Sunday, 23 September 2018

Tarihin Sarkin Kano Abbas

Sarkin Kano Muhammad Abbas

Sadiq Tukur Gwarzo
   Shine sarkin Kano na hamsin da ɗaya, kuma na takwas a jerin Sarakunan fulani da suka mulki Kano. Shi ɗa ne ga Marigayi Sarkin Kano Abdullahi Maje Karofi, watau ƙani yake ga Galadima Yusufu da kuma Sarki Alu Babba.
   Babu takamaimen lokacin da aka haifeshi kasancewar Hausawa basu cika kiyaye ranakun haihuwa ba a wancan lokacin, amma dai an samu cewar ya zama sarkin Kano a watan mayu na shekarar 1903 miladiyya har kuma zuwa shekarar 1919 bayan rasuwarsa aka binneshi a Nassarawa (daga nan ya samo sunan Maje Nassarawa) sai ɗansa Shehu Usmanu ya gajeshi.  Gwamna Lugard ne ya naɗa shi sarauta sa'ar da yaci kano da yaƙi.
  Ga yadda hawa mulkinsa ya kasance:
Kamar yadda aka sani, Mabiya Galadima Yusufu sunyi bore ga Sarki Tukur bayan rasuwar Sarki Muhammadu Bello, wanda ya kai ga yaƙin Basasar Kano. Daga bisani aka hallaka Sarki Tukur, Alu ƙani ga Galadima Yusufu wanda ya rasu a Garko tun kafin soma yaƙin, ya zamo Sarkin Kano. A wannan lokacin sai ya naɗa ƙaninsa Abbas muƙamin Wambai.
   Ana haka sai turawa suka zo kano, sarki Alu ya shirya tafiya Sokoto tare da tawagarsa tun kafin isowarsu, ciki kuwa harda wambai Abbas, inda ya danƙa amanar gari a hannun Sarkin Shanu.
   Bayan Sarki Alu ya juyo daga Sokoto, sai ya sauka a ƙasar zamfara, anan ne kuma mai ɗakinsa tazo da dare a sukwane ta sanar masa cewar turawa sun ƙwace iko da kano, wanda a cikin daren yayi hawa a ɓoye ya bar jama'arsa.
   Koda gari ya waye sai ragowar mutane suka shiga neman Sarki Alu, amma rasa shi da sukayi yasa suka yanke shawarar cigaba da tafiya zuwa kano. Inda a yankin kwatarshi wannan runduna ta haɗu da turawa masu neman Sarki Alu, waɗanda bayan sun karɓe ikon Kano suka nemeshi suka rasa, sai suka bar wasu turawan riƙon kano, suka biyo sahun Sarki Alu zuwa Sokoto.
    Waziri Amadu ne ke jagorancin wannan tawaga, anyi wannan haɗuwa ne kuma a wani daji da ake kira 'Dajin Rubin' (Tana kuma iya yiwuwa turawa ne suka sanyawa dajin wannan suna saboda mutuwar ɗanuwansu Reuben a dajin)
  Da gamuwar su sai faɗa ya kaure a tsakani. Aka soma fafatawa, dakarun waziri Amadu suka afkawa turawa da sara da suka, yayin da suma turawa suka mayarwa da dakarun martani da harbi.
   Sai dai cikin abinda baifi awa ɗaya ba, turawa suka karya lagon wannan tawaga suka kuma watsa ta. Ya zamana an kashe wasu, wasu kuma suna zube a kakkarye harsashi yayi misu lahani, yayin da saura suka shige daji da gudu suna masu neman tsira da rayukansu..
  Anan ne Wambai Abbas ya jagoranci wata tawaga suka gudu daga wannan yaƙin tare da nufowa birnin Kano.
  Sai dai tun kafin su iso, tuni har labari yazo ga turawan da suka rage a kano, waɗanda aka barsu a gari da zimmar su tsare garin tunda sun karɓe iko dashi.
   Ai kuwa tun kafin dakarun su iso, sai turawan suka haɗa tawaga suka nufi wajen ganuwa, suka jejjeru suna sauraren su.
   Bayan misalin awa guda suna jira, sai ga dakarun sun karaso.
   Turawan nan suka tsaida waɗannan dakaru, sannan suka karɓe dukkanin makaman dake jikkunan su.
  Daga nan aka basu damar shiga garin kano bisa sharaɗin kowa gidansa kurum zai nufa, banda kuma yinkurin tada tarzoma.
  Anyi haka a lokacin tsakiyar sanyi na wannan shekarar.
   Daga nan kuma, sai Turawa bayan sun koma gida suka shiga neman shawarwari daga gurin Larabawa mazauna kano akan wanda ya kamata a naɗa sarki a kano musamman wanda ya fito daga zuriyar Abdullahi Maje Karofi.
  Sai larabawan nan sukace ai kuwa Wambai Abbas ne yafi dacewa, tunda babban su waziri Amadu ya rasu.
  Sai turawa suka amsa da cewar haka nan ne.
 Sai dai fa duk da haka, turawa sun shiga tambayar Manyan kano na wancan lokacin dake zaune a birni, cewar wa ya dace ayiwa sarki, sai suma ɗin kuwa suka ce abaiwa Wambai Abbas sarauta.
  To kunji yadda sarki Abbas ya zama sarki na farko a kano a zamanin turawa. Shi suka ɗorawa nauyin kwantarwa da mutanen Kano hankali ma zamanin, sannan ya rinƙa kiran duj waɗanda sukayi hijira saboda zuwan turawa Kano su komo gida.
   A zamanin mulkinsa jirgin ƙasa ya soma zuwa kano, har wata rana turawa suka buƙaci yahau domin a ɗana shi.
   Ai kuwa Sarki Abbas yahau jirgi, mutanen Kano duk suka firgice dube da jin kuwwarsa, wadda basu taɓa jin irin taba.
  Labari ya nuna cewar har mutan kano sun fara zunɗen cewa turara ƙarya sukeyi, wayau kawai sukayi domin su tafi da Sarki Abbas su kashe, amma daga bisani sai Allah ya dawo dashi gida lafiya.
   Har ila yau, a zamanin sa ne aka tara ɗaukacin sarakunan Arewa a kano domin tarben wakilin Sarkin Ingila, shine ma har Sarkin Zazzau na zamanin Shehu ya rera shahararrar waƙar nan tasa mai taken 'Zuwan mu Birnin Kano'.
  A zamaninsa har ila yau aka gins makarantar Elemantare ta farko a kano, aka soma shirya gidan tarihi na Kano tare da wasu ayyuka masu yawa.
  Haƙiƙa Sarki Abbas yana da karamci da son jama'a, kuma yayi matuƙar ƙoƙarinsa wajen kare haƙƙin Kanawa daga turawa masu mulkin mallaka a zamaninsa duk kuwa da kasancewar umarninsu yake bi, sannan cigaba mai yawa ya riski kano a mulkinsa.
   Dafatan Allah ya rahamsheshi Amin

