Monday, 15 February 2021

01. ZUWAN TURAWA KANO: MAHAMGA TA 2

 Zuwan Turawa na Farko Kano


Tun zamanin Sarkin Kano Ibrahim Dabo Turawa suka fara zuwa Njeriya ta Arewa domin wasu dalilai kamar sayen bayi da neman dukiya da mulki.

   Turawa Sun somashigowa Nijeriya ta ruwa ne ruwa ta Libya suka biyo ta Katsina suka zarce har suka iso Kano. Su ma TuraWasun zo Wannan kasa ne

Kungiyoyi daban- daban da kuma a daidaiku.

 Misalin-

Turawa da suka zo Kano akwai Dr. Barth da kuma Mr. Clappertom da Mr. Denham da Mr. Oudney, Wasu dag cikinsu ma sunzo ne da shiga irin ta Larabawa ta yadda ba za a gane su ba.

 Mr. Clapperton ya ce, da isowarsa kasaitacciyar ganuwar gari ta Kano, ya yi matukar murna da farin ciki. Amma ya yi mamaki, maimakon ya fara ganin manya-manyan gine-gine irin na Larabawa a cikin gari, tun daga shiga cikin badala, sai da ya yi tafiya mai nisa kafin ya isa ga gine-

ginen cikin gari. Ba kamar yadda ya sami labari ba, shi dai birnin (Kano) mai girman gaske ne, ga jama'a masu yawa, wasu suna shiga wasu suna fita, amma kuma ba su kula da shi ba, saboda irin shigarsa da launin fatarsa.

 Ya ce, saboda rashin kulawa da shi, shi ma bai kula da mutanen ba, ballantana ya ba da labarinsu. 

  Ya ci gaba da cewa, hakika ko a wancan lokacin akwai mutane masu yawan gaske da gine-gine a birnin Kano. Yawan mutane a Kano ya fi na kowanne daga cikin garuruwan da ya gani a Afirika, Akalla a cikin garin akwai mutum dubu talatin (30,000) ko dubu arba'in (40,000) a hautsine da bakin mutane daga nahiyoyin Afirika wadanda suka zo ciniki. 

   Garin kuma yana da yawan kududdufai. Daga Arewacin garin akwai wasu fitattun duwatsu guda biyu wato Dala da Goron Dutse, kowanne kuwa tsawonsa ya kai kafa 200. A dab da kofar gari kuwa wato à cikin badala akwai babban dakali wanda 'yangadi suke hawa su hango wajen gari.

  A tsakiyar gari cikin wani kurmi akwai wata ƙasaitacciyar kasuwa tana cike da manya-manyan fatake da dillalan bayi. Sannan  kuma suna yin ciniki ne ta hanyar furfure. Alal misali, wani ya zo da gishirinsa tafi daya, sai suka yi musaya da mai kifaye biyar. Wani kuma da ya kawo tunkiya aka saye ta da adadin wuri masu yawa."

Daga littafin

DAULAR FULANI A KANO, na   Alh Nasidi Umaru (Galadiman Daji)

Saturday, 23 January 2021

01- HIKAYAR SAIFUL MULUKI DA ALJANNA BADI'ATUL JAMALI

 HIKAYAR SAIFUL MULUKI DA ALJANNA BADI'ATUL JAMALI

NA ƊAYA

A zamanin da, anyi wani sarki daga cikin sarakunan Ajamawa a Hurusan, sunan sa Muhammadu ɗan Sabbaki. Kowacce shekara yakan kai yaƙi ƙasashen Hindu, da Sindu, da Sinnu dama wasu ƙasashen na Ajamawa. Shi kuwa adalin sarki ne, ga shi kuma da jarumtaka kamar ache ya fi kowa. Al'adarsa kuwa itace yana matuƙar son labaru da hikayoyi da waƙoƙi da firarraki da labarun mutanen da ke gare shi.

A haka har sai da ya kasance duk wanda ya samu baƙon labari ba ya zamewa ko ina sai wurin sa, idan kuwa har labarin ya gamshe shi, sai aga ya cika mutum da kyaututtukan dinari da tufa guda dubu da ƙwarƙwara da taka-haye a matsayin sallamar sa.

