TARIHIN KASUWANCI A KANO
Tsakure daga littafin 'Kano cibiyar Kasuwanci ta Africa' wanda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo (Allah yajiqansa da Rahama ya wallafa).
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
Kashi na biyu
A karni na goma sha biyar, zamanin mulkin Sarkin Kano Muhammdu Rumfa, wasu turawa fatake sunzo kano daga girka. Kasarsu acan kusa da Istanbul take, ana kiranta Yunana, a yankin kasashen Turawa.
Su waɗannan turawa sunzo kano ne domin fatauci, sun kai kimanin arbain, da rakuma kusan talatin da biyar, masu ɗauke da kayayyakin dukiyoyi masu yawa kamarsu alkyabbu, jabbobi, falmarori, kuftoci, jauhohi, hulunan dara, takalma, kilisai, takardu da kuma takubba.
Sai waɗannan fatake suka iso kofar fadar sarki, suka nemi iso sannan sukayi gaisuwa gareshi da larabci.
A cikin malamn da suke zaune, sai wani Malami mai suna Abdurrahman ya rinka fassara maganarsu da hausa.
Daga nan sai waɗannan fataken suka gayawa sarki Muhammadu Rumfa cewa su ba larabawa bane, Turawa ne mutanen Giris. Sun iya larabci ne kurum kuma fatauci ne ya kawosu kano. Nan take sai suka fito da kayayyakin da suke siyarwa.
Da yake a wannan zamanin, ba'a soma ciniki da kuɗi ba, sai sarkin na kano ya tambayesu cewa ku kuma me kuke da bukatar saye a wurinmu? Sai sukace muna bukatar bayi, fatu, kiraga, albasa da tafarnuwa. Daga nan sai sarki yace yana bukatar dukkanin kayayyakin nasu, sannan yasa a shirya musu kayayyakin da suke da bukata.
Ance an basu masauki a inda asbitin unguwar Marmara yake a yanzu, akayi musu ɗakuna dogaye da tsangayu masu faɗi da tsawo, aka yi musu hayin shirayi, sannan kowanensu aka bashi gado da tabarma.
Sarki ya tura musu bayi domin suyi musu hidima. A lokacin saida bayin suka haka musu tijiya domin samar musu da ruwa saboda rashinsa, shine har akace idan turawan suna bukatar ruwa sai suce Akwa, wai sunan ruwa kenan da yarensu, daga bisani sai aka sanyawa rijiyar suna 'Yar Akwa.
Waɗannan turawa da suka zo a zamanin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa, sune suka fara kawo takardu da takobi. Suna kiran takardu "Yarta krata", takobi kuma "Takopis". Watakila daga nan sunayen suka samo asali domin da harshen hausa kansakali ake kiran takobi.
Da lokacin tashin fataken yayi, sai suka haɗa gagarumar kyauta suka baiwa sarki, sarki ya ɗauki nasa ya kuma rarrabawa hakimansa, sannan yasa aka basu bayi hamsin mata da maza, da dawaki masu yawa, gami da sauran kayayyakin da suka bukata tunda fari, sannan aka haɗa tawaga domin tayi musu rakiya.
Suka fita daga kasar kano, suka bi ta wani gari mai suna Dingas zuwa Damagaran, suka kalli hanyar Tunis, suka shiga cikin sahara har zuwa Wani gari mai nisan gaske dake cikin sahara a yankin Libya, sunansa Murzuk, daga nan suka dangana da birnin Turawa a bakin babban tekun bahar Rum, suka shiga manyan jiragen ruwa, suka koma kasar su ta girka. Waɗannan sune turawan farko da suka soma zuwa kano.
Tsakure daga littafin 'Kano cibiyar Kasuwanci ta Africa' wanda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo (Allah yajiqansa da Rahama ya wallafa).
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
Kashi na biyu
A karni na goma sha biyar, zamanin mulkin Sarkin Kano Muhammdu Rumfa, wasu turawa fatake sunzo kano daga girka. Kasarsu acan kusa da Istanbul take, ana kiranta Yunana, a yankin kasashen Turawa.
Su waɗannan turawa sunzo kano ne domin fatauci, sun kai kimanin arbain, da rakuma kusan talatin da biyar, masu ɗauke da kayayyakin dukiyoyi masu yawa kamarsu alkyabbu, jabbobi, falmarori, kuftoci, jauhohi, hulunan dara, takalma, kilisai, takardu da kuma takubba.
Sai waɗannan fatake suka iso kofar fadar sarki, suka nemi iso sannan sukayi gaisuwa gareshi da larabci.
A cikin malamn da suke zaune, sai wani Malami mai suna Abdurrahman ya rinka fassara maganarsu da hausa.
Daga nan sai waɗannan fataken suka gayawa sarki Muhammadu Rumfa cewa su ba larabawa bane, Turawa ne mutanen Giris. Sun iya larabci ne kurum kuma fatauci ne ya kawosu kano. Nan take sai suka fito da kayayyakin da suke siyarwa.
Da yake a wannan zamanin, ba'a soma ciniki da kuɗi ba, sai sarkin na kano ya tambayesu cewa ku kuma me kuke da bukatar saye a wurinmu? Sai sukace muna bukatar bayi, fatu, kiraga, albasa da tafarnuwa. Daga nan sai sarki yace yana bukatar dukkanin kayayyakin nasu, sannan yasa a shirya musu kayayyakin da suke da bukata.
Ance an basu masauki a inda asbitin unguwar Marmara yake a yanzu, akayi musu ɗakuna dogaye da tsangayu masu faɗi da tsawo, aka yi musu hayin shirayi, sannan kowanensu aka bashi gado da tabarma.
Sarki ya tura musu bayi domin suyi musu hidima. A lokacin saida bayin suka haka musu tijiya domin samar musu da ruwa saboda rashinsa, shine har akace idan turawan suna bukatar ruwa sai suce Akwa, wai sunan ruwa kenan da yarensu, daga bisani sai aka sanyawa rijiyar suna 'Yar Akwa.
Waɗannan turawa da suka zo a zamanin Sarkin Kano Muhammadu Rumfa, sune suka fara kawo takardu da takobi. Suna kiran takardu "Yarta krata", takobi kuma "Takopis". Watakila daga nan sunayen suka samo asali domin da harshen hausa kansakali ake kiran takobi.
Da lokacin tashin fataken yayi, sai suka haɗa gagarumar kyauta suka baiwa sarki, sarki ya ɗauki nasa ya kuma rarrabawa hakimansa, sannan yasa aka basu bayi hamsin mata da maza, da dawaki masu yawa, gami da sauran kayayyakin da suka bukata tunda fari, sannan aka haɗa tawaga domin tayi musu rakiya.
Suka fita daga kasar kano, suka bi ta wani gari mai suna Dingas zuwa Damagaran, suka kalli hanyar Tunis, suka shiga cikin sahara har zuwa Wani gari mai nisan gaske dake cikin sahara a yankin Libya, sunansa Murzuk, daga nan suka dangana da birnin Turawa a bakin babban tekun bahar Rum, suka shiga manyan jiragen ruwa, suka koma kasar su ta girka. Waɗannan sune turawan farko da suka soma zuwa kano.
No comments:
Post a Comment