Thursday, 20 September 2018

YADDA AKE BIKIN SALLAH A ƘASAR HAUSA

YADDA AKE SHAGULGULAN SALLAH A ƘASAR HAUSA

Hausawa nacewa 'Sallah biki, ɗaya Rana'. Ma'ana, Sallah wani lokaci ne na biki duk da kasancewar Rana ɗaya akeyin Sallah ɗin.
Sallah ibada ce da addinin musulunci ya sunnata, wadda aduk shekara akeyi sau biyu, babba da ƙarama, to amma anan ƙasar Hausa ba ibadar ƙaɗai akeyi ba, ana haɗawa ma harda wasu lamurori na biki. Akwai abubuwa kala-kala da akeyinsu a lokacin wannan biki, wasunsu ma har mutane na ɗaukarsu a matsayin abubuwa na addini, alhali kuwa na al'ada ne. Wanda kuma hakan ke nuni da cewa irin shagalin bikin dake tattare da ranar Sallah tun da jimawa yske anan ƙasar Hausa.
Daga cikin abubuwan da akeyi don bikin sallah akwai:
1. Ɗinkin sabbin kayan Sallah
 Tun kafin ranar sallah zakaga mutane nayin tanajin sabbin kaya dasu da iyalansu wanda zasu sanya domin murnar zagayowar wannan lokacin biki da ibada mai albarka.
2. Tanajin Kayam miya
Sallah biki ce, a biki kuwa an sani anaci ana sha. Don haka tun kafin isowarta zakaga mutane na tanajin kayan abinci da nasha wanda za'ayi amfani dasu a lokacin wannan biki mai albarka.
3. Tanajin Rago a sallar layya
A lokacin gabatowar babbar sallah, kasuwanni na cika da dabbobi misalin rakuma, shanu da kuma raguna. Hakan nada nasaba da abinda yazo a koyarwar addinin islama na yanka rago ko dabba mai lafiya don yin hadaya da ake kira layya a lokacin wannan biki.
4. Zuwa idi ranar sallah
Idan ranar sallah tazo, maza da mata, yara da manya na sanya sabbin kaya, suci ado da komai sabbi gwargwadon sukunin da mutum yake dashi sannan a tafi bayan gari, zuwa wani fili da aka ware wanda ake kira masallacin idi. Anan ne ake sallatar sallah raka'o'i biyu mai ɗauke da kabbarori, watau faɗin 'Allahu Akbar Allahu Akbar' aƙalla guda goma sha biyu baki ɗaya. Idan an idar, sai kaga mutane sun cika da murna suna gaisawa da juna, daga nan sai liman yayi nasiha garesu sannan su dawo gida.
5. Abinci ranar sallah
Akwai abinci da ake girkawa a ranar babbar sallah, koda yake wasu basa yin girkin sai kashe gari.
Wannan abinci shine ake rarrabawa gida-gida na maƙwabta da ƴanuwa.
A lokacin da ake da sukuni a gari, a kusan kowanne gida anayin wannan girkin, suna kuma rarrabawa izuwa makwabta. Tayadda zakaga an tara abinci kala kala misalin funkasau, tuwo, waina, shinkafa da sauransu a mazubai.
6. Yanka rago
Ana dawowa daga sallar idin babbar sallah ake yanka ragon layya ko kuma duk dabbar da aka tanadar domin yin wannan hadaya da ita. Liman ne ke fara yanka nashi a masallacin idi. Daga nan kuma sai a shiga gyaran dabbar. Zuwa kashe garin sallah sai a shiga suya.
7. Ziyara Gidan ƴanuwa da abokan arzika
Ana ziyara zuwa gidajen ƴanuwa da abokan arziƙa a lokacin bikin sallah. Anan ne kuma ake bada goron sallah, koda yake yanzu an sauya abin, kusan kuɗi ake bayarwa yayin wannan ziyara.
Wanda yafi wani ƙarfi shine ke bayar da wannan kyauta. Don haka a wani lokacin, wanda yaje ziyara ke bayarwa, yayin da a wani juyin wanda aka zowa ne ke bayarwa.
8. Zuwa kallon Hawan sallah
Mazauna manyan birane dake nan ƙasar hausa suna zuwa gidan sarki domin kallon hawan sallah.
A kano, sarki nayin hawa bayan saukowa daga masallacin idi da ake kira 'Hawan daushe'. Daga baya kuma sai hawa masu suna hawan nasarawa, hawan ɗorayi, hawan fanisau su biyo baya.
9. Zuwa wuraren shagulgula
misalin gidan zoo
Yara da manya kanje wuraren da aka kawwame don yin shagalin sallah, inda akasari makaɗa da mawaka da masu barkwanci ke taruwa don nishaɗantar da al'umma.
  Misalin irin wannan wuri a kano shine gidan namun daji da akafi kira da gidan zoo. Inda yara da manya ke taruwa don kallon namun daji, wasu kuma ke zagayawa wurin kallon makaɗan kalangu da makaɗan zamani.

