Tuesday, 10 July 2018

TARIHIN KARAYE

TARIHIN KARAYE

Daga Sadiq Tukur Gwarzo
  08060869978

Littafin 'Ƙaraye Maƙarar Maganar Kano' da Alh Shehu Garba Ƙaraye da kuma Umar Ƙaraye suka wallafa ya kawo manyan muhimman batutuwa na tarihi da suka faru a Ƙaraye.
   Daga ciki, sunyi maganar Wanzuwar garin ƙaraye tun kafin soma sarautar Bagauda a Kano, a shekara ta 999 miladiyya.
   Littafin ya tafi akan cewa tun da jimawa, akwai maguzawa da suke zaune a garin ƙaraye, waɗanda suke bautawa bishiyoyin kukoki da kuma na Rimaye.
  Daga Rimayen da aka samu ana yiwa bauta don samun tagomashi akwai Rimin yaki-yaki, Rimin Kwatankwaro, Rimin tagwaye, da Rimin kofar Zango. Sai dai littafin bai faɗi asalin daga inda waɗannan mutane maguzawa suka zo ba.
   Dangane da sunan wannan gari na Ƙaraye kuwa, a wani wuri littafin ya faɗi cewa Sunan shugaban Maguzawan farko a garin shine Ƙaraye, don haka ake kiran garin da sunansa.
Amma kuma a wani wuri na daban, littafin ya sake kawo cewar sunan ƙaraye ya zone daga yawaitar Ƙaro dake wata bishiya a tsakiyar garin.
     Garin ya soma kafuwa ne a arewa da inda yake a yanzu, kuma anan ya wanzu tsawon lokaci har bayan jihadin fulani, sannan ya dawo inda yake da zama yanzu. Koda yake, har yanzu ana kiran wancan gari da suna tsohuwar ƙaraye, domin akwai mutane zaune acikinsa. Kuma akwai alamu masu nuni da tsufan gari da kai tsaye akan iya lura da zarar an shiga cikinsa.
   Ana ganin Ƙaraye ta girmama, kuma ta shahara a zamanin baya, ta yadda faɗaɗar ta ya tuƙe da ƙasashen Katsina, Zaria da kuma kano, kafin daga bisani a kacaccala ta.
Haka kuma tayi tashen sadaukantaka da ƙarfi wurin yaƙi, tayadda tun sa'ar da ta ƙulla alaƙar zumunta da kano, ba'a taɓa samun wata rundunar mayaƙa data shigo Kano daga yamma don kawo hari ba, domin tun kafin isowarta Ƙaraye zata tarbeta tare da tabbatar da cewar tayi nasara akanta. Wannan shine asalin kiran ƙaraye da suna 'ƙyauren yamma da birni'.
   Tsoffin garuruwan yammacin kano da sukayi tarayya da ƙaraye a tsawon zamunna da suka shuɗe sune Baɗari, Goɗiya, Yalwan ɗan ziyal da kuma shanono, sai kuma Getso, da Ƙwanyawa, da Gwarzo daga baya, da wasu makamantansu.
Waɗannan garuruwa na fsrko suna da tambura da ake ƙaɗawa sarakunansu, wanda ke nuna bunƙasar sarautarsu da kuma haɓakar garueuwan nasu.
   Garin Ƙwanyawa na can yamma da Ƙaraye, kuma ya haɓaka ta yadda har akwai ganuwa kewaye dashi . An samu cewa awancan zamanin, dukkan garuruwan dake kewayen, basu da wurin fakewa idan an kawo harin yaƙi sama da Ƙwanyawa ko Ƙaraye. Da zarar sun shige birni aka ɓame ƙofa tofa sunsha, sai dai kaga sadaukai na hawa saman ganuwa suna harbo kibbau ga abokan gaba.
   Wata rawa gagaruma da ƙaraye ta taka itace lokacin yaƙin Jihadin fulani don tsarkake addinin musulunci a kano. A wannan zamani, ƙaraye ta fafata da dakarun masu jihadi aƙalla sau uku, kuma ta samu nasara akansu sau biyu.
Kashi na farko shine a lokacin da masu jihadi suka yaƙi Goɗiya, sai suka gangaro yamma da nufin barin ƙasar kano izuwa ƙasar Ghana.
   Karo na biyu kuwa shine a lokacin da masu jihadi suka dawo kano, sai suka riski dakaru sun haɗu ana saurarensu a ƙaraye, suka fafata dasu amma basu samu nasara ba.
    Sai da taimakon Allah masu jihadi suka karya lagon ƙaraye gami da ƙwace garin a karo na ƙarshe da suka buga.
   Ance a zamanin Sarkin Kano Sulaimanu ne aka ɗaga darajar Shugabancin ƙaraye izuwa darajar Sarki, saboda kasancewar wanda aka naɗa ya shugabanceta mai suna Mallam Adamu Kwasanlo, bafulani ne basulluɓe, wanda ya taka rawa a yaƙin jihadi. Don haka akace masa darajar sarautarsa ta sarki ce, yadda a gaba ba zaizo ya shiga sahun masu neman sarautar kano ba.
A yanzu haka, karaye ƙaramar hukuma ce a jihar kano. Kuma har yau sarkin yanka gareta, amma dai yana a matsayin Hakimi ne na mai martaba Sarkin Kano.
(Kaɗan daga tarihin ƙaraye kenan. Mai son jin ƙsri sai ya nemi littafin 'Ƙaraye Maƙarar Maganar Kano').