  Labarin wannan sarki ya shahara a cikin alƙaryu.

  Sai dai kuma wannan Sarki, yana da wani mugun waziri, bahili, mai yawan hassada ga mutane. Idan sarki ya yi wa mutane alheri sai ya rinƙa yin hassada, ya riƙa cewa: "Irin abin nan da kake yi, shi yake ƙarar da dukiya, har gidaje su risbe". 

  Sarki kuwa ya kan mayar masa da martanin cewa " wannan hassadar kace waziri, al'amari dukkan sa ga Allah yake".

   Ana nan rannan Sarki yaji labarin wani malamin  mawaƙi, attajiri mai yawan alheri, sunan sa Hassan. Wanda darajar sa ta ɗaukaka, mutane sai yabon sa suke yi, suna cewa babu tamkar sa a wajen hikima da da-ɗa-ɗan hikayoyi. Sai kuwa Sarki ya aika aka kirawo masa shi.

   Da zuwan Hassan, sai sarki yace masa " Ya Hassan, kayi sani cewa waziri na ya saɓa mini alkawari, ya zama maƙiyina domin dukiyar da nake baiwa mawaƙa da masu hikayu. Ina son yanzu ka gaya mani wani baƙon labari mai-ban al'ajabi wanda ban taɓa jinsa ba.

 Idan har ya ƙayatar dani, zan baka yankin ƙasa ta guda ɗaya, kuma in sanya dukkan abin da na mallaka cikin hannun ka, in ɗora ka bisa kan waziri na dama gare ni, ka zamo mai yin hukunci ga talakawa.

  Idan kuwa baka zo mini da abin da na ce maka ba, zan washe ka, in kore ka daga ƙasata".

  Hassan yace "Ran sarki ya daɗe, an gama.. Amma idan ka yarda, kayi hakuri, ka bani jinkiri na shekara ɗaya tak. Bayan haka, zan baka labari wanda baka taɓa jin kamar sa ba, wanin ka ma bai taɓa jinsa ba daɗai a ƙasar nan idan Allah yaso".

Sarki yace "Jeka nayi maka wannan jinkiri, amma da sharaɗin banda fita, banda hawa, sannan kada kazo guri na sai bayan shekara ɗaya".

  Daga nan Hassan attajiri ya durƙusa yayi bankwana da saeki ya wuce gida.

   Da komawar sa gida sai ya zaɓi mutane biyar malamai marubuta mahankalta acikin bayin sa. Yace dasu " Ban neme ku ba sai don wannan rana mai kamar ta yau, ina so ku taimake ni bisa ga biyan buƙatar sarki, ku tsamar dani daga hannun sa"

  Suka ce " Rayukan mu fansa ne gareka ya sidi, me kake da buƙata a tare damu?".

  Attajiri Hassan yace " Ina son kowanne ɗayanku ya shiga ƙasashe, ya binciki malamai da ma'abota labaru da hikayoyi, ku tono mini labarin Saiful Muluki.. 

Ko a gurin wa kuka same shi, kuyi ƙoƙarin da ya baku labarin ku ruwaito shi gare ni, ko da dinare dubu ya nema a gareku ku bashi, ina son kuzo mini dashi.

  Wanda duk a cikin ku yazo mini da wannan labarin a cikin ku, na ƴanta shi, zan bashi komai na duniya guda dubu, kuma zai zama shine wakilin gidana duka".

   Daga nan bayi suka ɗauki guzurin tarin dukiya sannan suka bazama cikin duniya suna masu neman hamshaƙin labarin Saiful Muluki da Aljanna Badi'atul Jamali. 

Ɗaya daga cikin su ya nufi Hindu da Sindu, na biyun su ya nufi ƙasar Ajami da Sinu, na ukun su ya nufi ƙasar Yamma, na huɗun su ya nufi ƙasar Sham, sai na biyar ɗinsu ya nufi ƙasar Masar. ..

TARIHIN GARIN KURA

 

Sunday, 17 January 2021

TARIHIN DORAYI

 TARIHIN ƊORAYI

Sadiq Tukur Gwarzo

Marubuci Alhaji Ahmad Bahago ya ruwaito a littafin sa KANO TA DABO TUMBIN GIWA: Tarihin Unguwannin kano da Mazaunanta da Ganuwa da Kofofin Gari, cewa;- A da duk filin wannan unguwa ta Ɗorayi itatuwan ɗorawa ne. Shi ne dalilin da ya sa ake cewa da wannan waje Ɗorayi.

