TARIHIN NUFE: LABARIN MALLAM DANDO
Kashi na biyar
SADIQ TUKUR GWARZO
Alƙalin Gwari Ummaru ya ruwaito cewa Farkon labarin Fulanin Nufe ya soma ne da Mallam Dando, wanda yazo ƙasar Nufe daga ƙasar Hausa.
Ance shi mutum ne matsakaici wajen tsawo da haske, bashi da kaurin jiki kuma. Ya iske Nufe a zamanin da Sarki Majiya ke mulki. Sai ya zama almajirin sa.
A zamanin da Mallam Dando yazo ƙasar Nufe yana da ƴaƴa uku, Majigi, Abdu Ɓuya, da Etsu Usmanu. Ya rinƙa yawo garuruwan Nufe yana wa'azi har ya isa Daba.
A wannan garin kuwa akwai wata mahaukaciya tana ɗaure cikin mari, ana kiranta da suna Fatsumako.
Masu magani sunyi har sun gaji ba tare da ta samu sauƙi ba.
Rannan Mallam Dando na shigewa inda take sai tayi ƙara har ya jiyo muryar ta, sai ya tambaya "wanene yake ƙara haka?" sai akace masa "Wata mahaukaciya ce wadda masu magani suka kasa warkad da ita"
Sai Mallam Dando yace "Ku bani ita ina warkad da ita, in Allah ya yarda".
Da waliyanta suka ji sai suka amsa masa da cewa "Mun baka ita". Mallam Dando ya koma gida ya yi rubutu a alluna biyu, ya wanke, ya zuba a cikin ƙoƙuna biyu ya aika musu. Yace ƙwarya ɗaya ayi mata wanka da ita. Ɗayar kuwa a bata tasha. Sannan ya haɗa musu da turare na hayaƙi da za a yi mata turare dashi.
Iyayanta suka aikata kamar yadda manzon Mallam Dando ya sanar musu.
Da aka kwana uku sai Mallam Dando ya tafi don ya ganta, sai yace da iyayen ta "ku kwance mata marin nan". Iyayenta suka yi wa Mallam Dando musu kaɗan, sa'an nan suka yarda suka kwance ta. Mallam Dando ya kaita cikin kafe yace ta zauna nan.
Daga baya sai ya nemi aurenta suka amince masa, bayan sunyi aure ya tafi da ita Juguma suka kwana ɗaki ɗaya. Daga nan bata sake komawa cikin halin hauka ba. Ta sami cikin ɗa Mustafa, sannan ta haifi Muhammadu Saba.
A zamanin da ta haifi Muhammad Saba sai sarki Majiya Zubairu yace yana sonsa, don haka abar shi a hannun sa ya girma.
Akwai wata rana da Sarki Majiya ya shirya zuwa yaƙi Kukuku, mallam Dando ne ya bashi asiri ya kai ya zuba acikin ƙasar, sannan yaci su da yaƙi ya samu dukiya mai tarin yawa. Daya komo gida sai ya aikewa Malamin kuyangi guda biyu a matsayin kyauta.
Mallam Dando ya karɓe su yayi godiya, ɗaya ya mayar da ita sa ɗakan sa, ita ce Habibatu, ɗaya kuma ya aikewa Atiku ɗan Shaihu Usmanu, hasken zamani, kogin talikai, babban waliyi, itace ta haifi Ummaru Nagwamatse. Wannan duk anyi shine bayan rasuwar sarkin Musulmi Muhammad Bello ɗan Shehu Usmanu Ɗan Fodio.
Kashi na biyar
SADIQ TUKUR GWARZO
Alƙalin Gwari Ummaru ya ruwaito cewa Farkon labarin Fulanin Nufe ya soma ne da Mallam Dando, wanda yazo ƙasar Nufe daga ƙasar Hausa.
Ance shi mutum ne matsakaici wajen tsawo da haske, bashi da kaurin jiki kuma. Ya iske Nufe a zamanin da Sarki Majiya ke mulki. Sai ya zama almajirin sa.
A zamanin da Mallam Dando yazo ƙasar Nufe yana da ƴaƴa uku, Majigi, Abdu Ɓuya, da Etsu Usmanu. Ya rinƙa yawo garuruwan Nufe yana wa'azi har ya isa Daba.
A wannan garin kuwa akwai wata mahaukaciya tana ɗaure cikin mari, ana kiranta da suna Fatsumako.
Masu magani sunyi har sun gaji ba tare da ta samu sauƙi ba.
Rannan Mallam Dando na shigewa inda take sai tayi ƙara har ya jiyo muryar ta, sai ya tambaya "wanene yake ƙara haka?" sai akace masa "Wata mahaukaciya ce wadda masu magani suka kasa warkad da ita"
Sai Mallam Dando yace "Ku bani ita ina warkad da ita, in Allah ya yarda".
Da waliyanta suka ji sai suka amsa masa da cewa "Mun baka ita". Mallam Dando ya koma gida ya yi rubutu a alluna biyu, ya wanke, ya zuba a cikin ƙoƙuna biyu ya aika musu. Yace ƙwarya ɗaya ayi mata wanka da ita. Ɗayar kuwa a bata tasha. Sannan ya haɗa musu da turare na hayaƙi da za a yi mata turare dashi.
Iyayanta suka aikata kamar yadda manzon Mallam Dando ya sanar musu.
Da aka kwana uku sai Mallam Dando ya tafi don ya ganta, sai yace da iyayen ta "ku kwance mata marin nan". Iyayenta suka yi wa Mallam Dando musu kaɗan, sa'an nan suka yarda suka kwance ta. Mallam Dando ya kaita cikin kafe yace ta zauna nan.
Daga baya sai ya nemi aurenta suka amince masa, bayan sunyi aure ya tafi da ita Juguma suka kwana ɗaki ɗaya. Daga nan bata sake komawa cikin halin hauka ba. Ta sami cikin ɗa Mustafa, sannan ta haifi Muhammadu Saba.
A zamanin da ta haifi Muhammad Saba sai sarki Majiya Zubairu yace yana sonsa, don haka abar shi a hannun sa ya girma.
Akwai wata rana da Sarki Majiya ya shirya zuwa yaƙi Kukuku, mallam Dando ne ya bashi asiri ya kai ya zuba acikin ƙasar, sannan yaci su da yaƙi ya samu dukiya mai tarin yawa. Daya komo gida sai ya aikewa Malamin kuyangi guda biyu a matsayin kyauta.
Mallam Dando ya karɓe su yayi godiya, ɗaya ya mayar da ita sa ɗakan sa, ita ce Habibatu, ɗaya kuma ya aikewa Atiku ɗan Shaihu Usmanu, hasken zamani, kogin talikai, babban waliyi, itace ta haifi Ummaru Nagwamatse. Wannan duk anyi shine bayan rasuwar sarkin Musulmi Muhammad Bello ɗan Shehu Usmanu Ɗan Fodio.
No comments:
Post a Comment