TARIHIN BIRNIN RANO

 TARIHIN BIRNIN RANO

Daga Sadiq Tukur Gwarzo
08060869978

Saɓanin abinda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya kawo a littafinsa 'Tarihin Kano kafin Jihadi' cewa asalin garin Rano daga wani mai suna Ranau ne da yazo ƙasar Hausa daga ƙasar Habasha tare da ƴanuwansa Maguzawa masu suna Gayya da Dala tun kafin haihuwar Annabi Isa A.S, bayani daga Rano ya kawo wata mahangar wadda ta saɓawa haka.
        A littafin da Maigirma Barayan Kano Hakimin Bunkure Tafida Abubakar Ila ya wallafa mai suna Tarihin Rano, ya kawo cewa ƙabilar Kwararrafawa da suka zo daga Kwararrafa ta cikin ƙasar Riruwai sune asalin kafa Rano.
   A cewarsa waɗannan ƙabila mafarauta ne, kuma wasu daga cikinsu ne suka baro garinsu tare da riskar yankin da Rano take ayau, suka ganshi cike da albarkatu da tsaunika, don haka sai suka yanke shawarar zama akan duwatsun suna noma da kiwo.
     Basaraken ya faɗa cewar Asalin sunan Rano yazo ne daga wani sarkin Rano mai suna Ranau, wanda wata rana aka kawo yaƙi ƙasar sa har kuma aka hallaka shi a wajen yaƙi, aka binne shi a gefen wani dutse mai suna Tajika.
   Yace kasancewar akwai ƙorama da mutane ke zuwa domin samo ruwan sha, sai mutane ke cewa mun tafi gurin Rauno ɗebo ruwa, daga baya aka koma kiran yankin da suna Rano.
     Waɗannan Kwararrafawa sun jima suna mulkin Rano a tsakaninsu, sun zauna da fadojinsu akan waɗannan manyan tsaunika na Rano misalin Dutsen Damishi, dutsen Kurgun da dutsen Mairama, kuma har yanzu akwai sawun wanzuwarsu a wurare mabanbanta, misalin wasu mashigai da sawun gine-ginen duwatsu da koguna masu duhu da aka samu wsɗanda akace mutanen sukan ɓoye acikinsu idan an kawo musu hari, waɗanda kuna zuwa yanzu sai jarumin gaske ne kaɗai zai iya cusa kansa ciki, daga baya sai Hausawan Haɓe suka zo suka ƙwace mulkin yankin baki ɗaya.
Dangane da sarkin farko a zuriyar Haɓe daya fara mulkin Rano, kusan dukkanin maruwaita sun haɗu akan cewa Autan Bawo, ƙani ga Sarkin Kano Bagauda, kuma jikan Bayajidda shine ya soma mulkin Rano. Sai dai akwai saɓani akan ainihin sunansa da kuma dalilin zuwansa Rano.
Barayan Kano ya faɗa a littafinsa cewar Zamna Kogo shine sunan Sarkin Rano na farko da Haɓe suka ɗora. Kuma ya nuna kamar yaƙi ne Haɓe suka kawo Rano har suka cita da yaƙi gami da ɗora nasu a mulki a wajajen shekara ta 1082 miladiyya.
 Amma Maje Ahmad Gwangwazo ya tafi akan cewa Hamza Zimango ne sunan wannan sarki, kuma shi ƙani ne ga Bagauda sarkin Kano na farko.
 A cewarsa Zimango yazo ne daga Daura da iyalansa, ya sauka a wurin yayansa Bagauda, har kuma yayan nasa ya labarta masa dabarun da yabi ya zamo sarkin Kano, watau ta hanyar Jarumtarsa da kuma alƙalanci na adalci daya rinƙa yi tsakanin mutanen Kano, sai shima Zimango ya tashi daga Kano yayi kudu, har ya riski Rano, anan ya zauna tare da maguzawan yankin, har kuma daga baya suka naɗa shi sarkin su.
Don haka, Rano ta shahara da mayaƙa gami da ɗaukaka gagaruma a zamanin baya, kuma ko a lokacin Jihadi, itace ƙasa ta ƙarshe da Fulani suka ci da yaƙi a zamanin Sarkin Kano Sulaimanu, lokacin da Sarki Alwali ya gudu daga Kano sai ya zauna a Rano sannan ya tafi Zariya, bayan shekara ɗaya ya baro Zariya ya sauka a Rano, ya wuce burum burum, kafin daga bisani rundunar mayaƙan fulani ta kawo musu yaƙi wanda yayi sanadiyyar mutuwar shi kansa Sarki Alwalin da kuma Sarkin Rano Jatau na lokacin. Suka naɗa sarki Dikko bafulani na farko a tarihi..

Thursday, 5 July 2018

TARIHIN TSOHON BIRNI AUYO

Tarihin Tsohon birni 'auyo'.
                                       Daga
Sadiq Tukur Gwarzo
Da
 Gaddafi Hussain Auyo