Sunday, 16 September 2018

TARIHIN ASALIN ZAMFARAWA, BIRNIN DUTSI DA LABARIN ƳAR GOJE

TARIHIN ASALIN ZAMFARAWA: LABARIN BIRNIN DUTSI DA GIMBIYA ƳARGOJE



Birnin Dutsi wanda a halin yanzu yake ƙarƙashin Masarautar Zurmi dake Jahar Zamfara,  nan ne akace Zamfarawa suka Fara yada zango, a lokacin da suka riski ƙasar Hausa daga wurin zaman su na asali dake Gabas ta tsakiya.
 Jagoran su, da ake kira Dakka ne ya fara Sarauta a wannan Gari na Dutci/Dutsi a wajajen Shekarar 1300 AD.
 Ance Waɗan nan Mutanen (Zamfarawan Farko ) masu tsayi ne da girman jiki  sosai , kusan wannan ne dalilin da ke sanyawa ana alaƙan ta su da Jinsin Samudawa.
Haka kuma Kaburburan su da ke Dutci /Dutsi a halin yanzu ma wani babban misali ne na irin girman Jikin nasu.
Bayan Mutuwar Sarki Dakka Wanda shine Mahaifin Sarauniya Argoje/Yargoje, an yi Sarakuna biyu kafin ta samu damar ɗarewa kan Karagar Mulki.
 Ance Ƴargoje tayi Mulki a tsakiyar ƙarni na 13 miladiyya.
 Kuma ta Shahara a lokacin ta , domin har a dajin Kuyambana da ke ƙasar Ɗansadau ta Jahar Zamfara ta yanzu takan Zauna da Majalisar ta , tana yanke hukunci akan lamurran da suka shafi al'ummar ta.
A Yanzu haka akwai wata fitilar ta da ke ajiye a ginin hukumar Adana Kayan Tarihi da al'adun Gargajiya na Jahar Zamfara wanda ake dangantawa da ita.
 Bayan Rasuwar ta a Dutci /Dutsi sai aka naɗa ƙanenta mai suna Bakurukuru a matsayin Sabon Sarki.
Sarki Bakurukuru ɗan Dakka ne ya ƙirƙiri Sabuwar Hedikwatar Zamfarawa,  Mai Suna Birnin Zamfara daga ƙarshe-ƙarshen ƙarni na 13 zuwa farko-farkon ƙarni na 14 , shune silar da zamfarawan suka tashi daga Dutci/Dutsi zuwa can Birnin Zamfaran, inda sunan Gonar Alkalin Zamfarawan ya amshe sunan Birnin na Zamfara.
A Wannan Wuri ne suka yi Mulki har lokacin da Gobirawa suka ƙwache Birnin daga hannun su a cikin ƙarni na 17.

