SHIRIN GASKIYA DACI GARETA na biyu
LABARIN SARKI SIBANA DA GIMBIYARSA SULBANIYA
Tare da Sadiq Tukur Gwarzo
Da yake Allah shine mai yadda yaso a lokacin da yaso, a dare daya Sibana ya zamo sarki mai cikakken iko kuma qasaitacce. Shikuma azzalumin sarki ya zamo mazaunin gidan Jarun. Abinka da mai Ilimi, sarautar Sarki Sibana sai ta sauya. Ya kawo tsare-tsare masu kyau na adalci, ya haramta cin hanci da almundahna, ya kuma yi umarni da rage dumbin harajin da talakawa ke biya don sauqaqewa gare su. Wannan yasa nan da nan ya samu farin jini. Lungu da saqo sai waqoqi ake raira masa na yabo, gami da zambo ga tsohon sarki.
A daren farko da Sarki sibana ya shiga dakin amarya gimbiya subaniya, sai yake ganin abubuwan kamar a mafarki. Shi kansa yana mamakin wannan juyi da Allah yayi masa. Dakin nata an qawata shi da ado na alatu, ga fitilu masu kyawun gaske reras. Kamshi kuwa sai tashi yake yi, ga sautin wasu yammata kuyangi masu rera waqoqi yana tashi kadan-kadan, yabonsa kurum sukeyi tare da amaryasa, nan fa wani farin ciki ya qara cika masa zuciya, tuni ya fara mancewa da wahalar duniya, domin a yanzu jinsa yakeyi kamar tunda aka halicce shi shine Sarkin duniya.
Duk inda yasanya kafarsa, laushi yakeji kamar zai nutse. Ya hangota zaune bisa wata darduma, tana sanye da jajayen kaya masu ado da zinare, walwali da sheqi kawai takeyi.
Gimbiya Sulbaniya ta yaye mayafin daya rufe mata fuska, gami da dago kanta sama kadan. Ta dubi Sarki sibana, shima ya kalle ta, sannan ta duqar da kanta qasa tana mai cewa " Marhaban dakai Sarki daya tamkar da dubu,
sarkin da adalcinsa zai game duniya, sunan sa zai ratsa samaniya,
izzar sa zata wanzu har qarshen duniya,
An halicce ni don zamowa baiwa a gareka.
Maraba dakai haske maganin duhu.
Ina da buqata a gurin ka ya kai jarumin maza.."
( #SadiqTukurGwarzo )
Sarki sibana ya zura mata ido. Ganinta yake kamar aljana. Kyawun ta ya wuce a misalta, kallon kwayar idanunta kadai ya isa ya mantar da mutum wahalhalun duniya. Haka ma kallon daukacin fuskar tata . Kalmominta sun dauke shi daga wannan duniyar. A halin yanzu jinsa yake kamar anyi masa hisabi yana cikin aljanna. Sarki sibana ya nisa daga yanayin da yake ciki, dakyar ya samu kansa. Sannan yace "nayi miki alqari kome kike nema agurina zan miki matuqar ina iyawa"
Daga nan gimbiya sulbaniya ta fara bashi labarin ta kamar haka. "Ya kai wannan sarki mafi karimci daga sarakunan duniya, kayi sani cewa Sunana sulbaniya, mahaifina sarki Rama shike sarautar masarautar Ramayana dake kasar hindu. Ya kasance yana da fada aji, da karfin mulki. A yanzu haka ma, mutanen kasarmu na ganinsa kamar wani mahalicci, tunda har bauta masa akeyi. A lokacin da mahaifiyata ta dauki cikina, sai aka nemeta aka rasa. Nan fa hankalin mahaifina ya tashi. Da yake shima masanin tsafi ne, sai ya dugunzuma a cikin tsatuben sa, har saida ya gano inda take.
Ashe wani hatsabibin boka ne mai suna sundusur ya dauketa izuwa wani tsibiri mai suna Laaka, waje ne da ake kallo a matsayin mafi hatsari a duniya. Dalilinsa nayin hakan kuwa shine, yayi bincike a fagen tsafinsa sai yaga cewa za'a haifeni, zan kuma zamo mace kyakkyawa mai annuri, sannan kuma wani sirri zai kasance dani cewa dukkakan wanda ya aure ni, matuqar yana faranta min rai, babu wani abu dazai tunkara ba tare da yayi galaba akansa ba. Ya fahimci tauraruwa ta kakkarfa ce, hadimai na kuma suna da matuqar tasiri anan duniya.