Yace kuma "an kafa unguwar tun zamanin sarkin kano Abdullahi Maje karofi. Asalin mazauna unguwar bayin sarki ne, kuma akwai gidajen ƴaƴan sarki a wajen. Sarkin Haɗeja da na Kazaure a unguwar suka zauna suka yi karatu".

  Sai dai kuma littafin Tarihin Kano 'KANO CHRONICLE' ya kawo zance mai saɓawa wannan, sannan ya sanya kafuwar Ɗorayi nesa sosai da abinda Alh Ahmad Bahago ya ruwaito.

  Duk da yake littafin Kano chronicle bai kawo zance game da asalin inda kalmar 'Ɗorayi' ta samo asali ba, amma an jiwo sunan wani bamaguje mai suna 'Ɗoriyi (ko Ɗorayi) ɗan Bugazau' ɗaya daga waɗanda suka so yiwa sarautar kano zagon ƙasa a zamanin sarkin kano na shidda Naguji ɗan Ɗariki, lokacin da alaƙa ta soma tsami kenan tsakanin masu riƙe da sarautar kano jikokin Bagauda da kuma masu bautar tsumburbura.

   Ga abinda yazo a kano chronicle game da unguwar Ɗorayi:-

 A cikin zamanin Sarki na goma sha biyar Dawuda Baƙin-damisa, wani sarki mai suna Dagaci ya zo daga Barno tare da jama'a masu yawa da malamai. Shi ne yazo da bayanin bangar doki da pampami da tuta da bindiga.

  Yayin da ya iso Bampai, sai sarkin Kano ta fita zuwa gareshi. Sa'ad da ya sadu dashi, sai ya ganshi sarki ne mai-girma, ya bar shi ya komo gida, ya yi shawara da jama'arsa yace "wannan mutum ina zai zauna?" 

   Sai Galdaima Babba ya ce masa "Idan ka bar shi ya zauna a cikin wannan alƙarya wallahi zai mallaki wurin da ya zauna duka". 

Sarki yace "A ina zai zauna acikin wannan alƙarya tare da rundunar sa, Ganuwa ta kuntata da mutane, sai ko a ƙara ta?"

  Sa'annan sai Sarki ya aiki Galadima Babba wurin sa ya zo da shi, aka gina masa gida a Ɗorayi, da jama'ar sa duka. 


Saturday, 2 January 2021

1. TAKOBI A HANNUN MATA: TARIHIN FITATTUN MATA DA SUKA YI IKO DA KANO

 TAKOBI A HANNUN MATA: TARIHIN FITATTUN MATA DA SUKA YI IKO DA KANO


Sadiq Tukur Gwarzo


1.0 GABATARWA

Ɗumbin Tarihi, ƙasaitacciyar masarauta, dogon zamani, sharafi, nasibi, iko da nufi, tumbatsa da nasara, duk sun tabbata ga kano. Mutane da dama sun yiwa kano kirari mai nuna kwarzantakar ta gami da ɗaukaka a tsawon zamunna, amma watakila mafi daɗaɗa rai shine wanda Farfesa Sani Zahraddin, babban limamin kano ya kawo yayin ta'aliƙin sa ga littafin Tarihin Kasuwanci da ƴan kasuwar kano wanda marigayi marubuci Maje Ahmad Gwangwazo ya wallafa, yana mai cewa: ana yiwa kano kirari da:- '

Ka misulu alfin, 

Jalla babbar Hausa, 

Gari ba kano ba dajin Allah, 

ko dame kazo an fika'.