Sunday, 9 September 2018

HIKAYA MAFI TSAYI A DUNIYA

HIKAYA MAFI TSAYI A DUNIYA.

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO

A wani zamani mai tsawo daya shuɗe, a daular larabawa, anyi wani hamshakin sarki mai ilimi da hikima.
  Wannan sarki yana da yawan neman ilimi, gami da yawan sauraron hikayoyi tun yana karami. Don haka ya zamana ya kiyaye mafi yawan hikayoyin da alummar zamaninsa ke labartawa mutane, har takai ga cewa da-zarar mai bada labari ya soma labarta masa wata hikaya, kafin yakai karshenta, wannan sarki zaice dakata, ai nasan wannan hikaya, ba itace karshen ta kaza da kaza ke faruwa ba?
  Da Sarkin yaga kamar ya kure masu bada hikayoyi na fadarsa, sai yasa akayi shela cewar yana so azo masa da hikaya mafi tsawo a duniya wadda zata bashi dariya, shikuma yasha alwashin zai bada gagarumar kyauta ga duk wanda yaci nasarar yin haka.
   Ai kuwa mai shela yabi kwararo-kwararo yana sanarwa, mutane kuma suka rinka ɗungomowa ga sarki, suna masu bada labarin hikayoyin da sukaji daga iyaye da kakanni, amma duk babu wanda yazo da wata hikaya wadda sarkin bai santaba, balle har yaji wani sabon abin dariya acikinta.
  Ana haka sai ga wani yaro karami ya karaso, yanaso akaishi gaban sarki domin yazo da dogon labarin dazai baiwa sarki, yana da tabbacin zai kayatar da sarki.
  Har Mutane sun soma hantararsa saboda ganin yaro neshi alhali ga manya sun gaza, amma dai sarki yace a iso dashi gabansa.
  Da yaro yai gaisuwa gaban sarki, sai ya fara bada labarinsa kamar haka:-
   Akwai wani mutum mai suna Mugambo, acici ne na hakika. Bai taɓa koshi ba a tarihin rayuwarsa. Duk tulin abinda ka bashi sai ya cinye, kuma bazai ce maka ya koshi ba. Har takai yakanyi shelar cewa wanene zai iya kosar dashi koda sau ɗaya ne a rayuwarsa?
 To Rannan dai sai sarkin garin mai Suna Sarfin, yace zaiyi maganin wannan acici, don haka a kawo shi gabansa zai ciyar dashi.
  Sarki yasa aka yi abinci daro-daro kala-kala sama da daro ɗari, aka kawo abinsha tulu-tulu, sannan aka zaunar da Mugambo, akace ga abinci, kayi taci har saika koshi
   Mugambo ya russuna gaban sarki cikin girmamawa, sannan yace Ranka ya daɗe, waɗannan duk nawa ne? Cikin farin ciki. Daga nan ya zauna dirshan kamar mai ɗaukar karatu, sannan ya soma cin abinci.
  Mugambo yayi taci, yayi taci, yayi taci, yayi taci, yayi taci.... Yaro mai bada hikaya yayi ta maimaita kalmomin yayi taci.. Yayi taci.. Yayi taci.. Tun daga safe har yamma.
  Sarki ya daka masa tsawa, yace kai yaro, wannan wanne irin labari ne haka sai maimaita abu ɗaya kakeyi?
  Yaro yace Ranka ya daɗe, daro sama da guda ɗari fa aka tara masa a gabansa, ga kuma abinsha duk a gabansa, a yanzu kuwa a labarin ko daro ɗaya bai kammala ci ba.
   Yaro yaci gaba da cewa da yaci yaci yaci, sai kuma yasha abinsha, yasha abinsha, ya kara shan abinsha, sannan ya cigaba da cin abinci.
  Yayi taci.. Yayi taci... Yayi taci.... Yayi taci....
  Sarki ya tuntsure da dariya, yace lallai wannan labari ne mafi tsawo dana taɓa ji.. Nasan zanuɓiya sgafe kwanaki ɗari an maimaita waɗannan kalmomi.. Kai fadawa ku kawowa wannan yaro kyaututtukansa ya tafi ya bamu wuri.
  Aka baiwa yaro tulin kyaututtuka, aka ɗora shi akan rakumi tare da kyaututtukan , sannan aka haɗa shi da bawa guda ya rakashi gida.
  Yaro ya zauna bisa rakuminsa cikin farin ciki, sannan ya cigaba da cewa Sai Mugambo yayi taci.. Yayi taci.. Yayi taci...
  Alummar wajen kuwa duk sai suka kwashe da sowa...