Wannan lamari ya tayar da hankalin mahaifina matuqa gaya. Har ya rasa sukuni. Duniya tayi masa kunchi. Ya rasa menene mafita. Ana haka sai ya tara hakimansa da sarakunan yaqinsa, ya nemi shawararsu abisa zuwa tsibirin laakha domin dauko matarsa. A haqiqa, kasancewar kowannen su yasan hatsarin dake kunshe cikin wannan tafiya, babu wanda ya goyi bayan sa. Har mutane na ganin bai kamata ace akan rai guda daya tilo ba ayi asarar rayuka marasa adadi.
Daga nanfa kunchi ya qara tasarwa mahaifina. Kullum cikin hawaye yake da bege, kawai sai wata basira ta fado masa. Yace aransa, tunda ina da karfi a tasirin tsafi, kuma ta hanyar tsafi aka sace matata, to kuwa tilas nabi ta hanyar siddabaru na kwato ta, koda kuwa hakan zaisa nayi asarar rayuwa tane ma baki daya. Daga nan ya kira wazirinsa ya mallaka masa jiran gari, sannan ya nufi daji abinsa.
(#SadiqTukurGwarzo)
Koda isar sa kungurmin daji, sai ya sami kan wani dutse ya hau, ya zauna yana mai harde kafafuwansa, ya janyo wani kuben tsafi qarami irin na yaqi, ya fara busawa. Ai kuwa nan take dabbobin daji suka fara amsa kira. A wannan lokaci, namun daji kala-kala sun samu halarta, birai da karnukan dawa sune manya 'yan gaba dai-gaba dai. Bayan runduna ta hadu, kawai sai ya nausa cikin daji yayin da sukuma dabbobi suke biye dashi. Duk inda suka ratsa sai dai kaga bishiyoyi na zubewa aqas, qura na turnuqewa sama, iska kuma qaqqarfa na kadawa. A haka har suka isa wawakeken ramin da za'a tsallake a isa tsibirin Laakha.
Shi daman wannan tsibiri, ana kallon cewa babu mutum ko dabba dake rayuwa acikin sa, sai dai gagarumai kuma hatsabiban maridan aljannu. Don haka ne Boka sundusur ya zabi ya gina gidansa anan, saboda yasan babu mai iya kai masa chaffa. Dadin dadawa, tsibirin yana kewaye ne da wani wawakeken rami, babu wanda yasan zurfin sa, kuma wuta ce ke fitowa daga qasan sa izuwa sama. Saboda haka ya zamo cewar koda tsuntsaye basa kai kawo a saman ramin, domin babu zato wutar ke fitowa, duk kuwa abinda ta samu ko ta shafa, take zaka ganshi yayi qurmus.
Mahaifina ya zurawa wannan rami ido yana nazari akan hanyar qetare shi. Daga bisani dai sai yayi shawarar cewa gada zai hada ta tsafi wadda zata rinqa tafiya a saman ramin har taje daya gavar, kuma zata rinqa gociya da zamiya ga wannan wuta. Wannan shine kadai mafita. Nan take ya umarci dabbobi dasu karyo itatuwa.
Haka kuwa akayi, yasa aka daddatsa wasu, aka nemo ganyayen da ake igiyoyi dasu, dashi da birrai suka shiga aikin gada. Sai da suka gama tsaf, sannan suka hau kanta suna mai fuskan tar ramin. Gada ta tashi sama, ta fara tafiya sannu a hankali akan wannan rami.
Basu jima da fara tafiya ba sai ga wani katafaren tsuntsu, ashe shima aman wutar yake yi, nan take suka fara gumurzu. Tsuntsu na kwararo wuta daga sama, rami na watso tashi daga qasa, ita kuma gadar tsafi nata faman zuzzullewa. Idan ta zulle, shashin wuta ya shafi wasu daga dabbobin nan sai dai kawai aga sun kama ci da wuta, kafin a jima sun zama toka. Wannan abu yayi matuqar dagawa magaifina rai. Har saida yayi nadamar fitowar sa, sai ma da ya gamsu cewa tilas rayuwar sa zata salwanta a saman ramin nan, sannan akayi sa'a wuta ta fito ta qasa, shikuma tsuntsun nan na sama yayo qasa-qasa gami da saito gadar da nufin qone gadar baki daya qurmus, kawai sai gadar da waske, ai kuwa nan take wutar ta chafki tsuntsun. Yayi wata qara gagaruma, kafin ajima ya qone qurmus.
