Wednesday, 4 August 2021

ADABIN ZUBE

 RUBUTUN ZUBE

  Rubutun zube wani jigo ne ma adabi wanda ya tattara mabanbantan abubuwa kama daga rubutattun labarai, hikayoyi, da sauran su.

  Mallam Yakubu Musa Muhammad ya rubuta a littafin sa 'Adabin Hausa' cewa "Zube; ya haɗar da tatsuniya, hikaya, maganganun azanci, azancin magana da sarrafa harshe.."

  Akan raba Adabin zube izuwa rubutattun Tatsuniya, Labarun Gargajiya, Barkwanci da Tarihi, ko kuma a rarraba shi gida uku izuwa Almara, Ƙissa da Hikaya.

*Azancin Magana na nufin wata magana da akeyi mai ma'ana saɓanin gundarin maganar, misalin karin magana (i.e, Kowanne Allazi..) , zambo (i.e, mai bakin zalɓe..), ba'a (i.e hassada bata hana samu), habaici (i.e, yaro bari murna karen ka ya kama zaki) da sauransu.

* Sarrafa harshe ya tattara zantukan azanci da hikima waɗanda ake amfani dasu wajen siffantawa, ƙawatawa, bayyanawa da sauran su.

* Ƙissa: maanar ta shine wani jinsin labari na gaskiya wanda babu sofanen ƙarya a cikinsa musamman wanda ya shafi addini. Missali, maimakon ace labarin Annabawa sai a kira shinda Ƴissoshin Annabawa.

*Almara: maanar sa shine, jinsin labari wanda yake shiryayye domin janyo hankulan mutane, a wasa musu ƙwaƙwalwa ta hanyar samar musu da wata gagarumar matsala a cikin labarin wadda take buƙatar nazari da tunani wajen warwareta.

*Hikaya: Maanar ta shine jinsin labari na gaskiya amma wanda aka yi masa ƙari da wasu abubuwa don ƙawatashi ko zuzutashi. A wani fannin kuma akan samu labarai na hikima da ake kira hikayoyi waɗanda suka ƙunshi dabbobi da tsuntsaye waɗanda ake bayar dasu domin koyawa alumma darasi.

Tatsuniya: Labarai ne ƙirƙirarru da ake bayarwa musamman ga yara domin koyar dasu halaye kyawawa da tunkuɗe su daga munanan halaye.

 

No comments:

Post a Comment