Sunday, 19 August 2018

KANO DAGA TSAUNIN DALA: WATA MAHANGA A TARIHIN HAUSA

KANO DAGA DUTSEN DALA: WATA MAHANGAR AKAN TARIHIN HAUSA DA HAUSAWA

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
  08060869978
Kano ta dabo tumbin giwa, mai Dala da Gwauron dutse.
  Wannan wani shahararren kirari ne da kowa ya sani ana yiwa Kano, ta yadda ake koɗa garin  tare da  jiɓantashi da manyan tsaunikan garin masu suna Dala da Gwauron dutse.
Akwai maganganun masana da dama game da tarihin waɗannan tsaunika, sai dai kuma wannan wani tarihi ne da muka samo daga bakunan mazauna yankin da waɗannan duwatsu suke a wata ziyara da mukayi zuwa yankin.
Mal Yahaya Madigawa, matashi mai bibiyar tarihi kuma marubuci, shine ya zagaya damu wuraren da muke da bukatar gani, ciki kuwa harda saman tsaunin Dala, inda tsawon lokuta ake bautar aljana tsumburbura akai.
  Da fari dai, wannan mahanga ta tafi akan cewa Dala, Gwauron dutse da kuma Fanisau kamar yadda aka sani ba duwatsu bane, tarin ƙasa ce da wata ƙabila ta taɓa tarawa tsawon shekaru da suka gabata.
Ance Marigayi Mal Mudi Speaking, da wasunsa na daga cikin masu irin wannan ra'ayin.
Ance sunan wannan ƙabila Dala, kuma dalilin tara ƙasar na da alaka da al'adarsu ta tulawa ƙabarin manyansu ƙasa kwatankwacin gine-ginen pyramid da aka samu a ƙasashen Misira da Sudan.
Don haka ake ganin sa'ar da shugaban ƙabilar Dala ya rasu sai aka binne shi a inda tsaunin Dala yake ayau, sannan mabiya ƙabilar suka bazama kurfa-kurfa tare da lalubo ƙasa suna tulawa a saman ƙabarin, shine kuma har saida wajen ya zama tsauni babba kamar dai yadda ake iya gani zuwa yanzu duk kuwa da kasancewar Ruwa ya zaizaye tsaunin sosai.
Shi kuma Gwauron dutse ance gawar matar Shugaban nasu ce, yayin da ake kallon tsaunin Fanisau a matsayin kushewar ɗansu.
Ance asalin waɗannan ƙabila mai suna Dala mazauna duwatsu ne, kuma a Magwan aka sansu da zama baki ɗayansu. Koda yake, wasu na hasashen daga habasha suka taso tun zamanin Nana Bilkisu da Annabi Sulaiman A.S, yayin da wasu ke kallon kasancewarsu a matsayin jikokin ƙabilun NOK da kimiyya ta tabbatar da fakuwar su a wuraren arewacin Nigeria shekaru kimanin dubu biyu da suka gabata.
Babban abu dai shine, lallai da akwai alamar alaƙa tsakanin waɗannan mutane da akace sun zauna a Magwan da kuma ƙabilun da suka zauna a Lupur, Sontolo, Kwatarkwashi da sauran tsoffin duwatsu dake wannan yanki waɗanda aka tabbatar da cewa mutanen baya sunyi rayuwa a samansu, musamman idan aka kalli yadda ɗaukacinsu suka rayu akan duwatsu.