  Manufar wannan rubutu shine zaƙulo wasu fitattun mata waɗanda suka taka rawar gani wajen iko da kano, ko ace waɗanda suka samu gagarumar nasarar aiwatar da muradun zukatun su sabili da nasabar su da masu zartar da iko a kano. Wannan birni na kano mai tsohon tarihi bai taɓa samun jagora mace ba a iya abinda muka riska, amma kwatan-kwacin mulkin da turawan mulkin mallaka suka aiwatar a ƙasar hausa (in-direct rule) ta hanyar sarakunan gargajiyar lokacin su, akan iya cewa an samu zamunnan da mata ke irin wancan mulki a sakaye. Don haka wannan rubutu zai bi diddigin irin waɗannan mata ne tun daga zuwan Bagauda kano har zamanin da muke ciki (2021) da yardar Allah.

 2.0 KAƊAN DAGA TARIHIN KAFUWAR KANO DA SOMA IKO DA ITA

Akwai mabanbantan zantuka game da tarihin kano.

Amma dai ama iya cewa shekaru sama da dubu biyu da suka gabata, sun tabbatar da cewa akwai mutane masu rayuwa a Afirka ta yamma. Waɗannan mutane basu da wata sana'a sama da farauta. A wancan lokacin sana'ar noma bata shahara ba a duniya, don haka mutane suka fi dogaro da farautar namun daji a matsayin aikin yi. Lokaci yana tafiya, har labarin wani babban dutse ya fara zama shahararre a kunnuwan mafarauta. Dalili shine, akwai namun daji masu yawa a yankin da dutsen yake. Sannan ana iya haƙo Tama sinadarin haɗa ƙarfe a wurin. Waɗannan abubuwan suna daga mafi daraja a wancan lokaci. Domin akasarin kayayyakin farautar waɗannan mutane da duwatsu aka sassaƙa su, don haka suke da matuƙar buƙatar kayayyakin ƙarfe masu daraja da sauƙi wajen sarrafawa. Sunan wannan dutse DALA.

    A bisa wata mahangar ta masana, wasu na ganin yankin Dala a matsayin wuri ne wanda k'abilu daban-daban (kazo-na-zo) ke taruwa domin shiga dajin dake kusa dashi don yin farauta. Shine har wasu ke ganin babu takamai_miyar ƙabilar da ta fara zama a yankin. 

  Haka kuma babu takamaiman wanda ya fara zuwa bakin wannan dutsen, wasu sunce mambobin wata ƙabila da suka taso daga wani birni mai suna Dahlak dake Habasha (daga baya sunan ya koma Dala) ce ta fara zama a wurin, daga nan aka sanyawa dutsen suna Dala, wasu kuma suka ce sunan wanda ya fara gina gida akan dutsen tare da fara rayuwa akai shine Dala. Don haka ake yiwa dutsen kachokan laƙabi da sunan sa.

   Daga bisani dai, sai mutane suka fara zama kadan-kadan a gefen dutsen domin neman arziki. Maƙera na zuwa don haƙo tama da ƙarfe tare da sarrafawa, mafarauta kuma na zuwa don siyen ƙarafa tare da shiga farauta a dajin dake bayan dutsen Dala, kamar dai yadda yake a tarihi, za'a ga cewa mutanen da suka gabacemu sunfi rayuwa a wuri mafi daraja. Watau sa'ar da ruwa yake da tsada a wuri, sai kaga mutanen sun gina gari a wurin da ruwa yake, kamar yadda ya faru a garuruwan Makkah da wasun su.

  Waɗanda suka ce Dala ne ya fara zama akan dutsen, sun cigaba da cewa ya rayu tsawon shekaru masu yawa akan wannan dutse, tare dashi akwai matarsa da 'ya'yansu bakwai, huɗu maza uku mata. Wani mai suna Garegaji aka bayyana a matsayin babban ɗansa, shine kuma akace uban wani ƙaƙƙarfa mai suna Nuzamu, Nuzamu kuwa ance shine ya haifi Barbushe. Barbushe mutum ne ƙaƙƙarfan gaske, wanda akace yakan iya kashe giwa ya saɓota a kafaɗa duk girmanta.

 Littafin Tarihin Kano 'Kano chronicle' ya faro tarihin kano ne daga lokacin Barbushe. Shine ma har wata masaniyar tarihin Nigeria mai suna Elizabeth Isichei tayi hasashen cewa Barbushe ɗan k'abilar Sao ne saboda yadda akace girmansa da ƙarfin sa yake yafi kamanceceniya da ƙabilar ta sao. Ƙabilar sao kuwa itace tsohuwar ƙabilar da tarihi ya nuna cewa al'ummar kanembou (Kanem) sun samo tsatso daga garesu.