(#SadiqTukurGwarzo)
Wannan yasa suka sami raguwar bala'in da suke ciki. Amma kuma saukar su kan tsibirin keda wuya wani sabon bala'in ya dawo. Domin irin wadannan tsuntsayen n sunfi dubu ke dakon su. Da hango saukar su kuwa sai suka tashi sama, suka shiga aman wuta babu qaqqautawa. Nan fa rundunar mahaifina ta tarwatse, gashi basu da wasu makamai na mayar da martani, dole dabbobi suka shiga gudun neman mafaka, wasu suka nufi qarqashin duwatsu, wasu kuma suka koma da baya kan gada.
Da dai mahaifina ya rasa abinyi, sai shima ya quduri niyyar jarraba irin nashi tsafin, amma ga mamakinsa, duk abinda ya qudurci yi sai yaqi yiwuwa, sai da dabarunsa suka qare qar-qaf, yayi gudu kamar zai halaka wajen tsira daga sharrin tsuntsayen nan, wasu dabbobin kuwa duk sun qone, sai da suka dawo 'yan qalilan. Kwatsam sai mahaifina yayi wata shawara. Yaga cewa tunda tsuntsayen nan wuta suke fesowa, to bari shima ya koma wutar, wataqila zai kubuta daga sharrin su. Ai kuwa sai kawai ya rikide izuwa curin wuta, sannan ya nufi kofar shiga fadar da gudu.
Nan fa tsuntsayen nan suka ce dawa aka gama mu ba da kai ba? Suka tashi haiqan akansa, wuta kurum suke fesowa, shi dai bai canza siffa ba a haka har ya shiga fadar boka sundusur, duk inda ya wuce sai dai kaga wuta naci ganga-ganga a fadar, suma kuma tsuntsayen suka himmatu a mayar da wuta, kafin jimawa sai ga sassan fadar yana ci da wuta.
***
Darussan mu na wannan lokaci sune:
1. Kayi imani da Allah a kowanne lokaci, kada kuma duniya ta rudeka. Allah na iya canza duniyar ka akoda yaushe.
2. Shugabanci yana da wuya. Dole sai ka rinqa bin maslahar al'umma. Kada don kana shugaba ka dora buqatar ka fiye data mabiyanka.
3. A kowanne lokaci ka fadawa kanka gaskiya. Duk lamarin da zaka shiga, ka lura da wahalhalunsa, kada ka bari dadi ko bakin ciki ya rudeka kayi abin ba tare da kasan rikicin da zai iya aukuwa ba.
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
LABARIN SARKI SIBANA DA GIMBIYARSA SULBANIYA
Tare da Sadiq Tukur Gwarzo
Da yake Allah shine mai yadda yaso a lokacin da yaso, a dare daya Sibana ya zamo sarki mai cikakken iko kuma qasaitacce. Shikuma azzalumin sarki ya zamo mazaunin gidan Jarun. Abinka da mai Ilimi, sarautar Sarki Sibana sai ta sauya. Ya kawo tsare-tsare masu kyau na adalci, ya haramta cin hanci da almundahna, ya kuma yi umarni da rage dumbin harajin da talakawa ke biya don sauqaqewa gare su. Wannan yasa nan da nan ya samu farin jini. Lungu da saqo sai waqoqi ake raira masa na yabo, gami da zambo ga tsohon sarki.
A daren farko da Sarki sibana ya shiga dakin amarya gimbiya subaniya, sai yake ganin abubuwan kamar a mafarki. Shi kansa yana mamakin wannan juyi da Allah yayi masa. Dakin nata an qawata shi da ado na alatu, ga fitilu masu kyawun gaske reras. Kamshi kuwa sai tashi yake yi, ga sautin wasu yammata kuyangi masu rera waqoqi yana tashi kadan-kadan, yabonsa kurum sukeyi tare da amaryasa, nan fa wani farin ciki ya qara cika masa zuciya, tuni ya fara mancewa da wahalar duniya, domin a yanzu jinsa yakeyi kamar tunda aka halicce shi shine Sarkin duniya.
Duk inda yasanya kafarsa, laushi yakeji kamar zai nutse. Ya hangota zaune bisa wata darduma, tana sanye da jajayen kaya masu ado da zinare, walwali da sheqi kawai takeyi.
Gimbiya Sulbaniya ta yaye mayafin daya rufe mata fuska, gami da dago kanta sama kadan. Ta dubi Sarki sibana, shima ya kalle ta, sannan ta duqar da kanta qasa tana mai cewa " Marhaban dakai Sarki daya tamkar da dubu,
sarkin da adalcinsa zai game duniya, sunan sa zai ratsa samaniya,
izzar sa zata wanzu har qarshen duniya,
An halicce ni don zamowa baiwa a gareka.
Maraba dakai haske maganin duhu.