Wani Masanin kimiyyar tantance adadin shekarun kayan tarihi mai suna Mallam Habib ya faɗa cewar sunbi diddigin tarin wannan ƙasar dake tsube a tsaunin Dala a wani ɗan ƙwarya-ƙwaryar bincike da suka gudanar, har kuma sun samu cewa tsaunin na ɗauke ne da tarin ƙasa mabanbanciya da aka ɗebo daga wasu sassan kano. Har yake ganin an ɗebo ƙasar ne a wasu yankunan da suke tsakanin birnin kano zuwa Gwarzo.
Sai mahangar tace gushewar wannan ƙabila data auku tsawon lokaci ne ya kawo zamanin ƙabilar Barbushe, waɗanda suka gaji tsaunin har kuma suka rinƙa bautar aljanna tsumburbura a saman sa.
Dangane da shaharar wannan tsauni a zamanin da, har zuwa yanzu mun lura akwai wasu mutane daga mazauna yankin tsaunin Dala masu iƙirarin cewa asalin tushen su ba anan yake ba, kawai dai farauta ce tayi silar  zuwan kakannin su gefen tsaunin a tsawon zamani daya gabata, har kuma daga baya mutanen suka yanke shawarar zama a wurin.
Asalin wajen ance daji ne mai ɗauke da albarkatu, amma daga baya sai aka soma  haƙar tama a jikin tsaunin, kasancewar an ɗebo ƙasashe masu ɗauke da ita tamar tsawon zamani daya gabata, sai kuma ta kasance tana girma kamar yadda marmara keyi.
 Haƙo tama ɗin ne kuma ya sake janyo hankulan mutane suka rinƙa zama a yankunan, suna sarrafa ta wajen yin ƙarafa, sannu a hankali wajen ya zama gari mai haɓaka.
A irin haka ne akace wani shehin malami ya ƙaraso wurin daga ƙasar Libya mai suna Fatahullahi, wanda akewa laƙabi da Abul Raas, amma hausawa ke kiransa da suna 'Bunsurun Dala' wai saboda tulin gemanyar dake fuskarsa wanda yasha ban-ban da al'adarsu ta wancan lokacin.
Shehi Fatahullah ya riska a lokacin ana musulunci a kano, amma kuma hawa tsaunin Dala don neman biyan buƙatu bai saki kanawa daga abinda suka gada na maguzanci ba, wanda hakan yasa ya ƙirƙiro da wata al'ada data ɗoru akan musulunci bisa burin sauya akalar mutanen daga maguzanci zuwa ɗorar da wani abu na addini, wanda yayi hasashen idan addini yayi ƙarfi za'a tureshi baki ɗaya a ɗora mutane akan addini zuryan. Wasu na ganin tun daga can aka sauya dalilin hawa tsaunin da wani abu makamancin bikin takutaha.
Ance marigayi Fatahullah ya riski Kano a lokacin tana ƙarƙashin daular Borno ne, shine yasa wasu ke ƙaryata zamansa a Kano dube da rubututtukan da almajiransa sukayi suna masu ambatar sunan Borno a matsayin inda ya koma da zama, don haka tana iya yiwuwa a zamanin sarkin Borno Mai Idris Alooma ne wanda ya rayu tsakanin ƙarni na goma sha uku zuwa na sha biyar.
Har yanzu kuma kabarinsa yana gefen tsaunin dala, zagaye acikin wani masallaci kawwamamme.
Game da asalin Hausawa, mun samu cewar akwai daga mazauna yankin da suke cewar Hausawa na asali wata ƙabila ce mai suna 'MANGU', kafin daga baya a rinƙa kiransu da suna 'Maguzawa', waɗanda akace sun taso ne daga wani yanki na Jos. Kuma akace har yanzu akwai ɓurɓushin su dake zaune acan....



