Sunday, 1 November 2020

TARIHIN JAGABAN, CHIF BOLA AHMED TINUBU

 ikakken sunan sa shine Bolanle Ahmed Adekunle Tinubu

Bolanle; a yarbanci na nufin, "wanda aka haifa cikin arziƙi," Adekunle kuma na nufin ; "Ƙari akan adadin yalwa da arziƙin iyali''. Sunan Ahmed kuwa  daga sunan shugaba ne Annabi Muhammad, S.A.W, wanda yake shine Muhammad Ahmad, cikamakin annabawa, abin godiya.

Shine mai rike da sarautun 'Asiwaju' na Lagos da kuma 'Jagaban' na masarautar Borgu dake jihar Niger.

An haife shi a ranar 29 ga watan Maris na shekarar 1952 a mafi inganci, a cikin birnin Ikko (Lagos). Shi musulmi ne.  Ya halarci makarantar firamare mai suna St. John's Primary School, dake Aroloya a Lagos, sai sakandiren Children's Home School dake Ibadan. Tinubu ya samu tafiya kasar Amurka domin karo karatu a shekarar 1975, inda ya soma karatu a kwalejin Richard J. Daley College dake Chicago, Illinois kafin daga bisani ya koma jami'ar jihar Chicago mai suna Chicago State University. Ya samu kammala digirin sa a shekarar 1979 daga wannan jamiar inda ya karanci Ilimin gudanarwar kuɗi da ake kira "Accounting".


Tinubu yayi aiki da kamfanin Amurka mai suna Arthur Andersen, da kuma wasu kamfanonin irin su Deloitte, Haskins, & Sells, da GTE Services Corporation duk a can Amurka. Bayan komowar sa gida Nigeria a cikin shekarar 1983, Bola Tinubu ya soma aiki da kamfanin Mobil Oil Nigeria, kafin daga bisani ya zamo cikin jagororin kamfanin.

 Ya soma shiga harkokin siyasa ne a shekarar 1992, lokacin da ya shiga jamiyyar Social Democratic Party (SDP) inda ya zamo mamba na ɗariƙar  'Peoples Front' wanda marigayi Shehu Musa Yar'Adua ke jagoranta, ɗarikar da ta ƙunshi manyan ƴan siyasu irin su marigayi shugaba Umaru Yar'Adua, Atiku Abubakar, Baba Gana Kingibe, Rabiu Kwankwaso, Abdullahi Aliyu Sumaila, Magaji Abdullahi, Dapo Sarumi da Yomi Edu da wasunsu. 

  An zaɓi Bola Tinubu a matsayin sanata mai wakiltar sanatoriyar Lagos ta yamma a jamhuriya ta uku wadda bata yi nisan zango ba sojoji suka yi juyin mulki tare da rushe mulkin dimokraɗiyya baki ɗaya.


 Bayan soke zaɓen shugaban ƙasa na kwanan watan '12 June' na shekarar 1993, sai Tinubu ya zamo ɗaya daga iyayen da suka kafa gungun kungiyoyin rajin dawo da mulkin dimokraɗiyya a Nigeria, kungiyar da ta shiga wayar da kan ƴan ƙasa akan nuna rashin goyon bayan mulkin soja da kuma ayyana marigayi Moshood Abiola a matsayin wanda yaci zaɓen shugaban ƙasa da aka soke na ranar 12 ga watan yunin 1993. 

Don haka, juyin mulkin da marigayi Shugaban ƙasa a wancan lokaci Abacha yayi na zamowa shugaban ƙasa da kuma yunkurin da yayi na ɗaukar tsauraran matakai akan masu niyyar bashi matsala a mulkin sa, sai Tinubu ya ƙetare ya bar Nigeria, bai sake dawowa ba sai bayan rasuwar Abacha a shekarar 1998, inda aka soma kafa tubalin ginin jamhuriya ta huɗu. 


A zaɓen shekarar 1999, Bola Tinubu ɗaya ne daga shugabannin jamiyyar Alliance for Democracy (AD), tare dasu Abraham Adesanya da Ayo Adebanjo. Ya shiga zaɓen firamare na jamiyyar ta AD a matsayin ɗan takarar ta na Gwamnan jihar Lagos, kuma ya samu nasara, inda ya doke abokan takarar sa na lokacin  Funsho Williams da Wahab Dosunmu, tsohon ministan ayyuka a Nigeria. Don haka a zaɓen shekarar 1999, Bola Tinubu ya samu tsayawa takarar gwamnan jihar Lagos a karkashin tutar jamiyyar AD, tare da samun nasarar lashe zaɓen cikin kwanciyar hankali.

A zaɓen shekarar 2015 kuwa, Tinubu shine jagoran gamin gambizar jamiyyan AC, ANPP, da CPC waɗanda suka dunƙule tare da komawa inuwar jamiyyar APC. Shine kuma ya jagoranci marawa shugaban ƙasa Buhari baya har ya samu tikitin takara a jamiyyar ta APC, har kuma daga bisani ya samu nasarar lashe zaɓen shugabancin ƙasar baki ɗaya.

No comments:

Post a Comment