TARIHIN FULANI SULLUƁAWA
SADIQ TUKUR GWARZO
Sulluɓawa kuwa jam'i ne na sulluɓe, kalmar da akace an samo ta daga kakansu ko ace asalin wanda zuriyar ta fito daga tsatsonsa mai suna Sisillo. Shikuwa Sisillo, ai miji ne ga bafullatanar nan ta jinsin Toronkawa mai suna Chippowo, kanwa ga bafullatani batoranke Mallam Usmanu Toroddo, waɓda yake kakan-kakan shehu Usmanu Mujaddadi ɗan fodio.
Don haka ake ɗaukar jinsunan sulluɓawa da toronkawa na fulani a matsayin 'yanuwan juna. (Ado-Kurawa 1989:45-49).
Asalin sulluɓawa wangarawa ne, watau ana iya cewar kakanninsu ne suka taɓa zuwa kano zamanin Sarkin Kano Muhammadu Kanajeji har suka kawowa garin musulunci. Amma suna da alaka da yarukan Mandigo dana Mandika na yankunan Mali.
Sunan asalin yarensu shine wakore, daga baya suka nutse cikin fulatanci yayinda suka mance yarensu suke yara fulbe (Usman 1974: 168-169).
Izuwa yanzu kuwa yana da wuya ko a gidan sarautar kano da jikokin marigayi mallam Ibrahim Dabo ke mulka kaji ana fulatanci, domin tuni sun rikiɗe izuwa hausa zuryan.
An kuma samu cewar jinsin sulluɓawa, sunfi kowanne jinsi tsari mai kyau acikin kabilun fulani tun kafin jihadin shehu Usmanu, domin kuwa suna da shugabancinsu mai suna 'Sarkin Sulluɓawa' a duk inda suke.
Kuma a zandam suka soma zama, daga bisani suka rinka kwararowa yankunan katsina, zariya, sokoto da rima da sauran yankunan hausawa.
Sannan kuma, tun da jimawa suna rike ne da addinin musulunci bisa kyakkyawar turba. Don haka da yakin jihadi ya ɓarke, 'yan kaɗan daga cikinsu ne suka goyi da bayan sarkin gobir, amma mafi yawansu suna cikin waɗanda suka bada gagarumar gudunmuwa wajen samun nasara, don haka nema ɗansu ya samu zamowa sarkin kano.
Wasu jimsunan fulanin da yadda ake gane su sune:
UDAWA : Jakai, rakuma da shanu suke kiwo. Kusan kasar su Niger amma suna fantsaowa har Nigeria.
Bararoji: Suna da fararen shanu, suna siyar da magunguna. Wasunsu nada jakuna.
Hana Gamba: Sunfi kama da Buzaye, suma siyar da magunguna bayan kiwo.
Yaɓeji: Masu fararen shanu
Bakolo: Shanun su babu ƙaho
SADIQ TUKUR GWARZO
Sulluɓawa kuwa jam'i ne na sulluɓe, kalmar da akace an samo ta daga kakansu ko ace asalin wanda zuriyar ta fito daga tsatsonsa mai suna Sisillo. Shikuwa Sisillo, ai miji ne ga bafullatanar nan ta jinsin Toronkawa mai suna Chippowo, kanwa ga bafullatani batoranke Mallam Usmanu Toroddo, waɓda yake kakan-kakan shehu Usmanu Mujaddadi ɗan fodio.
Don haka ake ɗaukar jinsunan sulluɓawa da toronkawa na fulani a matsayin 'yanuwan juna. (Ado-Kurawa 1989:45-49).
Asalin sulluɓawa wangarawa ne, watau ana iya cewar kakanninsu ne suka taɓa zuwa kano zamanin Sarkin Kano Muhammadu Kanajeji har suka kawowa garin musulunci. Amma suna da alaka da yarukan Mandigo dana Mandika na yankunan Mali.
Sunan asalin yarensu shine wakore, daga baya suka nutse cikin fulatanci yayinda suka mance yarensu suke yara fulbe (Usman 1974: 168-169).
Izuwa yanzu kuwa yana da wuya ko a gidan sarautar kano da jikokin marigayi mallam Ibrahim Dabo ke mulka kaji ana fulatanci, domin tuni sun rikiɗe izuwa hausa zuryan.
An kuma samu cewar jinsin sulluɓawa, sunfi kowanne jinsi tsari mai kyau acikin kabilun fulani tun kafin jihadin shehu Usmanu, domin kuwa suna da shugabancinsu mai suna 'Sarkin Sulluɓawa' a duk inda suke.
Kuma a zandam suka soma zama, daga bisani suka rinka kwararowa yankunan katsina, zariya, sokoto da rima da sauran yankunan hausawa.
Sannan kuma, tun da jimawa suna rike ne da addinin musulunci bisa kyakkyawar turba. Don haka da yakin jihadi ya ɓarke, 'yan kaɗan daga cikinsu ne suka goyi da bayan sarkin gobir, amma mafi yawansu suna cikin waɗanda suka bada gagarumar gudunmuwa wajen samun nasara, don haka nema ɗansu ya samu zamowa sarkin kano.
Wasu jimsunan fulanin da yadda ake gane su sune:
UDAWA : Jakai, rakuma da shanu suke kiwo. Kusan kasar su Niger amma suna fantsaowa har Nigeria.
Bararoji: Suna da fararen shanu, suna siyar da magunguna. Wasunsu nada jakuna.
Hana Gamba: Sunfi kama da Buzaye, suma siyar da magunguna bayan kiwo.
Yaɓeji: Masu fararen shanu
Bakolo: Shanun su babu ƙaho
No comments:
Post a Comment