  Garin Auyo tsohon gari ne, domin kuwa tarihi ya bayyana mana  cewa Auyo na ɗaya daga cikin tsoffin birane kuma mashahurai a wannan kasa waɗanda sukayi sharafi har kuma ya zamo suna cin gashin kansu tun tsawon zamani daya gabata.
  Haka Kuma birnin Auyo ya jima yana ɗauke da tsarin masarauta wadda sarakuna ke tafiyarwa cikin ka'idoji gami da lura.
    Dangane da daɗewar Auyo, tarihi ya bayyana mana cewa ko lokacin da fir'auna Remesis II na zamanin Annabi Musa (A.S) yayi yekuwa tare da gangami daga manyan birane yana mai neman waɗanda suka kware akan sihiri da surkulle, a wannan karawar da tarihi ya ruwaito Firaunan yayi da Annabi Musa A.S, an samu cewa tabbas akwai matune a Auyo, har kuma wasu shahararru akan sihiri daga kasar Auyo sun halarci wancan taron tare  kuma da jarraba tsibbace-tsibbacen su a wurin, amma daga bisani da Annabin Allah Musa yayi galaba akan ɗaukacin Masihirtan, ance suna cikin waɗanda suka gaskata Annabi Musa (A.S) kuma sukayi masa mubayi'a.
    Har ila yau, akwai zance na gaskiya mai nuna cewar lokacin da tawagar wakilai daga  kasar Borno a zamanin wani Sarkinsu da ake kira 'Maidinama' suka tafi birnin Madina  domin su karɓo addinin musulunci a wajen Shugaba, Manzon Allah (s.a.w) har kuma suka tarar Manzon Allah yayi wafati sai Sayyadina Abubakar R.A ne ke Halifanci, har da mutanen Auyo acikin tawagar.
  A wancan lokacin ance shima Sayyidina Abubakar ɗin yana fama da yakuna, don haka yace su zauna kafin a samu natsuwa, har kuma Allah ya karɓi rayuwar sa. Amma da fara Halifancin Sayyidina Umar R.A sai ya taso da maganar, ya haɗo rundunar sahabbai da littattafai suka taho Borno..
 Kasar Auyo ta kasance mai  daɗaɗɗen tarihi, domin kuwa anyi imanin cewa duk wasu garuruwa da ake alakantawa da hausa bakwai ko banza bakwai, to kuwa Auyo ta girme su.. A ciki harda Daura, domin dai abisa kiyasi na bincike an gano cewa Auyo tafi shekara dubu biyar da kafuwa.
   Ance wani mutum mai suna 'Auya' shine ya kafa garin na Auyo, don haka daga sunan sane aka samo kalmar 'Auyo', kuma shi ɗan kabilar 'Bagirmine' waɗanda akace tun da jimawa suna zaune a arewaccin kasar Sudan.
       Kasar Auyo tana da mashahuran malamai masanan addinin musulunci. Tarihi ya bayyana mana cewa daga cikin malaman da sukayi fice a kasar kano akwai da yawansu waɗanda asalinsu Auyakawane.
  Garin Auyo yana ɗaya daga cikin garuruwan da anan baya-baya aka haɗe aka samar da masarautar Hadejia. Amma wannan gari sam ba koma baya bane acikin tarihin kasar Hadejia, kasancewarsa tsohon gari wanda ya daɗe da wanzuwa zamuna masu tsawo da suka shuɗe, gashi kuma sanan-nan gari daya tattara mutane masu baiwa iri daban-daban kama daga dakaru da baraden yaki zuwa uwa uba  malamai mahardata alqur'ani mai girma.
   Auyo ta jima ɗauke da masana masu ilimin taurari dana bugun kasa da masu lakkuna da sauran iliman asararu na tsaron kai da tsaron kasa, haka ma suna da mutane wadanda suka shahara  wajen sihiri da surkulle irin na wancan lokacin. Don haka muna iya cewa ita tunjimin gari ne wanda kome mutum yaje nema yana iya samu..
   