Ina da buqata a gurin ka ya kai jarumin maza.."
( #SadiqTukurGwarzo )
Sarki sibana ya zura mata ido. Ganinta yake kamar aljana. Kyawun ta ya wuce a misalta, kallon kwayar idanunta kadai ya isa ya mantar da mutum wahalhalun duniya. Haka ma kallon daukacin fuskar tata . Kalmominta sun dauke shi daga wannan duniyar. A halin yanzu jinsa yake kamar anyi masa hisabi yana cikin aljanna. Sarki sibana ya nisa daga yanayin da yake ciki, dakyar ya samu kansa. Sannan yace "nayi miki alqari kome kike nema agurina zan miki matuqar ina iyawa"
Daga nan gimbiya sulbaniya ta fara bashi labarin ta kamar haka. "Ya kai wannan sarki mafi karimci daga sarakunan duniya, kayi sani cewa Sunana sulbaniya, mahaifina sarki Rama shike sarautar masarautar Ramayana dake kasar hindu. Ya kasance yana da fada aji, da karfin mulki. A yanzu haka ma, mutanen kasarmu na ganinsa kamar wani mahalicci, tunda har bauta masa akeyi. A lokacin da mahaifiyata ta dauki cikina, sai aka nemeta aka rasa. Nan fa hankalin mahaifina ya tashi. Da yake shima masanin tsafi ne, sai ya dugunzuma a cikin tsatuben sa, har saida ya gano inda take.
Ashe wani hatsabibin boka ne mai suna sundusur ya dauketa izuwa wani tsibiri mai suna Laaka, waje ne da ake kallo a matsayin mafi hatsari a duniya. Dalilinsa nayin hakan kuwa shine, yayi bincike a fagen tsafinsa sai yaga cewa za'a haifeni, zan kuma zamo mace kyakkyawa mai annuri, sannan kuma wani sirri zai kasance dani cewa dukkakan wanda ya aure ni, matuqar yana faranta min rai, babu wani abu dazai tunkara ba tare da yayi galaba akansa ba. Ya fahimci tauraruwa ta kakkarfa ce, hadimai na kuma suna da matuqar tasiri anan duniya.
Wannan lamari ya tayar da hankalin mahaifina matuqa gaya. Har ya rasa sukuni. Duniya tayi masa kunchi. Ya rasa menene mafita. Ana haka sai ya tara hakimansa da sarakunan yaqinsa, ya nemi shawararsu abisa zuwa tsibirin laakha domin dauko matarsa. A haqiqa, kasancewar kowannen su yasan hatsarin dake kunshe cikin wannan tafiya, babu wanda ya goyi bayan sa. Har mutane na ganin bai kamata ace akan rai guda daya tilo ba ayi asarar rayuka marasa adadi.
Daga nanfa kunchi ya qara tasarwa mahaifina. Kullum cikin hawaye yake da bege, kawai sai wata basira ta fado masa. Yace aransa, tunda ina da karfi a tasirin tsafi, kuma ta hanyar tsafi aka sace matata, to kuwa tilas nabi ta hanyar siddabaru na kwato ta, koda kuwa hakan zaisa nayi asarar rayuwa tane ma baki daya. Daga nan ya kira wazirinsa ya mallaka masa jiran gari, sannan ya nufi daji abinsa.
(#SadiqTukurGwarzo)
Koda isar sa kungurmin daji, sai ya sami kan wani dutse ya hau, ya zauna yana mai harde kafafuwansa, ya janyo wani kuben tsafi qarami irin na yaqi, ya fara busawa. Ai kuwa nan take dabbobin daji suka fara amsa kira. A wannan lokaci, namun daji kala-kala sun samu halarta, birai da karnukan dawa sune manya 'yan gaba dai-gaba dai. Bayan runduna ta hadu, kawai sai ya nausa cikin daji yayin da sukuma dabbobi suke biye dashi. Duk inda suka ratsa sai dai kaga bishiyoyi na zubewa aqas, qura na turnuqewa sama, iska kuma qaqqarfa na kadawa. A haka har suka isa wawakeken ramin da za'a tsallake a isa tsibirin Laakha.
Shi daman wannan tsibiri, ana kallon cewa babu mutum ko dabba dake rayuwa acikin sa, sai dai gagarumai kuma hatsabiban maridan aljannu. Don haka ne Boka sundusur ya zabi ya gina gidansa anan, saboda yasan babu mai iya kai masa chaffa. Dadin dadawa, tsibirin yana kewaye ne da wani wawakeken rami, babu wanda yasan zurfin sa, kuma wuta ce ke fitowa daga qasan sa izuwa sama. Saboda haka ya zamo cewar koda tsuntsaye basa kai kawo a saman ramin, domin babu zato wutar ke fitowa, duk kuwa abinda ta samu ko ta shafa, take zaka ganshi yayi qurmus.