Thursday, 9 August 2018

TARIHIN SARAKUNAN KANO A TAƘAICE

KASHI NA ƊAYA

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
         08060869978

Mazaunan Kano na Farko
Marigayi Alhaji Abubakar Dokaji ya faɗa a littafinsa mai suna 'Kano ta dabo cigari' cewar tun a ƙarni na tara waɗansu maharba da babu takamaimen inda suka fito suka zauna akan duwatsun dake sararin da ake kira Kano ayau, watau misalin dutsen Dala, Gwauron dutse, Magwan, da Fanisau.
  Sai dai, wasu na ganin faruwar hakan ya auku ne tun a wajajen ƙarni na bakwai
   Farauta shine mafi akasarin abinda waɗannan mutane suka fiyi, amma daga bisani suka soma taɓa noma.
Sarkin Kano na ɗaya: Bagauda.
Masu haɗa tarihin Kano dana Bayajidda, sunce yawaitar rashin zama lafiya daga mahara masu zuwa kamen bayi ne yasa mazauna kano suka rinƙa kai ƙorafi ga sarauniyar Daura Daurama. A lokacin Sarkin Daura Bawo kuwa sai ya turo ɗansa Bagauda Kano don yayi mulki.
  Akace Bagauda yayi zamani da wani bafaden Barbushe shugaban masu bautar tsunburbura mai suna Jankare, kuma daya ƙi bashi goyon baya sai yasa aka kama shi aka yanka.
  Bagauda ya iske alƙaryun Gazargawa, Zadawa, Fangon, Zaura, Dundunzuru, Shiriya, Sheme, Gande, Tokarawa, da wasunsu waɗanda ke zazzaune a sassan ƙasar kano irinsu Wasai, Sontolo, Barkum Watari, Jakara,  Shike, karmami, Ringim da wasunsu.
Bagauda ya sauka a Dinari ya shekara biyu, sannan ya koma Barka ya gina Talotawa, sannan ya koma Sheme inda ya tarar da waɗansu manyan matsafa waɗanda ya mallake su, misalin Galosami, Barmi, Gazawari, Dabgege, Fasataro da Bakin Bunu.
   Ance sa'ar da Bagauda zai baro Daura ya taho ne da mutanensa irinsu Kududdufi, Buram, Isa, Baba, Akasan, Darman, da Goriba.
  Sai dai, Maje Ahmad Gwangwazo ya ruwaito shigen haka a littafinsa 'Tarihin Kano kafin Jihaɗi littafi' na ɗaya, amma akwai saɓani a wasu wuraren, musamman dalilin zuwan Bagauda daga Daura da kuma hawan Sarautarsa.
   A nashi ɓangaren, yace Bagauda ɗan Bawo tun yana yaro yake jin labarin yadda yankin Kano ke haɓaka daga mahaifiyarsa Sarauniya, don haka daya girma sai ya kwashi abokansa ya sulale zuwa kano. Kuma sai daya shafe shekaru biyu yana koyon yaren Hausa, domin shi Bamange ne. Sannan yace mutanen kano da kansu suka ga dacewar ayi masa sarauta saboda halayensa na kirki wajen yiwa jama'a Hukunci da kuma jarumtakarsa.
 Waƙar Bagauda kuwa da Mal. Abdullahi Kabuga ya rera mai bayar da tarihin Kano, ta nuna cewar Kafin Bagauda yazo kano, anyi wata gagarumar yunwa a wannan yanki daya zama ƙasar Hausa ayau, don haka mutane suka rinƙa barin  garuruwansu suna tafiya neman abinci. A haka Bagauda yazo kano ya sauka a Maɗatai, kuma ya soma taɓa noma tare da ganin albarkarsa. Daga nan ya aika gida iyalansa, ƴanuwansa da abokansa suka taho gare shi. Daga cikinsu akwai irinsu Shehe, Gwale,
A wata mahangar kuma musamman wadda ta fito daga wasu Maguzawan Kano, sun faɗa cewar Bagauda Bamaguje ne Bahaushe, wanda ya riski Kano daga yamma. Kuma asali ya baro gida ne da ɗan Uwansa mai suna Bugau. Bagauda ya rabu da yayansa Bugau a garin Baɗari yazo wurin wani ɗan kabilarsa mai suna Goɗiya ya zauna, daga bisani ya wuce zuwa kano.
  Bagauda dai yayi shekaru 66 a mafi inganci yana mulkin kano, kuma a zamaninsa ance an samu matuƙar tsaro da zaman lafiya a kano, duk da wasu na ganin har ya mutu akwai ɓurɓushin mabiya Barbushe da basa yi masa biyayya.
Sarkin Kano na biyu: Warisi
Ance shi ɗa ne ga Bagauda, sunan Mahaifiyarsa Saju. Alhaji Ahmad Bahago ya kawo waɗannan sunaye a matsayin manyan fadawan Warisi a littafinsa Kano ta Dabo Tumbin Giwa: Galadima Mele, Barwa,Buram, Sarkin Gija Koramayi, Maidalla Zakar, Makama Gargi, Jarmai Goshin wuta, Jarmai Baƙoshi da waɗansu.
Ance ya shekara 33 kan karagar kano, a zamaninsa aka soma naɗa sarautar gado a kano, watsu ƴaƴayen abokan mahaifinsa suka rinƙa samun sarautar iyayensu bayan rasuwarsu kamsr yadda ta auku gareshi. Kuma an samu zaman lafiya a mulkinsa, saidai ba kamar zamanin Bagauda ba.
Sarkin Kano na uku: Gijimasu
Ance shi ɗane ga Warisi, sunan mahaifiyarsa Yanusa, ya zauna a Garazawa da mulki tsawon lokaci, sannan shine ya soma bada shawarar yiwa kano ganuwa don kangeta daga mahara.
   A zamanin nasa ne kuwa aka soma ginin ganuwa, ya haɗa kusan kafatanin mazauna kano aka soma aikin ginin ganuwa. Bayan an gama, sai akayi mata kofofi takwas. Ance shanu ɗari sarki ya yankawa ma'aikata a ranar farko ta soma wannan aiki. Wasu sunce ya kasance mai yawan kyauta don haka ya samu nasarar haɗa kan jama'ar Kano a zamanin sa.
 Akwai masu cewa ya gina fadarsa ne a Madabo, amma wasu sunce a Gwammaja yayi ta.
Sarakunan kano na huɗu: Nawata da Gawata
Ance su tagwaye ne sunyi mulki tsawon shekara ɗaya kuma a tare, idan yau ɗaya na bisa mulki, ɗayan zai kasance a gida sai kashegari yazo yahau karagar mulki.
  Kuma tagwayen masu da ake gani har yanzu a hannun Sarkin Kano nasu ne aka haɗe wuri ɗaya tsawon lokaci.

Tuesday, 7 August 2018

TARIHIN FANISAU

TARIHIN DAKE YANKIN 'TSAUNIN FANISAU'

Sadiq Tukur Gwarzo, RN.