HIKAYAR WANI SARKIN HINDU DA ƊIYARSA HARIBAI

HIKAYAR ƊIYAR SARKIN DAULAR PITUGAR DAKE HINDU
SADIQ TUKUR GWARZO
A wani lokaci mai tsayi daya gabata a Hindu, anyi wani sarki a daular Pitugar mai jiji-da-kai. Sunansa Dheema.
  Sarkin yana da ƴaƴaye ƴammata guda biyu, dukkansu kyawawa ne. Ɗaya ta faye yawan surutu, gata da halin ko-in-kula, sunanta Kalimbai. Ɗayar kuwa sunan ta Haribai, kuma ita mai shiru-shiru ce da natsuwa.
   Da lokacin aurensu yayi, sai wani hamshaƙin attajiri ya fito neman auren babbar cikinsu watau Kalimbai, ai kuwa sarki ya bashi aurenta. Akayi gagarumin biki na ƙawa, duk gari kowa sai labari yake saboda kece raini da akayi a wannan biki.
  Bayan biki ya ƙare, sai Sarki Dheema ya lura da kaɗaicin da ɗiyarsa Haribai take fama dashi tun bayan auren yayarta Kalimbai, don haka sai yakan ware lokaci yana zuwa ɗakinta suna firar duniya da ita.
   Rannan sarki ya shiga ɗakin Haribai suna taɗi kamar yadda suka saba, sai idanuwansa yakai ga wani fai-fai a ɗakin mai ɗauke da rubutu kamar haka: "Duk gidan da mace mai hikima take a cikinsa, a koda yaushe zai rinƙa bunƙasa"
"Wanene ya sanar dake wannan zance?" Sarki Dheema ya faɗa yana mai nuni da rubutun dake jikin fai-fan.
 "Babu wanda ya sanar dani, amma da kaina nayi imani da hakan" Haribai ta bashi amsa.
 Sarki Dheema yayi murmushin yaƙe saboda yadda zuciyarsa ta sosu daga wannan magana.
Yace "kinga, ni Sarki ne, kuma kasancewata a gidan nan shine yasa komai da komai yake bunƙasa acikinsa. Don me zakice sai gida na ɗauke da mace mai hikima zai bunƙasa?"
  Haribai tace "Baba, magana ta fa haka take. Bunƙasar gidan nan ta dogara ne ga Hikimar mahaifiyar mu"
  Sarki ya fusata, ya daka mata tsawa yana muzurai, yace sam ba haka wannan zance yake ba. Amma Haribai ta dage kai-da-fata cewar hikimar mahaifiyarsu a wannan gida ne sanadin haɓaka da albarkar gidan baki ɗaya.
  A ƙarshe Sarki ya tashi ya fice daga ɗakin, yana tunanin hanyar da zai ladabtar da wannan ɗiya tasa, har ta gane cewa tayi laifi babba.
  Akan haka ya ƙudurce cewa shine zai lalubo mata ƙasƙantaccen mutum ya haɗata aure dashi.
  Cikin wannan mako Sarki Dheema ya lalubo wani mutum mai sana'ar saran itatuwa da faskarawa mai suna Nandu, yace masa "Kai Nandu! Zan aura maka ɗiyata Haribai"
  Nandu yace "Ranka ya daɗe ni talaka ne, sam-sam ba zan iya ɗaukar ɗawainiyar rayuwar jindaɗin da ɗiyarka zata iya buƙata daga gareni ba. Don haka bani iyawa".
  Sarki Dheema yace "aikuwa zaɓi biyu gareka, kodai ka auri Haribai ko kuma nasa a datse min kanka"
  Ba shiri Nandu yace ya yarda da wannan aure.
  Duk da irin dagewar da waziran Sarki gami da iyalansa sukayi akan hana wannan aure, amma ya kafe sai da akayi.
 Haribai kuwa bata taɓa ɗaga kanta akan lamarin ba.
 Akayi biki babu armashi, ta tafi tarewa a wani ruɓaɓɓen gida da mijinta Nandu ke rayuwa aciki nesa da gari.
  A kullum da garin Allah ya waye, Nandu zai ɗauki gatarinsa ya tafi daji sana'arsa ta saran itace. Acan ne zai wuni aiki, sai da marece  zai siyo kayan abinci da ɗan abinda ya samo, sannan ya kaɗo kansa gida abinsa, ita kuwa matarsa ta sarrafa abinda ya kawo ɗin zuwa abinci.
 Sai Haribai ta lura da cewa tana wuni bata aikin komai a gida har sai mijinta ya kawo kayan abinci da yamma take aiki. Don haka rannan sai ta shaida masa cewar "ina ganin, daga yau, ka rinƙa raba ƙuɗin da kake samowa zuwa gida uku, kashi biyu ka siyo mana abinci wanda zamuci sau biyu a rana, kashi ɗayan kuwa mu rinƙa tara shi, idan yayi yawa sai mu ƙaro sabon gatari.. Inaso na rinƙa binka daji aiki."
 Abinda ya faru kenan, babu jimawa kuɗin siyan gatari ya taru. Suka siya suna zuwa daji saro itace tare. Ya zamana ƙuɗin da suke samu a wannan aiki da wanda suke ajiyewa tari duk sun ƙaru.
 Jimawa kaɗan kuma sai Harimbai ta sake samun wata dabarar. Ta sanar da mijinta cewar ta lura da cewar maƙwabciyarsu nada dutsen tishi da ake niƙa alkama izuwa fulawa, don haka tana ganin ya kamata su siyo shi domin ƙara haɓaka hanyar samar da kuɗinsu.
 Nandu yayi murna matuka da haka, yace "duk yadda kikace haka za'ayi". Ya ɗauki kuɗin da suka tara ya nufi kasuwa. Bai dawo ba sai da ƙaramin dutsen tishi na dai-dai kuɗinsu.
  Sannu a hankali ya zamana suna iya samar da kuɗin da zasu iya warware matsalolin gabansu.
 Ita Haribai a iya niƙan data keyi tana samar da abinda zasuci a kullum. Don haka duk kuɗin da Nandu zai kawo gida ajiyewa kurum akeyi.
Daga baya sai Nandu ya ware fili a gidan, ya zamana a kullum itacen yake kawowa ya ajiye ba tare daya siyar ba.
