Sunday, 30 January 2022

MUYI KOKARIN KARE KAWUNAN MU DAGA RIBA

 MUYI ƘOƘARIN NESANTA KANMU DAGA RIYA, ƘARAMAR SHIRKA. 

   Allah Ta'ala ya umarci masu imani a cikin littafin sa Alqur'ani da cewa su bauta masa, kada kuma su haɗa wannan bauta da ta waninsa. Harma ya kira aikata haɗa bautar Sa maɗaukakin Sarki da ta wanin sa a matsayin zalunci wanda yake abu maigirma. 

  Annabi Muhammad (s.a.w) ya bayyana Riya a matsayin shirka wadda take ƙarama, wadda kuma Allah ba ya amsar aiki komai kyawunsa matsawar akwai ta a ciki.

 Malamai sun fassara riya a matsayin 'yin abu don neman yardar mutane, ba don neman yardar Allah ba'. 

   Shin yardar Allah muke nema ko ta murane a ayyukan da muke aikatawa? 

   Mallam Umar Sani fagge yayi tsokaci akan haka, inda yace "Idan kana so ka auna cewa akwai Riya acikin aiyukanka, to kayi duba acikin waɗannan abubuwan guda biyu;

   1. Na farko, Ibadar Ka.

Mallam yace, ka auna Sallar ka da sauran ibadun da kake yi duka, idan har ka samu cewa kana yin su da kyau acikin/gaban jama'a sama da yadda  kake yinsu kai kaɗai, haƙiƙa kana aikata Riya; ƙaramar shirka. 

Mallam Ya ce "Ba ibada kadai ba, hatta sadaka, kyauta da sauran ayyukan alheri, indai kana fifita yinsu akan idon jama'a don jama'ar suyi maka shaidar kai mai aikata aiyukan alheri ne, a bayan idonsu kuma ba ka yi, haƙiƙa kana aikata Riya. "

A ranar alqiyama kuma Allah zai tozartar da duk mai aikata Riya, Allah Ta'ala zaice masa 'kayi abu kaza da abu kaza don mutane suce kayi, kuma sun faɗa, don haka baka da lada a wurina'. Daga nan sai mala'iku su kifa fuskar mai aikata Riya da qasa, su jashi izuwa wutar jahannama. (Allah yayi mana tsari da ita).

  2. Abu Na biyu: Rayuwar ka

Mallam Umar Sani Fagge ya labarta mana wata ƙissa, inda  yace "watarana wani mutum yana yawo, yana sanye da riga mai tsada, wadda farashinta zai tasarwa dirhami arba'in, sai Sayyadina Umar(R.A.) ya kirashi yake tambayar sa nawa ne jalin kasuwancin sa da har yake sanya irin wannan tufafi? Sai wannan mutumi yace Jalinsa yakai misalin dirhami dubu daya. Sai kuwa Sayyadina Umar (R.A) ya dakeshi da sanda, sannan yace "Amma kake sanya irin wannan tufafi saboda Riya?" Akace ana cikin haka kuma sai ga Sayyadina Abdurrahman bn auf (R.A) yazo wajen yana sanye da tufafi wadanda darajarsu takai ta durhami dubu hudu (Mallam yace sama da miliyan dari kenan a yanzu), amma Sayyidina Umar bai ce masa komai ba."

 Sai Mallam ya cigaba da cewa "dalilin haka shine, wannan mutumi mai jarin durhami dubu, idan aka ƙyaleshi yana sanya tufa kurum na durhami arba'in, watarana sai ya karya jalinsa da kansa, domin yana yin abinda matsayinsa bai kai ba, yin hakan kuma nau'I ne na Riya. Shikuwa sahabi Abdurrahman bn auf, Allah ya bashi mamakon dukiya, yana da ikon sanya tufafi masu tsada ba tare da ya girgiza ba".

 Don haka Mallam yace, "duk wanda yake ƙuƙutawa ya sayi wani abu, ko yayi wani abu sama da matsayin da Allah ya ajiye shi don gama da nuna isa, wannan Riya ne, Allah ba yaso, idan mai aikata haka kuma bai tuba ba, zai gamu da fushin Allah a ranar alqiyama". 

  Lallai Riya babban lamari ne da ya kamata mu yi ƙoƙarin kare ayyukan mu da shi. Lallai Allah Ta'ala ne mafi kyautatuwar miƙa lamura da kuma neman yarda daga gareshi ba sauran mutane ba. 

  A sani cewa duk wanda Allah Ta'ala ya so, kuma ya ƙaunata, to Mala'ikun sa masu tsarki zasu ƙaunace shi, hakanan  al'umma zata ƙaunace shi kamar yadda yazo a cikin Hadisi.

  Dafatan Allah ya kiyaye mu daga dukkan wani nau'I na Shirka. Amin. 

#Sadiq Tukur Gwarzo

No comments:

Post a Comment