Mahaifina ya zurawa wannan rami ido yana nazari akan hanyar qetare shi. Daga bisani dai sai yayi shawarar cewa gada zai hada ta tsafi wadda zata rinqa tafiya a saman ramin har taje daya gavar, kuma zata rinqa gociya da zamiya ga wannan wuta. Wannan shine kadai mafita. Nan take ya umarci dabbobi dasu karyo itatuwa.
Haka kuwa akayi, yasa aka daddatsa wasu, aka nemo ganyayen da ake igiyoyi dasu, dashi da birrai suka shiga aikin gada. Sai da suka gama tsaf, sannan suka hau kanta suna mai fuskan tar ramin. Gada ta tashi sama, ta fara tafiya sannu a hankali akan wannan rami.
Basu jima da fara tafiya ba sai ga wani katafaren tsuntsu, ashe shima aman wutar yake yi, nan take suka fara gumurzu. Tsuntsu na kwararo wuta daga sama, rami na watso tashi daga qasa, ita kuma gadar tsafi nata faman zuzzullewa. Idan ta zulle, shashin wuta ya shafi wasu daga dabbobin nan sai dai kawai aga sun kama ci da wuta, kafin a jima sun zama toka. Wannan abu yayi matuqar dagawa magaifina rai. Har saida yayi nadamar fitowar sa, sai ma da ya gamsu cewa tilas rayuwar sa zata salwanta a saman ramin nan, sannan akayi sa'a wuta ta fito ta qasa, shikuma tsuntsun nan na sama yayo qasa-qasa gami da saito gadar da nufin qone gadar baki daya qurmus, kawai sai gadar da waske, ai kuwa nan take wutar ta chafki tsuntsun. Yayi wata qara gagaruma, kafin ajima ya qone qurmus.
(#SadiqTukurGwarzo)
Wannan yasa suka sami raguwar bala'in da suke ciki. Amma kuma saukar su kan tsibirin keda wuya wani sabon bala'in ya dawo. Domin irin wadannan tsuntsayen n sunfi dubu ke dakon su. Da hango saukar su kuwa sai suka tashi sama, suka shiga aman wuta babu qaqqautawa. Nan fa rundunar mahaifina ta tarwatse, gashi basu da wasu makamai na mayar da martani, dole dabbobi suka shiga gudun neman mafaka, wasu suka nufi qarqashin duwatsu, wasu kuma suka koma da baya kan gada.
Da dai mahaifina ya rasa abinyi, sai shima ya quduri niyyar jarraba irin nashi tsafin, amma ga mamakinsa, duk abinda ya qudurci yi sai yaqi yiwuwa, sai da dabarunsa suka qare qar-qaf, yayi gudu kamar zai halaka wajen tsira daga sharrin tsuntsayen nan, wasu dabbobin kuwa duk sun qone, sai da suka dawo 'yan qalilan. Kwatsam sai mahaifina yayi wata shawara. Yaga cewa tunda tsuntsayen nan wuta suke fesowa, to bari shima ya koma wutar, wataqila zai kubuta daga sharrin su. Ai kuwa sai kawai ya rikide izuwa curin wuta, sannan ya nufi kofar shiga fadar da gudu.
Nan fa tsuntsayen nan suka ce dawa aka gama mu ba da kai ba? Suka tashi haiqan akansa, wuta kurum suke fesowa, shi dai bai canza siffa ba a haka har ya shiga fadar boka sundusur, duk inda ya wuce sai dai kaga wuta naci ganga-ganga a fadar, suma kuma tsuntsayen suka himmatu a mayar da wuta, kafin jimawa sai ga sassan fadar yana ci da wuta.
***
Darussan mu na wannan lokaci sune:
1. Kayi imani da Allah a kowanne lokaci, kada kuma duniya ta rudeka. Allah na iya canza duniyar ka akoda yaushe.
2. Shugabanci yana da wuya. Dole sai ka rinqa bin maslahar al'umma. Kada don kana shugaba ka dora buqatar ka fiye data mabiyanka.
3. A kowanne lokaci ka fadawa kanka gaskiya. Duk lamarin da zaka shiga, ka lura da wahalhalunsa, kada ka bari dadi ko bakin ciki ya rudeka kayi abin ba tare da kasan rikicin da zai iya aukuwa ba.
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
No comments:
Post a Comment