 Rannan akayi sa'a, lokacin ana fama da muku-mukun sanyi, sai wani Sarki yazo shigewa ta wannan ƙasa da jama'ar sa.
Ya sauka a wani daji nesa da gari, sannan ya umarci barorinsa su bazama nemo itacen da za'a hura wuta don jin ɗumi.
 Koda isowar barorin cikin gari, sai sukayi kiciɓus da gidan Nandu mai ɗauke da tarin itace. Sai kuwa suka nuna buƙatuwarsu ga wannan itace. Nandu ya siyar dashi baki ɗaya garesu. Ai kuwa ya samu riba mai yawa daga wannan ciniki.
A wannan lokaci, Kar kaso kaga murna wurin Harimbai da Nandu.
Rannan kuma, Nandu yana saran itace, sai yazo kan wata bishiya mai kyau. Ganyayenta yala-yala, itacen jikinta kuwa sala-sala ne.
Daya komo gida sai yake nunawa matarsa kalar itacen daya samo a wannan ranar. Sai ta cika da murna, tace "Maigida, wannan ai itacen Sandal ne mai daraja. Aikuwa ya kamata ka ƙoƙarta samo irinsu da yawa ka girke a gidan nan".
Kasancewar Haribai daga gidan sarauta take, ta san darajar wannan itace. Domin sarakuna sunfi son ayi amfani dashi wajen ƙone gawarsu idan sun mutu ko kuma wajen shagalin bukuwan Havan da Pujan.
  Kashe gari Nandu ya tafi daji, ya lalubi wannan itaciya ta sandal tare da soma saran ressan ta a hankali ta yadda zata ƙara tohowa. Haka ya rinkayi a kullum, daga wannan zuwa waccan, har sai daya tara wannan itace da yawan gaske.
Akwai wata alƙarya a kusa da birnin Pitugar wadda aka wayi gari Sarkinta ya rasu. Kafin rasuwarsa kuwa attajirin gaske ne. Har kuma yayi wasicci da a ƙone gawarsa da itacen Sandal bayan rasuwarsa.
 Sai dai kuma akaf garin, an rasa wanda keda wadataccen itacen sandal da zai isa shagalin wannan biki. Akan haka ɗan sarki mai mutuwa ya bada cigiya zuwa maƙwabtan birane, har kuma akazo masa da labarin cewa akwai wani mai suna Nandu yana dashi.
  Sai yace aje wajensa a siyo masa itacen akan ko nawa ya yanka.
Barorin ɗan sarkin sukayi murna da suka tarar da cewa Nandu nada kalar itacen da uban gidansu keso kamar yadda labari yaje gareshi. Suka siyi itacensa da darajar gaske.
Daga nan fa Nandu da mai ɗakinsa suka fita daga kangin talauci. Tunda sun samu tarin dukiya.
 Nandu yasa aka gina musu ƙatan gida na sarauta mai cike da manyan zauruka, kai kace gidan sarkin garin ne.
Bayan tsawon lokaci da auren Nandu da Haribai, sai mahaifinta Sarki Dheema ya cika da tausayin ƴartasa, har ya soma da-na-sanin hukuncin daya ɗauka akanta.
Rannan sai ya yanke shawarar ya kai ziyara a garesu duka domin ganin halin da suke ciki.
Bayan ya gama shirya kyaututtukan dazai kai musu, sai ya tashi tare da da barorinsa, kai tsaye ya nufi gidan babbar ɗiyarsa Kalimbai. Yana ɗokin ganinta, a zuciyarsa yana rayawa cewar tabbas tana cikin farin ciki.
 "Ɗiya ta Kamli, yaya kike?" Sarki Dheema ya faɗa yayin haɗuwar su da Kalimbai.
Kalimbai ta rugo da murna, ta gaishe da mahaifinta. Sannan ta gabatar masa da ƴaƴayenta waɗanda tace ƙiriniya tayi musu yawa, ko makaranta ma basa zuwa.
Sarki Dheema ya kaɗu da yadda yaga wannan gida duk a hargitse. Ga yara duk babu natsuwa. Sannan Barori biyu ne kaɗai suka rage a gidan, yayin da a farkon aurensu gidan cike yake da masu hidimta musu. Tabbas da alamu karayar arziƙi ta gitta a wannan gida.
Ai kuwa da Sarki ya zanta da ɗiyar tasa sai ya gane cewar itace silar durƙushewar maigidan nata, domin kullum cikin buƙatar kashe kuɗaɗe take, ta gaza sauya rayuwa daga wadda ta saba a gidan sarauta zuwa gidan aure data samu kanta.
Ran Sarki Dheema a ɓace ya fito gidan, yace gida zai koma domin shawarta abinyi.
Yana isa kuma sai akazo masa da katin gayyata, akace masa wani attajiri ne yayi sabon gida yake gayyatarsa bikin tarewa domin neman albarkarsa.
Da sarki ya isa gidan, sai yake ta mamakin girma da kasaitar sa. Mai gidan ya fito ya tarbeshi. Sarki yayi mamakin yadda wannan baƙon attajiri yazo garinsa ya bunƙasa ba tare da saninsa ba.
Ana haka sai ga ƴarsa Hambai ta fito cikin kayan ƙawa, tana ɗauke da murmushi a fuskarta, tana mai marhaba lale ga mahaifinta.
  "Sannu da zuwa mai martaba mahaifina".
Sarki Dheema ya cika da mamaki, "ɗiya ta, gidan kine wannan!!!?"
Ta amsa masa da cewa "kwarrai kuwa"
"Tayaya haka ta faru?" inji Sarki Dheema.
 Hambai tace "Ranka ya daɗe, ka tuna da abinda ka taɓa karantawa a ɗaki na?.." Daga nan cikin ladabi ta zayyana masa duk hanyoyin da suka bi har rayuwarsu ta zamo haka.
Sarki Dheema ya gyaɗa kansa sama cikin mamaki. Ya raya a zuciyarsa cewa hakika ƴarsa tayi gaskiya.. Duk gidan dake ɗauke da Mace mai hikima, wannan gida sai ya bunƙasa.."








