RUBUTUN ZUBE
Rubutun zube wani jigo ne ma adabi wanda ya tattara mabanbantan abubuwa kama daga rubutattun labarai, hikayoyi, da sauran su.
Mallam Yakubu Musa Muhammad ya rubuta a littafin sa 'Adabin Hausa' cewa "Zube; ya haɗar da tatsuniya, hikaya, maganganun azanci, azancin magana da sarrafa harshe.."
Akan raba Adabin zube izuwa rubutattun Tatsuniya, Labarun Gargajiya, Barkwanci da Tarihi, ko kuma a rarraba shi gida uku izuwa Almara, Ƙissa da Hikaya.
*Azancin Magana na nufin wata magana da akeyi mai ma'ana saɓanin gundarin maganar, misalin karin magana (i.e, Kowanne Allazi..) , zambo (i.e, mai bakin zalɓe..), ba'a (i.e hassada bata hana samu), habaici (i.e, yaro bari murna karen ka ya kama zaki) da sauransu.
* Sarrafa harshe ya tattara zantukan azanci da hikima waɗanda ake amfani dasu wajen siffantawa, ƙawatawa, bayyanawa da sauran su.
* Ƙissa: maanar ta shine wani jinsin labari na gaskiya wanda babu sofanen ƙarya a cikinsa musamman wanda ya shafi addini. Missali, maimakon ace labarin Annabawa sai a kira shinda Ƴissoshin Annabawa.
*Almara: maanar sa shine, jinsin labari wanda yake shiryayye domin janyo hankulan mutane, a wasa musu ƙwaƙwalwa ta hanyar samar musu da wata gagarumar matsala a cikin labarin wadda take buƙatar nazari da tunani wajen warwareta.
*Hikaya: Maanar ta shine jinsin labari na gaskiya amma wanda aka yi masa ƙari da wasu abubuwa don ƙawatashi ko zuzutashi. A wani fannin kuma akan samu labarai na hikima da ake kira hikayoyi waɗanda suka ƙunshi dabbobi da tsuntsaye waɗanda ake bayar dasu domin koyawa alumma darasi.
Tatsuniya: Labarai ne ƙirƙirarru da ake bayarwa musamman ga yara domin koyar dasu halaye kyawawa da tunkuɗe su daga munanan halaye.
No comments:
Post a Comment