Tarihin garin Fanisau na komawa ne shekaru sama da dubu kwatankwacin shekarun kafuwar Kano.
   Wani tsoho mai suna Usman Abdul'aziz Jikan wakilin Shawara, ya sanar mana da cewa tarihin Fanisau da  tarihin Kano abubuwa biyu ne da suke a matsayin ɗaya.
    Babu wanda ya san ainihin lokacin da mutane suka soma zama a gefan wannan tsauni na Fanisau tun kafin ma wurin ya zama gari kenan amma dai an gamsu da cewa kusan duk shigen al'adun da suka wakana akan dutsen Dala an samu kwatankwacinsu akan tsaunin Fanisau.
    Wani Bamaguje da ake kira Gwambari Jade ne ya fara dawowa saman tsaunin Fanisau da zama daga kano sama da shekaru dubu ɗaya da suka gabata, shikuwa ya kasance Waziri ne ga Barbushe a wajen bautar gunkin Tsumburbura dake saman dutsen Dala tun a zamanin Maguzanci.
     Ance da mazauna Dala, da Magwan, da Gwauron Dutse gami da Fanisau duk maguzawa ne masu ƙabila iri ɗaya. Sai dai sanin tushen su gami da yarensu zuwa yanzu yana da matuƙar wahala.
   Irin waɗancan mutane ne suka soma zama a kewayen tsaunin Fanisau tun wurin yana ƙurgurmin daji.
 Tana iya yiwuwa albarkar namun daji dake wurin da kuma neman tallafin Aljanar dake saman dutsen ce ta sanya mutane suka rinƙa komawa yankin da zama, sannu a hankali har ya zama gari.
   Tabbas, akwai wata aljana dake saman wannan tsauni na Fanisau wadda ake kira da suna 'Aljanar Kan Dutse', wadda akace ita ƙawa ce ga Aljanna Tsumburbura. Wadda kuma aka samu cewa asalin maguzawan da suka soma zama a wurin suna mu'amala da ita na tsawon lokaci.
Ance tun a wancan zamani, takan taimaki garin wajen samun nasarar duk wani yaƙi daya taso. Sannan da zarar an tura mayaƙan Fanisau yaƙi zuwa wani yanki, har kuma sukaci nasara, sai aji garin fanisau ya kaure da guɗa. Don haka tanan mutanen garin kan gane nasarar yaƙin mayaƙansu tun gabanin su komo gida.
 Sannan duk tawagar data nufo garin Fanisau da yaƙi zata ganshi yayi duhu, hayaƙi na tashi daga gare shi.
   Wata majiya tace wani bamaguje mai suna Nisau shi ne uban Gumbarjado mai gida bisa saunin fanisau. Daga sunan ne aka samo fanisau.
A tsawon zamani, garin Fanisau ya kasance kamar wata unguwa ce dake nesa da birnin kano wanda sai an shige wani surƙuƙin daji ake kaiwa gareshi. Ance sai a zamanin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa yasa aka zagaye garin da ganuwa, sannan aka fitar masa da kofofin shiga ta yadda da zarar yaƙi ya matso, sai mutanen dake zaune a kewayen garin su rugo su shige don meman mafaka.
Ance Sheikh Abdulƙadir Al Magili daya  riski Kano a wuraren ƙarni na goma sha biyar zamanin Mulkin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa ya sauka ne a Fanisau, sarki yana aika masa da abinci gami da sauran ababen buƙata. Amma daga baya aka tasoshi ya dawo Zauren Tudu, dake Ƙofar Wambai ta birnin Kano.
Asalin sunan Fanisau ya fito ne daga wani shahararren malami daya soma zama a garin bayan gushewar mulkin Maguzanci, ana kiransa da suna Mallam Nisau.
Shaharar Mallam Nisau ta sanya har daga wurare ake zuwa ɗaukar darasu wurinsa. Don haka mutane kan ce 'Na tafi Fan Nisau'. Har daga bisani ake kiran garin baki ɗaya da suna Fanisau.
Garin Fanisau na cike da Mayaƙa waɗanda suka taka matuƙar rawar gani wajen kare martabar Kano. Shiyasa ake ganin akwai kyakkyawar alaƙa mai tsawo tsakanin mazauna Fanisau da kuma mutanen birnin Kano, saboda tun tale-tale, duk yaƙin da Kano zata buga sai ta tafi da mayaƙan Fanisau.
Amma sai a zamanin mulkin Fulani aka soma yunƙurin ginawa garin babban Masallaci tare da gidan Sarki. Kuma ana ganin koda sheik Abdullahi Gwandu, ƙani ga Mujaddadi Usmanu ɗan Fodio yazo kano, sai daya riski Fanisau.
An sanar mana cewa Sarki Ibrahim Dabo ne ya soma wannan aiki na gina masallaci, sai kuma babban ɗansa daya gajeshi watau Sarki Usmanu ya Kammala.
Daga nan kuma aka soma yin hawan Fanisau, inda Sarki ke ware rana dashi da tawagarsa su tafi Fanisau, ya zauna a gidansa tsawon yini ɗaya sannan ya komo birni, al'adar da har zuwa yau ba'a daina yinta ba.
Akwai labarun fitattun mayaƙa da yawa da aka taɓa samu a garin Fanisau, misalin su Samagi, Sha'aike, Ɗan Toro, Bashar, da wani mai suna Sa'adu Kuzo ku duka..
Sa'adu kuzo ku duka shine wanda akace a zamaninsa saboda tsabar jarumtaka, duk yawan dakaru zai afka musu har kuma yayi galaba akansu. Don haka jama'a ke matuƙar tsoronsa har takai ko Dagacin garin baya iya shigewa ta gabansa face ya cire takalmi.
Sannan ance ko ɓarawo aka kamo daga wani gari za'a kai shi Kano don yin hukunci, sai an kawo ɓarawon gabansa ya buge shi sannan ayi gaba..