 

 
  

Sunday, 10 June 2018

KOKAWA: TASIRI DA TARIHI

KOKAWA: TARIHI DA TASIRI

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO

  Kokawa ba kurum wasa bane, al'ada ce da mutum yayo gado shekara da shekaru.
   Wani masani Kendall Blanchard ya kalli kokawa a matsayin daɗaɗɗen wasa acikin abinda ya rubuta a littafinsa mai suna 'The Anthropology of sports: An Introduction' saboda duba da yadda yace mutanen farko sun rinka zana hotunan masu kokawa a jikin kogunan duwatsu da kuma tarin mutane suna kewaye dasu suna kallo.
   Amma dai mafi yawan masana kimiyyar salsalar ɗan adam suna kallon kokawa a matsayin daɗaɗɗen abu wadda ake amfani da ita wajen gane jarumi a tsakanin mazaje ba kurum a matsayin wasa ba.
   Zuwa yanzu, yana da wuya a iya faɗar inda aka soma kokawa, ko kuma waɗanda suka soma yinta. Amma dai, idan muka kalli abin ta fuskar addinai, muna iya hasashen cewa 'ya'yayen Annabi Adamu watau Habila da Kabila ne suka soma karawa a junansu bisa saɓanin fahimta daya shiga tsakaninsu. Har daga bisani ɗaya ya kashe ɗaya.
   Yazo a rubututtukan masana kimiyyar salsalar ɗan adam cewa jinsin maza sunfi rashin-ji da rashin son zaman lafiya sama da jinsin mata, don haka a kusan kafatanin tarihi sune sukafi kara kokawa a tsakaninsu ba mata ba. 
   Wasu masanan kimiyya mata da miji masu suna Martin Daly da Margo Wilson ne suka samar da sunan 'Young Male Syndrome' domin nuna yadda matasa mazaje ke jin karfi a jikkunan su gami da saurin aukawa cikin yanayin gogayya ko karawa a tsakaninsu, ta yadda abubuwa irinsu kokawa kan shigo ciki domin kece raini.
  Ma'ana, da akai alamun cewa tun asali, mutum ya soma kokawa ne ba domin wasa ba, sai dai  bisa dalilai guda biyu:-
  Na ɗaya shine Kece raini.
  Na biyu kuwa shine samun daraja ko ganima.
   Masanin halayyar ɗan adam Aaron Lukaszewski, yayi wani bincike game da dalilan dake sa mutane ke yawan faɗa a Junansu, inda a karshe ya karkare da cewa mafi yawan karfafan mazaje sukanso kece raini a tsakaninsu, don haka akwai yiwuwar kartai biyu majiya karfi su kaure da kokawa bisa karamin dalili a  zahiri, amma a baɗini suna yin kokawar ne domin kece raini. Saɓanin jinsin mata daya lura da cewa karfafan cikinsu sunfi kawaici da hakuri, yayin da raunanan mata keda yawan son tsokana da tada fitina gami da amfani da hakora don tserar da kansu idan aka samu ɓacin rana.
  Dangane da yin kokawa bisa rajin samun tagomashi kuwa, akwai kyakkyawan hasashen cewa mutanen da suka gabace mu sun sanya kokawa ne a matsayin hanyar gane wanda yafi wani jarumta, ta yadda duk wanda ya samu galaba kuma shine zai iya samun babbar tagomashi akan ɗanuwansa.
   Yazo a tarihi yadda dakarun tsohuwar daular Girka data Misra ke shiga kokawa don auna kakkarfa da jurau a tsakaninsu. Haka kuma a daular katsina ta kasar Hausa, an samu cewar a wani lokaci ana iya zamowa sarkin wannan daula ne kaɗai ta hanyar kokawa.
   Wani masanin kimiyyar tarihin ɗan adam mai suna Napoleon Chagnon yayi bincike kan wata kabilar daji da aka samo mai suna 'Yanomamo' wadda ke zaune a kasar Venezuela.
  Suffofin waɗannan mutane da ayyukansu kusan irin na mutanen farko ne waɗanda akace sun fara rayuwa ne a afirka kimanin shekaru sama da dubu hamsin baya. Don haka ana iya cewa har zuwa yau kabilar Yanomamo na rike da al'adu ne kwatankwacin irin na mutanen farko da suke rufe tsiraicinsu da ganyaye.
   A binciken na Napoleon, ya lura da cewa kabilar suna kiran jarumin cikinsu da suna 'Unokai', sunan dake cike da girmamawa ga mutumin da yake da karfin kare kabilarsa daga makiya.
  Unokai yana zamowa mai yawan mataye, da yawan 'ya'yaye. Don haka burin kowanne namiji dake wannan kabilar shine ya zama kamarsa.
  Wannan ke zama silar da yara tun suna kanana suke koyan kokawa, domin na farko su kece raini ga sa'anninsu, sannan na biyu idan girma yazo musu su samu lakabin Unokai tayadda zasu samu tarin girma acikin jama'arsu gami da mataye da 'ya'yaye.
   Wannan shine babban tarihin da zamu rinka tunawa a koda yausjlhe idan muka kalli kokawa.
  Na farko dai mu gane cewar asalinta an sanyatane domin auna wanda yafi wani jarumta a tsakanin mazaje.
  Daga baya kuma sai aka rinka sanya darajoji akanta gami da mayar da ita gasa tayadda duk masu son mallakar girma, sarauta, mataye da 'ya'yaye da sauran abubuwan duniya masu daraja sai ace su shiga kokawa domin nema, wanda yayi rinjaye shine da nasara.
  Sabo haka kokawa tsohuwar al'ada ce wadda mutum yayo gadonta shekaru da yawa da suka gabata. Shiyasa ake samunta cikin kusan kowacce kabila.
   Abu na karshe shine, tsarin kokawa yana nan bai sauya ba.  Domin har zuwa yau anfi yin kokawa ne a tsakanin mutane biyu domin samun wani abu mai amfani, kuma a tsakiyar tulin mutane masu shaidarwa.
  Sai dai kurum akwai wayewa da tayi tasiri acikinta tayadda ake sanya alkali mai lura da lokaci gami da yanke hukunci, da sanya yashi ko kasa ta musamman a wurin yin kokawa, sai kuma samar da abin kiɗa domin karfafa guiwa gami annushuwa tsakanin masu kokawa da masu kallonsu.
  

Tuesday, 15 May 2018

TARIHIN SARKI MOULAY ISMAIL SHARIF

TARIHIN SARKIN MOROCCO, MOULAY RASHID ISMA'IL.