  Tarihi dai ya nuna cewa a lokacin Barbushe shine sarkin mutanen dake zaune a zagayen dutsen Dala. Kuma suna da al'adar bautawa wani gunki mai suna 'Tsumburbura' wanda yake can kan saman dutsen dala, akan wata bishiya wadda take zagaye da katangu mai suna Shamus. Ance babu mai shiga wurin dodon tsafi tsumburbura sai barbushe. Duk kuwa wanda ya shiga sai ya mutu. Barbushe kuwa ance a saman dutsen yake rayuwa abinsa. Yana saukowa ga mutanen sa sau biyu a shekara domin gudanar da bikin bauta na al'ada. A lokacin mutane ke taruwa sosai a bakin dutsen na Dala suna jiran saukowar sarkinsu barbushe. Wanda yake saukowa gabanin faduwar rana. Yana mai buga ganguna. Sai yayi kirari da yabo ga tsumburbura, mutane suna tayashi. Daga nan akace sai yahau sama mutanen na biye dashi a baya har izuwa saman dutsen na dala. Wanda akace daf da isarsu saman dutsen sai mutanen su yanka hadayar da suka kawowa tsumburar, abinda sukan yanka kuwa shine ; bakin kare, bak'ar kaza, ko bak'ar akuya. Idan suka isa bakin d'akin bauta kuwa, sai kowa ya tsaya. Barbushe ne kadai ke shiga. Kafin shigarsa ance sai yayi kirari da kuwwa. Yana cewa "Sai ni magajin dala. Mutane dole su bini, ko sunƙi ko sun so". Daga bisani idan ya fito, sai ya jagoranci yin bautar tsumburbura, wadda ake zagaya dakin bauta ana rawa da kiɗa tsirara.

  Idan an kammala kuma sai aci asha a wurin. Sannan sai barbushe ya fadi saƙon da tsumburbura ya bashi. Saƙon da a mafi akasari akace labari ne na abubuwan da zasu faru a shekara mai zuwa. 

Duk waɗannan abubuwa ana hasashen sun faru ne a shekaru ƙasa da shekara ta 900AD (miladiyya) bayan wafatin Annabi Isah AS. Koda yake Marubucin littafin Kitab Al-buldan mai suna Al'yaqubi bayan yawace-yawacen sa da yayi a yammacin Afirka, ya ruwaito a shekarar 872-873 cewa "akwai wata masarauta awani wuri dake tsakanin masarautar kanem da tafkin kwara (dai-dai da ko kuma kusa da inda kano take a yanzu), mai suna 'HBSH'. Sunan mai mulkinta 'MRH' sunan birnin ta 'ThBYR'. Rashin wasulla a waɗannan kalmomi yasa shakku da jayayya a tsakanin masana tarihi. Domin wasu na hasashen sunan masarautar shine Hausa, (domin kuwa sunce HBshH na nufin Habasha ne), sunan da ake tsammanin daga cikinsa aka samo sunan Hausa. Wasu kuma na hasashen cewa masarautar ta auku ne a kusa da kano, amma daga baya kafuwa da ƙarfin da kano tayi ya rusa ta, ya kuma yi sanadiyyar komawar mutanen ta zuwa kanon.

   Koma ya abin yake, daga baya littattafan tarihi na kano misalin 'Kano chronicle' (har yanzu ana taba-bar wanda ya rubuta shi),  sun ruwaito cewa wani mai suna Bagauda ne ya zama sarkin kano na farko a tarihi a shekarar 999AD. Shi kuwa Bagauda wasu na cewa jikan Bayajidda na Daura ne, kuma daga garin Gaya suka taso shi da al'ummar sa, wai sunan su shine 'Abagayawa' (waɗanda suka zo daga gaya) ko ɗaya daga Gaudawa, shiyasa kuma ake kiransa da 'Bagauda', ma'ana, mutumin- Gaudawa, kamar yadda mallam bahaushe ya fitar da Bakibɗe daga Kibɗawa. 

