TARIHIN ƘASAR BAUCHI
SADIQ TUKUR GWARZO
Kashi na huɗu
Kalumbu mayaƙi ne daya tara taron mayaƙa masu yawa da raƙuma da dawakai marasa adadi, ya rubuta takarda ya aikewa sarkin musulmi Muhammadu Bello ɗan Usmanu bn Fodio da cewa " Ka sani, ni na mallaki abinda yake tsakanin mimi biyu (watau abinda yake tsakanin Mirsa da Malle)" yana mai bashi tsoro, yana yi masa narko da waɗansu baitoci dake cikin Nabinga, yace " Ni ina yi muku tsoro, kada rana ɗaya ta samu gareku domin tsananin ƙina, ranar nan kuwa wuyarta kamar ta ranaku masu yawa ce, saboda wuyar ta za a ga taurari da rana, gari zai zama haske ba haske ba, duhu ba duhu ba, har ku motsad da yaƙi mai hauhawa wanda bashi da misali, yana da kamar dare wanda yake cuɗanya da wani dare".
Ko da manzon Kalumba ya riski Sarkin Musulmi da wannan sako, sai ya karɓi takarda ya karanta dukkan abinda ke ciki, sannan bayan ya gama ya juya bayanta, ya mayar da amsa da cewa "Na juyad da lamari na ga Allah, babu kuma ƙarfi ga saɓon Allah, dukkan su masu samuwa ne da ikon Allah". Sannan ya baiwa ɗan aike ya koma da ita.
Sa'ar da Kalumba ya samu martanin sarkin Musulmi sai ya keta takardar bayan ya kammala karantawa, sannan ya hau da rundunar sa zuwa Kano. Ya sauka a ƙasar kano, duk inda ka duba sai jama'a da dawaki kawai ake gani. Jama'ar kano hankalinsu ya tashi, suka firgita firgici mai tsanani.
Ana haka sai Sarki Musulmi Muhammad Bello ya aikewa Sarkin Bauchi Yakubu da yake yaƙia Das da cewa ya tafi wurin Kalumba ya yaƙe shi. Yakubu yace yaji kuma yabi.
Daga nan sai Yakubu tara jama'arsa ya shaida musu halin da ake ciki tare da neman shawarar su, inda nan ma suka nuna goyon bayan su ga bin umarnin Sarkin Musulmi Bello.
Babu jimawa sai Yakubu ya tashi da tawagar sa zuwa Bauchi, ya shiga tara ƴam baka, da ƙarin mayaƙa, sannan ya tashi ya ƙetare ƙasar sa zuwa Kano, ya sauka a wani wuri da ake kira Gantsa inda sansanin Kalumba yake. Rumdunoni biyu suka fuskanci juna, sannam aka soma shirin fafatawa.
SADIQ TUKUR GWARZO
Kashi na huɗu
Kalumbu mayaƙi ne daya tara taron mayaƙa masu yawa da raƙuma da dawakai marasa adadi, ya rubuta takarda ya aikewa sarkin musulmi Muhammadu Bello ɗan Usmanu bn Fodio da cewa " Ka sani, ni na mallaki abinda yake tsakanin mimi biyu (watau abinda yake tsakanin Mirsa da Malle)" yana mai bashi tsoro, yana yi masa narko da waɗansu baitoci dake cikin Nabinga, yace " Ni ina yi muku tsoro, kada rana ɗaya ta samu gareku domin tsananin ƙina, ranar nan kuwa wuyarta kamar ta ranaku masu yawa ce, saboda wuyar ta za a ga taurari da rana, gari zai zama haske ba haske ba, duhu ba duhu ba, har ku motsad da yaƙi mai hauhawa wanda bashi da misali, yana da kamar dare wanda yake cuɗanya da wani dare".
Ko da manzon Kalumba ya riski Sarkin Musulmi da wannan sako, sai ya karɓi takarda ya karanta dukkan abinda ke ciki, sannan bayan ya gama ya juya bayanta, ya mayar da amsa da cewa "Na juyad da lamari na ga Allah, babu kuma ƙarfi ga saɓon Allah, dukkan su masu samuwa ne da ikon Allah". Sannan ya baiwa ɗan aike ya koma da ita.
Sa'ar da Kalumba ya samu martanin sarkin Musulmi sai ya keta takardar bayan ya kammala karantawa, sannan ya hau da rundunar sa zuwa Kano. Ya sauka a ƙasar kano, duk inda ka duba sai jama'a da dawaki kawai ake gani. Jama'ar kano hankalinsu ya tashi, suka firgita firgici mai tsanani.
Ana haka sai Sarki Musulmi Muhammad Bello ya aikewa Sarkin Bauchi Yakubu da yake yaƙia Das da cewa ya tafi wurin Kalumba ya yaƙe shi. Yakubu yace yaji kuma yabi.
Daga nan sai Yakubu tara jama'arsa ya shaida musu halin da ake ciki tare da neman shawarar su, inda nan ma suka nuna goyon bayan su ga bin umarnin Sarkin Musulmi Bello.
Babu jimawa sai Yakubu ya tashi da tawagar sa zuwa Bauchi, ya shiga tara ƴam baka, da ƙarin mayaƙa, sannan ya tashi ya ƙetare ƙasar sa zuwa Kano, ya sauka a wani wuri da ake kira Gantsa inda sansanin Kalumba yake. Rumdunoni biyu suka fuskanci juna, sannam aka soma shirin fafatawa.