Daga Sadiq Tukur Gwarzo, RN.
        08060869978
   An haifi Moulay Ismail Rashid a wajajen shekarar 1646 a birnin Fez na kasar Morocco. Ya gaji mulkin Morocco ne tun yana da shekaru 26 a duniya bayan da ɗan uwansa mai mulki ya faɗo daga kan doki ya mutu.
   A wancan lokacin Moulay Ismail ya samu daular Moroco rarrauna saboda yawaitar faɗace-faɗace tsakanin kabilu gami da rikicin sarauta da yayi tsamari a daular. Baya da haka ma, birnin Marrakesh yayi bore ga shugabancinsa, inda mutanen garin suka shiga biyayya ga ɗan amminsa mai suna Ahmad ibn Muhriz.
    Don haka da fara mulkinsa, sai ya jagoranci runduna zuwa Marrakesh dake kudancin birninsa, ya faɗawa garin da yaki har kuma yaci nasarar kwace ikonsa, amma sai shugaban boren Ahmad bn Muhriz ya tsere ba tare da an kame shi ba.
   Sarki Moulay Ismail na ɗaya daga cikin sarakuna masu karfin iko waɗanda duniya ba zata taɓa mancewa da sunansu ba.
 Da fari dai, ya ɗauke cibiyar daularsa daga birnin Fez zuwa Meknes, sannan ya umarci a kawata ganuwar birnin da kawunan sojojin abokan hamayya guda dubu goma.
  Ance akalla a kusan shekaru hamsin dayayi yana mulki, ya kashe mutane sama da dubu talatin waɗanda yawancinsu barorinsa ne, ɓata masa rai sukayi kurum, ko kuma ace lalacinsu ne ya isheshi sai yasa a kashe su.
  Wasu kuma ya sanya a kashe sune saboda ayyukansu bai gamsar dashi ba. Domin ance shi makarancin littafin alkurani mai girma ne, kuma indai yana bisa doki, yana umartar barori su bishi ɗauke da alkurani a buɗe yana mai karantawa, amma fa da zarar sun aikata abinda ya sosa masa rai sai ya sare kawunansu.
 Sarki Moulay Ismail ibn Sharif ya shahara wajen gwabza yakuna da makwabtansa, sannan ya ciri tuta wajen kawata babban birninsa, domin shine sarkin daya umarci ayi gine-gine masu kayatarwa a birnin Meknes, misalin makarantu, masallatai, lambuna da wuraren hutawa da kuma ganuwa ga wannan birni.
  Haka kuma yayi gagarumin faɗa da daular Ottoman wadda cibiyarta ke kasar Turkiyya, anan ne har ya samu nasarar 'yantar da kasar Morocco daga karkashin wannn daula.
  A shekarar 1981 Sarki Moulay Ismail ya gwabza yaki da turawan Kasar Spain tare da karɓe ikon birnin 'La Mamora' mai ɗauke da tashar teku, inda ya sauyawa birnin suna izuwa al Mahdiya.
  A lokacin wannan yaki, wakilin sarkin mai suna Kaid Omar ya faɗawa Sifaniyawan cewa idan suka mika wuya ba zasu bautar dasu ba, wanda hakan ya karfafa musu guiwar dakatar da gwabza yaki bisa tsammanin samun adalci, amma bayan anci nasara, sai Sarkin yaga cewa sam ba zai iya barin sifaniyawa sama da dubu biyu masu ɗauke da kyawawan mataye da kayayyaki masu daraja ba sasakai, sai kawai ya bada umarnin a taso keyarsu zuwa birnin Meknes a matsayin ganimar yaki.
 A shekarar 1684 Moulay Ismail ya kwace ikon birnin Tangier wanda a lokacin turawan Portugal ke iko dashi, haka kuma a shekarar 1689 ya sake karɓe ikon wani babban birni mai suna Larache daga hannun turawan sifaniya.
  Bunkasar wannan sarki takai yadda sai daya tara rundunar mayaka bakaken fata mai ɗauke da akalla soji dubu goma sha biyar, dasu ya haɗa da nashi wajen yaki ta yadda sai daya karɓe ikon ɗaukacin kasar Morocco daga hannun turawa idan aka ɗauke yankunan Ceuta da Melilla.
  Akwai labaru masu nuna gwagwarmayar daya buga da faransawa, tunda ance ya kame wasunsu masu zuwa leken asiri kasarsa tare da mayar dasu bayi, amma wasu na ganin kasancewar a lokacin sarkin Faransa Louis na 14 yana kiyayya da Sipaniyawa, ance akwai zumunta maikyau a tsakaninsa da Sarkin na Meknes.
  An kuma ruwaito cewa Sarki Moulay Ismail na Morocco ya taɓa aikewa da jakada mai suna Muhammad Temimin domin nema masa auren gimbiyar Faransa  mai suna Marie Anne de Bourbon amma sai taki amincewa, sai dai duk da haka alaka mai kyau taci gaba da ɗorewa a tsakaninsu.
   A iya tsawon rayuwar Sarki Moulay Ismaïl, ance ya haifi 'ya'yaye guda 867, maza guda 525 da mataye 342. Ance baya da mataye guda huɗu da yake dasu, akalla yana da kuyangi guda 2,000, kuma an ƙlisssafta cewar a kalla a tsawon shekaru tamanin da yayi a raye, a shekarunsa sama da hamsin bisa karagar mulki akullum yana jima'i sau biyu, ko kuma da mataye guda biyu.
 Don haka sunansa ya shiga tarihi a matsayin wanda yafi kowanne namiji yawan haihuwa anan duniya a iya abinda ya fito ga sanin masana zuwa yau.
  Bayan rasuwar Moulay Ismaïl a shekarar 1727, rikici ya kara ɓarkewa tsakanin 'ya'yansa bisa wanda zai gajeshi a mulki, daga karshe wani ɗansa Muhammad yayi galaba, tare da ɗorawa akan gine-ginen da mahaifinsa ya soma. Sai dai girgizar kasar data auku a birnin Meknes  cikin shekarar  1755 ce ta lahanta kusan ɗaukacin waɗannan gine-gine, daga karshe tilas Sarki Muhammad ya ɗauke cibiyar birnin daga nan inda ya maida ita zuwa birnin Marrakesh.


