar Maasai.
Dajin da ya ratsa shahararrun yankunan Ngorongoro, Amboseli, Serengeti, Masai Mara da Tsavo dukkan su nan ne wuraren kiwon alummar Maasai. Kabilar Maasai na amfani da yaren Maa ne, kuma ana samun su a yankunan kasashen Kenya da Tanzania.
Haka Kuma duk da yadda sauyin zamani ke tunkuɗe al'adu ga ƙabilun duniya, amma kabilar Maasai suna yaƙi tukuru wajen kere al'adun su na kaka da kakanni, don haka suka yi shura a cikin ƙabilun kudancin afirka musamman wajen kiwon shanun su, tafiya bisa tituna ko rawar adumu.
Daga cikin shahararrun al'adun gargajiya na ƙabilar Maasai akwai rawar tsalle ta adumu, sanya tufar 'shuka' mai kaloli, da yin kaki ko kuma kwankwaɗar jini.
Adamu shine sunan rawar tsalle-tsalle da akeyi a matsayin biki yayin da yara matasa suka zama mahankalta waɗanda suka isa aure. Ana rera wakoki  nangargajiya yayin bikin, sannan wanda tsallen sa yafi na kowa shine yayi nasara, kuma shi ke samun macen aure da tafi ta saura.
Kalar tufafin shuka da suka fi sanyawa itace Ja, wadda take wakiltar jini, kuma take a matsayin kariya a garesu ga namun daji. Yayin da shuɗiya ke nufin sararin sama wadda ke samar da ruwan sama ga shanu. Kalar rawaya kuwa na nufin haihuwa da girma. Baki ɗayan waɗannan tufafi na su ke ƙara musu keɓantaka a cikin ƙabilun afirka.
Kasancewar a cikin wasu ƙabilun ana ƙyamar kaki, amma a Maasai shi abin so ne, domin babban abin girmamawa ne idan zaka gaisa da mutumin da kake girmamawa sai kayi kaki ka tofa a tafin hannu sannan ka miƙa masa hannun ku gaisa. Hakan na nufin share dukkan wani sharri daga tafin hannun, haka kuma idan kaje barka sai ka tofa kakin ka a goshin yaron sannan ka nuna soyayyar ka a gare shi. Shan jini kuwa wani abu ne da ya zama ruwan dare a garesu.
 Don haka alummar ƙabilar Maasai na shan jini ne a matsayin sinadarin ƙara lafiya da kuzari. Jinin da suka fi sha kuwa shine na saniya, wanda har sukan gauraya shi da madara su kwankwaɗa abinsu a duk sanda suke so.
   Zuwa yanzu kabilar ta rarrabu zuwa 21 kamar haka, kuma kowacce na da ɗan sirkin al'adu da saura:- Keekonyokie, Damat, Purko, Wuasinkishu, Siria, Laitayiok, Loitai, Kisonko, Matapato, Dalalekutuk, Loodokolani, Kaputiei, Moitanik, Ilkirasha, Samburu, Lchamus, Laikipia, Loitokitoki, Larusa, Salei, Sirinket and Parakuyo

Sunday, 5 July 2020



AL'ADA MAI BAN MAMAKI:  DALILIN RASHIN WANKA A KABILAR HIMBA 
Sadiq Tukur Gwarzo, GGA
08060869978
  Kabilar Himba da ke kasar Namibia rukunin wasu kaɗaitattun mutane ne waɗanda ɗabi'an su suka zamo bare, ko ace ababen mamaki ga sauran mutanen duniya.
 Akan kira su da suna Ovahimba ko Omhimba, suna rayuwa ne a yankin Kunene cikin kasar Namibia.
Daga cikin al'adun su da suka sha banban da mafi yawan sauran al'adu, akwai al'adar su ta tarbar baƙo da mata domin yin jima'i da su, da kuma sanyawa jarirai tsakiya a wuya tun suna zanin goyo. 
 Sannan basu cika cuɗeɗeniya da sauran kabilu ba balle har a samu sauyin al'adun da suka yi gado kaka da kakanni, waɗannan mutanen suna matukar kokari wajen ganin basu yi aron wata baƙuwar al'ada ba komai kyawunta, don haka muna iya cewa mafi yawan ababen da suka yi riko tun na kaka da kakanni ne.  
Sana'o'in da mazajen kabilar suka fi riko dasu  sune kiwo da noma, matan su kuwa sunfi damuwa da shiga daji samo itacen hura wuta don girka abinci da kuma jigilar samar da ruwan sha ga ahalin su.
  Suna bauta ne ga allolin iyayen su, sannan mazaje na auren mace sama da ɗaya, suna kuma yiwa yara mata aure tun da kuruciyar su.
Babban abin mamaki dangane dasu shine rashin yin wanka da ruwa. Yana daga al'adar da suka yi gado ta rashin wanka da ruwa kwata-kwata a rayuwar su, dalilin haka kuwa ance baya rasa nasaba da rashin kyawun yanayin yankin da suke raye. Yankin su ya shafi sahara ne, samun ruwa na da matukar wahala a tattare dasu. Don haka darajar sa ya sanya suke ganin tamkar asara ne a kwarar dashi wajen wanke gangar jiki.
  Sai dai kuma hakan bai sanya sun zama ƙazamai munana ba, ta yadda suka bullo da wata dabara wajen tsaftace jikin su wajen amfani da albarkatun dake zube a yankin nasu.
   Dabarun sune;  goge jikkunnan su da wata irin kuɓewa ja dake fito musu, sai kuma yin sirace a kullum don tsaftace jikkunan su.
   Yadda suke siracen shine, ana zuba garwashi a rufaffen mazubi mai cike da garin magani da kofa a sama, don haka da zarar hayaki ya soma tashi sai mutum ya durƙusa yana mai kara jikin sa ga tururin wanda zai rinƙa shiga sassa daban daban na jikin yana tsaftace shi. 
Ƙabilar Himba na da matukar son baƙo, tare da kyautata masa, amma fa basa bari baƙuwar al'ada ta gauraya da tasu.