   Wasu kuma  suka ce sam, Bagauda ba jikan Bayajidda bane, yazo yankin Dala ne tare da wata runduna mai yawa kamar yadda Barbushe ya taɓa bada labarin zuwan su, kuma ainihin sunan sa shine kano, don haka daga sunan sa kano ta samo asalin sunan ta. Amma kuma wasu sun tafi akan cewa Kano, sumam waninshahararren mautum ne mainsana'ar ƙira wanda yayi sharafi a gefen tsaunin Dala, wanda har ɗaukakar sa ta sanya ake kiran gurin baki ɗaya da sunan sa. Don haka a mahangar su Bagauda daban, Kano daban.

  3.0 FITATTUN MATA DA SUKA YI IKO DA KANO..

Sunday, 1 November 2020

TARIHIN JAGABAN, CHIF BOLA AHMED TINUBU

 ikakken sunan sa shine Bolanle Ahmed Adekunle Tinubu

Bolanle; a yarbanci na nufin, "wanda aka haifa cikin arziƙi," Adekunle kuma na nufin ; "Ƙari akan adadin yalwa da arziƙin iyali''. Sunan Ahmed kuwa  daga sunan shugaba ne Annabi Muhammad, S.A.W, wanda yake shine Muhammad Ahmad, cikamakin annabawa, abin godiya.

Shine mai rike da sarautun 'Asiwaju' na Lagos da kuma 'Jagaban' na masarautar Borgu dake jihar Niger.

An haife shi a ranar 29 ga watan Maris na shekarar 1952 a mafi inganci, a cikin birnin Ikko (Lagos). Shi musulmi ne.  Ya halarci makarantar firamare mai suna St. John's Primary School, dake Aroloya a Lagos, sai sakandiren Children's Home School dake Ibadan. Tinubu ya samu tafiya kasar Amurka domin karo karatu a shekarar 1975, inda ya soma karatu a kwalejin Richard J. Daley College dake Chicago, Illinois kafin daga bisani ya koma jami'ar jihar Chicago mai suna Chicago State University. Ya samu kammala digirin sa a shekarar 1979 daga wannan jamiar inda ya karanci Ilimin gudanarwar kuɗi da ake kira "Accounting".


Tinubu yayi aiki da kamfanin Amurka mai suna Arthur Andersen, da kuma wasu kamfanonin irin su Deloitte, Haskins, & Sells, da GTE Services Corporation duk a can Amurka. Bayan komowar sa gida Nigeria a cikin shekarar 1983, Bola Tinubu ya soma aiki da kamfanin Mobil Oil Nigeria, kafin daga bisani ya zamo cikin jagororin kamfanin.

 Ya soma shiga harkokin siyasa ne a shekarar 1992, lokacin da ya shiga jamiyyar Social Democratic Party (SDP) inda ya zamo mamba na ɗariƙar  'Peoples Front' wanda marigayi Shehu Musa Yar'Adua ke jagoranta, ɗarikar da ta ƙunshi manyan ƴan siyasu irin su marigayi shugaba Umaru Yar'Adua, Atiku Abubakar, Baba Gana Kingibe, Rabiu Kwankwaso, Abdullahi Aliyu Sumaila, Magaji Abdullahi, Dapo Sarumi da Yomi Edu da wasunsu. 

  An zaɓi Bola Tinubu a matsayin sanata mai wakiltar sanatoriyar Lagos ta yamma a jamhuriya ta uku wadda bata yi nisan zango ba sojoji suka yi juyin mulki tare da rushe mulkin dimokraɗiyya baki ɗaya.


 Bayan soke zaɓen shugaban ƙasa na kwanan watan '12 June' na shekarar 1993, sai Tinubu ya zamo ɗaya daga iyayen da suka kafa gungun kungiyoyin rajin dawo da mulkin dimokraɗiyya a Nigeria, kungiyar da ta shiga wayar da kan ƴan ƙasa akan nuna rashin goyon bayan mulkin soja da kuma ayyana marigayi Moshood Abiola a matsayin wanda yaci zaɓen shugaban ƙasa da aka soke na ranar 12 ga watan yunin 1993. 

