Friday, 7 January 2022

FALALAR MALAMAI DA TA'AZIYYAR MASANI SHEHU AHMADU BAMBA (Qala Haddasana)

 FALALAR MALAMAI DA TA'AZIYYAR MASANI SHEHU AHMADU BAMBA (Qala Haddasana)


SADIQ TUKUR GWARZO


Sahabi Aliyu R.A ya faɗa ga Jabir ɗan Abdullahi R.A cewa "Duniya ta dogara ne akan abu huɗu; Addini, da Malami, da Mai yin aiki da ilimin sa sai Jahili wanda baya girman kai wajen neman sani, da kuma Mawadaci wanda baya rowa da dukiyar sa.

  Marigayi Sheikh Dr.  Ahmad Bamba ya faɗa mana cewa ilimi ba komai bane sai sanin abu a zuciya da kuma gaskatar sa a zahiri, yayin da jahilci ke nuni da kiyaye abu a zuciya wanda a zahirance ba gaskiya bane. Saboda haka a  cewar sa ba kawai rashin sanin abu ake kira jahilci ba, a'a har ma da sani gami da riƙo na abinda bai gaskata ba. 

  Rayuwa irin ta Dr Ahmad madubi ce ga ɗaukacin al'ummar musulmi. 

  Shi mutum ne mai kyakkyawar fahimta ga lamurran addini, amma mai zafafawa wajen kare martaba irin ta Annabi Muhammad s.a.w

Mai kimanin shekaru 82 da haihuwa, wanda ya rasu ayau Jummu'a 7/1/2021, Marigayi Dr Ahmad Bamba ya shafe ɗaukacin rayuwar sa wajen nema da kuma bayar da sani. Ya shafe sama da shekaru 20 yana ɗaukar darasi a Madina, masallacin Annabi Muhammad s.a.w. Sannan ya fassara Littafin Muwaɗɗa wallafar Imamuna Maliku ɗan Anas daga harshen larabci zuwa harshen Hausa, baya da karantarwar sa ga manyan littattafai irin su Sahih Bukhari, Sahih Muslim, Sunnani Darimi, da makamantan su duk acikin harshen Hausa. Tabbas, rasuwar sa babbar asara ce ga kafatanin al'ummar musulmi musamman Hausawa.

  Ya zo a cikin littafin 'Al ilmu Huwal Imamu' na Shekh Ibrahim Nyasi cewa Hanyar aljanna ta na hannun mutane guda huɗu; Malami, da mai gudun duniya da mai ibada da kuma mai jihadi fi sabilillahi. Shi Malami idan ya kasance mai gaskiya ne cikin zuciyar sa, tabbas Allah zai azurta shi da Hikima. Duk kuwa wanda aka baiwa Hikima alal haƙiƙa an bashi gagarumar baiwa anan duniya da gobe lahira kamar yadda yadda yazo a cikin littafin Allah Alqurani.

  An tambayi Ɗan Mubarak cewa suwanene mutane?, sai yace 'Malamai', sai aka ce masa su wanene sarakuna? sai yace masu gudun duniya, sai akace su wanene kaskantattu?, sai yace masu cin duniya da addini. Don haka, ana iya cewa lallai malamai mutane ne masu daraja a cikin al'umma.

   Abdul-Aswad yana cewa babu wani abu wanda yafi Ilimi ɗaukaka. Sarakuna masu yin hukunci ne ga jama'a, yayin da Malamai ke yin hukunci a garesu.

AHNAF R.A yana cewa Malamai sun kusa kasancewa iyayen giji.. dukkan ɗaukakar da ba a ƙarfafe ta da ilimi ba, ƙarshen ta ƙasƙanci ce.

Annabi Muhammad s.a.w ya faɗa cewa "Malamai, sune magada Annabawa" (Tirmizi, Abu Dawood da Ibn Maja duknsun ruwaito shi)

Allah Ta'ala kuwa ya faɗa cewa "Iyaka dai masu jin tsoron Allah sune Malamai" (Suratul Fathi, 28).

  Babu buƙatar zafafa yabo ga marigayi Mallam Ahmad Bamba, domin shi ba mai son yabo ko kwarzantawa bane a zamanin ratuwar sa, amma shine wanda ya jaddada Sunnah a ƙasar Hausa bayan da ta ɗauko dusashewa, shi mutum ne wanda yake son Allah da Manzon sa, wanda yake tarbiyantar zukatan bayin Allah akan bautar Allah ta tsanin manzon sa Annabi Muhammad s.a.w da mayar da lamurra a gareshi, kuma mutum ne maras kwaɗayi, mai darrajanta ilimi da darrajanta kansa, gami da faɗar gaskiya walau ga shuwagabanni ko ga mabiyansu.

Allahu Akbar, shi mutum ne mai daraja a duniyar musulunci, tushen darajar sa kuwa bai wuce ga riƙon sa ga sunnar Annabi Muhammad s.a.w ba, da tsantsenin sa kai kace shine Imam Maliku bn Anas ko Imam Hasanul Basri. Hakika, rayuwar sa ta kasance abar koyi ga al'ummar musulmi.

  Wani sashen masana sun faɗa cewa An fifita Imam Hasanul Basri akan sauran Tabi'ai, saboda abubuwa guda 5;-

1. Baya umarni da aikata wani aiki face ya fara aikatawa.

2. Baya hanuwa ga barin wani aiki face ya fara hanuwa daga gareshi.

3. Duk wanda ya nemi wani abu daga abinda Allah ya hore masa zai bashi.

4. Ya kasance tana wadatuwa da ilimin sa ga barin neman wani abu a wajen mutane.

5. Ya kasance ciki da wajen sa duk ɗaya ne.

 Tabbas, duk waɗannan siffofi guda biyar sun tabbata ga Marigayi Shekh Ahmad Ibrahim Bamba. Gashi kuma ya samu cikawa irin tasa.. da fatan Allah ya rahamshe su duka amin.

Abdullah bin ‘Amr Ibnul ‘Ash ya ruwaito daga Annabi Muhammad s.a.w cewa "Lalle, Allah baya ɗauke ilimi daga hanawar sa ga bayin sa. Sai dai yana ɗauke ilimi ne daga mutuwar malamai ta yadda tsarkakan mutane zasu gushe, sai mutane su naɗa wawayen mutane a shugabanci. Sannan idan aka tambaye su, sai suyi magana ba da ilimi ba. Sai su taɓe kuma suyi asara.” ( Al-Bukhari da Muslim suka ruwaito).

    Kaicho da rashin babban masani Dr Ahmad Bamba, to amma ya kamata kowa ya sani wannan duniya ba abar dawwama bace. Tabbas, kowanne mai rai zai ɗanɗana mutuwa. Kuma tabbas, yadda Dr Ahmad ya koma ga mahaliccin sa, kowannen mu lokaci yake jira domin komawa zuwa ga Allah. Don haka ya kamata mu shagaltu wajen aiki da koyarwarsa, da neman ilimi, da bin Allah da kuma neman dacewar Allah da samun Aljanna.

  Dafatan Allah ya gafartawa Dr Ahmad Ibrahim Bamba, Allah ya tallafi bayan sa amin.

No comments:

Post a Comment