1. Allah sarki ne mai yawaita
Falala da tsari da kyauta
Bismillah zan karanta
Waƙar mafita da riba
2. Zamanin nan ya ƙazanta
Lamurra duk sun jirwanta
Ayyuka da halin mugunta
Ga cin amana bai tsaya ba.
3. Garkuwa don kuɗi da sata
Ga yawan fyaɗe da ƙeta
Ga rashin ladabin ƴammata
Duk ba zai mana mafita ba.
4. Tur da sauyi maras nagarta
Mai ɗorawa mutum kurumta
Ayyukan sharri ko mugunta
Mance Allah ba zai mana ƙa'ida ba
5. Son kuɗi duk ya tsananta
Burin kowa ya huta
Da kuɗi mata da mota
Babu cas, ko as dat ta'abba.
6. Shiyasa ayyukan mugunta
Munana, masu raba zumunta
Ayyuka na rashin aminta
Sun yawaita ba ma huta ba.
7. Ga uwa ta saida ɗanta
Ga uba ya haiƙewa ƴar ta
Ga ɗa yay fansa da wauta
Ya subhanallahi ka tsare mu gaba
8. Ran Hanan dai ya salwanta
Malaminta ya ha'inta
Ya aikata abin mugunta
Aikin sa gareshi babu riba
9. Aisha mai kasshe kanta
Wani jami'i shi yai lahanta
Cin zarafi mai muni na mata
A zamanin nan ana yi ba da ƙa'ida ba
10. Shugabanni da halin mugunta
An sa talaka yana ragaita
Daɗin haraji, tsada, duk an azabta
Janye tallafin mai ba abune mai kyau ba
11. Masu tsafi kun ƙazanta
Masu caca kuna da wauta
Luɗu da cin zali duk sun haramta
Wanda duk bai bi Allah ba ba zai zauna lafiya ba
12. Yau fasadi ya inganta
Mai bin shaiɗan zai kafirta
Ayyukan sa duk sun muzanta
Annabin Allah ya hane mu da cin riba
13. Masu shirka sun yawaita
Masu kiran haram saboda wauta
Ayyukan gaskiya ya ƙaranta
Lalle masifa a duniya ba ta gushe ba
14. A yau ƙarya itace mai tsafta
Wasu ma sun ƙware akanta
Samun kuɗin su shine mafitta
Ai kuwa hakan ba abune mai kyau ba
15. Aikin ƴan ta'adda ya ƙazanta
Zubar jini a yankin mu ya yawaita
Asalinsu akwai cin hanci da ƙeta
Jami'ai masu cin amana ƙarshensu ba zaiyi kyau ba
16. Ƴan siyasa ya kuke ta
Yaudarar talaka da sata
Kun hana arziƙi ya wadata
Kawunan ku kuke so ba talaka mai wahala ba
17. Ya kamata fa mu fahimta
Arziƙi ko da ya tsananta
Ko talauci in ya rabanta
Ga bawa ƙaddara ce wadda ba a guje ba
18. Tun gabannin yin halitta
Rabbuna Allah ya hukunta
Arziƙin ɗa, bawa ko jarrabta
Duk abinda mutum zai yi ba zai keta ƙa'ida ba
19. Yanzu menene mafitta?
Ga zukata sun firgitta
Rashin natsuwa ya yawaita
Duk abinda mutum zaiyi ba zai sake ba
20. Fahimtata a rayuwa ta
Sai mun sauya jigon nagarta
Sai mun rage raɗaɗen masu jinta
Sai muso juna da alheri banda gaba
21. Jama'ar mu akwai nagarta
A basu ilimi shi na fahimta
Zai kawar da talauci mai kanta
Duk mai aiki da hikima ba zai sha wuya ba
22. Ilimi mai sa nagarta
Mai gyara ayyuka da fahimta
Jahilci kuwa idan yayi kanta
Dole ayyukan jama'a ba zasuyi kyau ba
23. Tarbiyya ko mafi inganta
Turbar Islama binta
Ba fasadi babu cuta
Komai aka mayar ga Allah ba zai zama mai wuya ba
24. Ladabi abu mai kyau ga mata
Rufe tsiraicin su zusu kuɓuta
Bin iyaye da magabata
Barin fariya, yin ɗagawa abune ba mai kyau ga lahira ba
25. A koyar da yara jarumta
Aiki tuƙuru shine za a huta
Lalaci, sakaci ko sata
Ayyuka ne haramtattu da ba za a yisu da ƙa'ida ba.
26. Mu kalli Japan, Sin da Kolkata
Matasa na fafutika, kai hatta
Yara ƙananu da mata
Kowa nason ceton ƙasarsa ba cutar da ita ba
27. Neman halak abune mai tsafta
Mai gyara ƙasa da zukata
Idan zukata suka ladabta
Ayyukan bayi da dama ba zasu ƙetare ƙa'ida ba
28. Wajibi zalinci ya huta
Adalci shi ake buƙata
Tsayar da haddi ga masu gata
Matsawar kuɗi suka rinjayi adalci ba zamu zauna lafiya ba
29. Ya Allah ka bamu mafitta
Ya Rahmanu sarkin Nagarta
Ya man iza da aka fa ajibta
Ya Laɗiyfu ka yaye mana rashin aminci da gaba
30. Ni Sadiq Gwarzo na yawaita
Damuwa shiyasa na rubuta
Waƙar ina kewa da buƙata
Ina adduar samun tsira da rabo babba.
ALHAMDULLAHI
No comments:
Post a Comment