Macen da tarihi ya kiyaye a matsayin wadda tafi kowacce yawan haihuwa itace Mrs Vassillev  ta birnin Moscow, wadda ta rayu tsakanin shekarun 1725 - 1765.  Ance tayi nakuda sau 27,  sau 16 tana haihuwar tagwaye, ta haifi 'yan uku sau bakwai, ta haifi 'yan huɗu sau huɗu. Jimilla ta haifi 'ya'yaye 69 reras.. (Kimiyya ta tabbatar da haka)

Tuesday, 1 May 2018

TARIHIN KABILAR BABUR DAYADDA DABIUNSU NA AURE SUKE

BABUR MARRIAGE CULTURE AND RITUALS

TARIHIN KABILAR BABUR DA AL'ADUNTA NA AURATAYYA

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO, RN

Kabilar Babur tana danganta asalinta ne da Mutanen Yamen, don haka aka ruwaito cewa rundunar wasu mutane ne sukaƴi hijira daga Yemen a wajajen shekara ta 600 miladiyya suka riski Kasar Sudan, sannan suka shigo cikin sahara tare da sauka a yankin da Kabilar Babur ke rayuwa a yanzu cikin kasar Borno.
   Ba iya kabilar Babur ba, har kabilun Kanuri da Luguda da wasunsu dake rayuwa a wannan yankin suna ikirarin asalin kakanninsu daga Yemen suke. Gusawar zamani ne kurum ya sanya takamaimen tarihinsu ya sauya.
   Zuwa yanzu dai, ana samun kabilar Babur ne a Jihohin Borno da Adamawa.
  A jihar Borno, akwai kabilar Babur a garuruwan Biu, Hawul, Kwaya kusar, Shani, Kwajaffa, Sakwa, Marama, Shaffa, Wandali, Kida, Miringa, Buratai, Zuwa, Yimirshika ,Hyera ,Dayar, Fumwa, Azare, Gwaski, Diragina, Yimana, Gwallam, Tiraku, Shindiffu, Goski, Pela Birni, Wangdang, Bula tawewe, Kogu Tashan Alade, Kida, da hang shang  da kuma Bayo, amma a jihar Adamawa kabilar Babur sunfi yawa a garin Garkida cikin karamar hukumar Gombi.
  Dukkan waɗannan garuruwa da Kabilar Babur ke zaune ciki nada nasu tarihin.
  Misali, ance jarumin daya kafa daular mulki ta Biyu mai suna Yamta, ɗane ga wata mace 'yar kabilar Mandara.
  Wai Tun tana da cikinsa aka ɗauke ta zuwa gidan Sarkin Borno, don haka acan aka haifeshi kuma acan ya taso da tarbiyar kanuri.
  Amma da Yamta ya girma, sai ya tumbatsa wajen jarumta. Shine fa harbya karɓe ikon yankin da Biu take ayau tare da kafa masarauta.
   Ana ganin ya fara kafa mazaunin masarautar sane a wani wuri mai suna 'Limbur' tsakanin chikorkur da Mandagarau. Har zuwa yanzu kuma ance kabarinsa yana nan a Limbur ɗin.
  Kabilar Babur, sune keda rinjaye a garin Biu da wasu garuruwan makwabta, amma akwai kuma kabilar Bura wadda ke zaune a makwabciyar kasar Babur ɗin, mai suna 'Babur Bura'. Dukkansu kusan da yare ɗaya suke amfani, kuma yaren yana da kamanceceniya dana garuruwan Chibok, Marghi, Higgi , Kilba and Bazza.
 Anfi samun kabilar 'Babur Bura' a jihohin gabashin Nigeria, watau Borno, Adamawa, Gombe da Yobe.
  AL'ADUN AURE
Mafi yawan kabilun Borno musamman Kanuri, Shuwa Arab da Babur nada kamanceceniya wajen al'adun auratayya. Watakila hakan ya faru ne saboda jimawar kabilun wajen zaman tare ko kuma ana iya cewa kakanninsu ne ɗaya, don haka daga garesu sukayo gadon ɗabi'un.
  Bisa al'ada ta Kabilar Babir, Idan namiji yaga mace yana so, to bazai sanar mata ba, sai dai ya nemeta da abota.
  A wannan abotar ne zai rinka bincikar halayyarta dana magabatanta, ba tare da ta sani ba, daga bisani kuma sai ya samu wani dattijo a danginsa ya ɗora masa alhakin kammala masa bincike akan yarinyar da zuriyarta duka.
  Daga wannan matakin kuma sai mai neman auren ya zaɓi maza uku da mata biyu akalla, daga danginsa su rakashi gidan su yarinya.
   Anan ne zasu haɗu da iyayenta ko 'yanuwanta, har kuma a tambayeta abinda ke tsakaninsu da wannan mai neman auren nata, da kuma muradinta akansa da sauransu.
  Idan an aminta a kulla auratayya, to daga nan ne za'a sanya ranar yin Baye, suna kiranta 'Yuyma'.
  Idan ranar tazo, dangi zasu haɗu daga ɓangaren namiji da mace maza da mata a gabatar da kayan ci dana sha, sanna a sanya ranar aure, watau “Mbwa Nyika”.
  Dangane da batun kuɗin aure ko sadaki, namiji na iya bayar da dukkan abinda ya samu gareshi ga iyayen wadda yake so ya aura, sukuma zasu ciri wani abu kaɗan su mayar masa da ragowar, (wasu ma ance basa cirar kome), to amma za'a gabatar masa da sunayen wasu abubuwa da akeso ya siya mata.
  A hakan ma, ba dole bane ya siyi dukkan komai ba, kawai dai yana iya zaɓar abinda yake da iko ne ya siya.
  Idan namiji ya haɗa kayan, sai ya tashi yan uwansa su tafi sukai gidan su yarinya. Daga nan kuma za'a saurarar ranar ɗaura aure.
  Daura aure kuwa ya danganta da addinin da mutum yakebi, kasancewar addini yayi tasiri cikin kabilar Babur, don haka kiristocin cikinsu sukanje chochi ne domin ɗaura aure, yayin da musulman cikinsu kan ɗaura aure a Masallatai ko gidaje, tare da aiwatar da al'adun aure kalar wanda musulunci ya halatta