Don haka, juyin mulkin da marigayi Shugaban ƙasa a wancan lokaci Abacha yayi na zamowa shugaban ƙasa da kuma yunkurin da yayi na ɗaukar tsauraran matakai akan masu niyyar bashi matsala a mulkin sa, sai Tinubu ya ƙetare ya bar Nigeria, bai sake dawowa ba sai bayan rasuwar Abacha a shekarar 1998, inda aka soma kafa tubalin ginin jamhuriya ta huɗu. 


A zaɓen shekarar 1999, Bola Tinubu ɗaya ne daga shugabannin jamiyyar Alliance for Democracy (AD), tare dasu Abraham Adesanya da Ayo Adebanjo. Ya shiga zaɓen firamare na jamiyyar ta AD a matsayin ɗan takarar ta na Gwamnan jihar Lagos, kuma ya samu nasara, inda ya doke abokan takarar sa na lokacin  Funsho Williams da Wahab Dosunmu, tsohon ministan ayyuka a Nigeria. Don haka a zaɓen shekarar 1999, Bola Tinubu ya samu tsayawa takarar gwamnan jihar Lagos a karkashin tutar jamiyyar AD, tare da samun nasarar lashe zaɓen cikin kwanciyar hankali.

A zaɓen shekarar 2015 kuwa, Tinubu shine jagoran gamin gambizar jamiyyan AC, ANPP, da CPC waɗanda suka dunƙule tare da komawa inuwar jamiyyar APC. Shine kuma ya jagoranci marawa shugaban ƙasa Buhari baya har ya samu tikitin takara a jamiyyar ta APC, har kuma daga bisani ya samu nasarar lashe zaɓen shugabancin ƙasar baki ɗaya.

Tuesday, 6 October 2020

2. HIKAYAR SAIFUL MULUKI DA BADI'ATUL JAMALI

 HIKAYAR SAIFUL MULUKI DA ALJANNA BADI'ATUL JAMALI

NA BIYU

Bayana wata huɗu, mutane huɗu suka dawo, ba su samo kome ba, suka ba shi labarin  binchiken su da isa matuƙa ga kokarin su. Allah bai rabbatar da wannan nufi da suka tasamma ba, sai ran attajiri ya dugunzuma matuƙa ainun.

   Na biyar ɗin su shine wanda ya nufi ƙasar Sham, watau shine na huɗu a lissafi, bai zame ba sai Dimashƙu.

   Ya same ta babbar alƙarya ce mani'imchiya, ya zamna nan yana tambaya, babu wanda ya ce masa ci kanka.

  Yayi haramar fita ya sake tafiya zuwa ga wani garin sai ya hangi wani yaro yana famfala gudu, yana tuntuɓe da ƙafarsa.

  Yace masa "kai samari, me ya faru kake gaggawa haka? ina zaka?."

  Sai yaro yace "zani majalisar wa'azin wani tsohon Malami ne wanda yake zama rana mai kamar ta yau, yana bada labaru da daɗaɗan hikayoyi waɗanda daɗai mutum bai taɓa jinsu ba; don haka nike gaggawar in samu zuwa wurin da wuri don kada na rasa wurin zama, ina tsoron matsatsi."

   Yace masa "in biyo ka?" Yaro yace ''in kana iya gudu zo mu je".

   Sai kuwa ya ja ƙyauren ɗakinsa ya kulle, ya bi saurayin nan a guje. Da suka isa sai suka tarar da dattijo zaune bisa kujerar sa, bai soma ko Basmallah ba. Suka zauna kusa dashi, suka kasa kunnuwan su gare shi.

  Zuwa jimawa, sai Malamin ya shiga bada labarai, bai tashi ba sai da rana ta kusa faɗuwa. 

Da gamawar sa, jama'a suka watse, sai magudancin nan ya kusance shi, yayi masa sallama; ya amsa masa suka gaisa da juna sannan yace "Allah ya bamu albarkacin Mallam, idan ka yarda ina so nayi tambaya". Mallam yace "Allah ya sanasshe mu, tambayi abinda kake so ya ɗana". 

  Sai yace "Ko Allah ya sa kana da labarin Saiful Muluki da Badiatul Jamali?" 

Tsoho yace "kai kuwa a ina ka samu wannan zanche? wa ya gaya maka wannan labari?"

  Yace "ji nayi, neman sa kuwa na fito, kuma shi ya taso dani daga nisan duniya zuwa nan. Idan kana dashi ina bara ka sanad dani don Allah da Annabin sa domin alherin ka. Abinda ka nema kuwa duk zan baka, da dai raina a hannu yake, in kache shi ka ke so wallahi da na baka."

  Ɗan Tsoho yace " Yi farin ciki, buƙatar ka ta biya: amma bani faɗawa kowa bisa tafarki, ban kuwa taɓa faɗawa kowa shi ba daɗai. Idan kana son sa kazo gidana tare da dinari ɗari, zan gaya maka shi bisa sharaɗi biyar".

  Yace "Zan baka dinare ɗarin da ka ambata, zan kuma baka goma kafin alƙalami,  zan amshi wannan hikaya da dukkan sharaɗin da zaka ambata akanta."

  Tsoho yace "tafi gobe da safe kazo da su ka riƙi buƙatar ka".

  Ya tashi ya sunkuya yayi godiya gun tsoho ya tafi makwancin sa yana cike da murna, ya zuba dinari ɗari da goma a cikin rarita, da fitowar alfijir ya tashi yayi wanka ya sa tufafin sa ya ɗauki mayani ya tafi gidan malami yayi sallama, da fitowar sa sai ya gaishe shi sannan ya miƙa masa jaka.

  Tsoho ya amsa yayi godiya ya shiga tare dashi zuwa shamakin sa, ya shiga ya fito masa da da tawada da alkalami da takardun rubutu, ya mika masa wani  littafi  yace "shine wannan littafi mai ɗauke da wannan hikayar". 

Ya amsa ya duba ya rubuce shi, ya karance shi ga malamin, sannan tsoho yace masa 

"Ya ɗana, farkon sharaɗin  da zan gaya maka shine kada ka bayar da wannan labari akan tafarki, na biyu kada ka gayawa mata shi, na uku kada ka gayawa wawayen mutane shi, na huɗu kada ka gayawa yara, na biyar karatun sa sai a gun sarakuna."   Bawan Attajiri Hassan Yace "to naji na karɓa", ya durkusa yayi godiya sannan ya tafi.

   A wannan lokacin saura kwanaki goma wa'adin sarki ga ubangijin sa Hassan ya cika, don haka yayi saurin aikewa da mai bushara zuwa gareshi, sannan cikin hanzari ya haɗa kayan sa ya nufi komawa gida.

  Sannu a hankali ya isa gida, koda attajiri yayi arba dashi sai ya rungume shi don murna, ya cire tufafin jikinsa na alfarma ya danƙa masa su, ya bashi ingarmun dawakai goma, taguwowi goma, alfadarai goma, bayi goma, waɗannan fa duk a matsayin barka da sauka ne ba a cikin ladan aikin sa ba.

 Bayan haka, Hassan attajiri ya sake rubuta wannan hikaya da hannun sa, sannan ya tafi ya yiwa Sarki albishir da ita a ranar da wa'adin su ya cika.

 Sarki ya cika da farin ciki, sannan ya aike a tara masa dukkan sarakunan sa, da malamai da mahankalta da masu duban tamrari duk na ƙasar sa, da suka gama taruwa sai Hassan attajiri ya labarta wannan hikaya a garesu.

   Ɗaukacin jama'ar suka cika da mamaki, babu wanda ya taɓa jin wannan hikaya mai daɗin gaske daɗai, babu zato sai dinare da azurfa da jauharori ke ta zuba akan Hassan Attajiri, ana yi masa kyauta dasu.. 

  Sarki ya shiga gida ya tuɓe tufafin jikin sa ya kawo masa su kyauta, ya mallaka masa yankin ƙasa guda, ya sanya shi wazirin dama. Yayi umarni a rubuta masa wannan labarin da ruwan dinari a taskance masa shi a taskar sa, a duk lokacin da ransa ya ɓaci sai Waziri Hassan ya karanta masa shi, kafin ya ƙare sai kaga farin ciki da annushuwa ya dabaibaye shi.

 Ga yadda wannan hikaya take:-

  A zamanin da anyi wani sarki a Masar, sunan sa Asimu ɗan Safwana...