Wednesday, 30 September 2020

TARIHIN KANO

 ASALIN KANO

(Fassarar Tarihin asalin Kano kamar yadda ya fito daga tsohon kundi mai suna 'TARIYK ARBAB BALADIL LAZIY MUSAMMA KANO' watau 'KANO CHRONICLE' da turanci, wanda aka gutsura shi a littafin 'HAUSAWA DA MAKWABTAN SU' littafi na biyu' )

SADIQ TUKUR GWARZO

Littafin ya soma kamar haka:-

Wannan tarihi ne na ma'abotan wannan gari wanda ake kira Kano. Shugaban su shi ne Barbushe, shi kuwa daga ƙabilar Dala yake. Shi Dala mutum ne baƙi, kakkaura, ƙaƙƙarfa, mafarauci ƙwarai. Ya kasance ya kan kashe giwa da sandar sa, ya saɓo ta a kansa, yayi tafiya da ita kamar mil tara.

  Ya zo garin nan, ba a san asalin sa ba. Da zuwan sa sai ya gina gidansa a saman dutsen Dala, ya zauna akan sa, shi kaɗai tare da matan sa da ƴaƴansa bakwai, huɗu maza uku mata.

   Sunan babban ɗansa Gargaji, shine kakan Buzami. 

Buzami kuwa shine uban Barbushe. Shikuwa Barbushe, shine ya gaji dukkan halayen Dala tun daga sanin tsafi har zuwa ƙarfi da sihirinsa da rinjaye ga ƴanuwansa, domin haka sai ya zamo shugaba a zamanin sa.

  Ga sunayen fadawan Barbushe; 

-Gunzago: gidan sa yana a ƙarƙashin Gwauron dutse daga gabas.

- Gagiwa uban Rubu wanda yake kama giwa da igiya saboda tsabar ƙarfin sa.

-Gubanasu

-Ibrahimu

-Bardoje

-Nisau (wanda garin Panisau ya samu daga sunan sa)

- Kamfatau

- Duje

-Janberi

-Gamakora

-Safataro

-Hangugu

-Gardangi.

- Ɗan buru: wanda gidan sa yake a jigirya.

-Jan Damisa: wanda gidan sa yake a magwan. Sunan sa Ruma, kuma shine kakan Rumawa. Tun daga Guga har zuwa Salanta ana danganta su da shi, ana ce musu rumawa, su jama'a ne masu yawa.

- Hamɓarau: gidan sa yana Tanagar.

-Gunbarjado: gidan sa yana Panisau, kuma shi ɗa ne ga Nisau.

  A wancan zamani na Barbushe, mutane kan taso tun daga Tuda zuwa Ɗan-baƙoshi, haka kuma tun daga Duji har zuwa Ɗankwai, dukkan su suna taruwa a wurin Barbushe a daren salla biyu,  domin shine babban su cikin tsafi.

  Sunan inda gunkin su yake ajiye 'Kakuwa', sunan gunkin kuwa 'Tsumburbura', domin itaciya ce da ake ambatonta 'Shamus', sunan mutumin da yake zaune a ƙarƙashin ta dare da rana 'Mai Tsumbura'. 

  An kewaye itaciyar da gini ne, babu mai shiga cikin ginin sai Barbushe, duk kuwa wanda ya shiga sai ya mutu nan take.

  Barbushe kuwa baya saukowa daga saman dutsen Dala sai idan ranakun idi biyu sun gabato. A lokacin ne mutane ke zuwar masa da ga gabas da yamma, kudu da arewa, waɗansu da baƙar kaza, waɗansu da baƙin bunsuru.

  Idan sun gama taruwa a ƙarƙashin dutsen Dala a ranar jajibere kenan bayan la'asar, sai Barbushe ya fito daga gidansa da dare tare da makaɗansa. Ya na mai kururuwa da ƙarfi yana cewa "Babban jimina aka sa mun gama kara-gaga laya Tsumburbura"

  Mutane kuma sai su amsa masa da cewa "Ga Tsumburbura, Kanawa, ga wajen Dala".

   Daga nan sai su ɗunguma tare dashi zuwa saman tsauni wurin gunki. Da isar su gurin gunkin sai kowa ya yanka abin da yazo da shi.

   Sa'an nan sai Barbushe ya shiga cikin ginin shi kaɗai, yana mai cewa "Ni magajin Dala da kun ƙi da kun so ku bini ba ra'ayi ba"

  Su kuma mabiyan suna kewaye ginin da gunki Tsumburbura take tsirara suna masu cewa " Mai gida bisa kan dutse, Ubangijin Mama, bi mun bi ka ba ra'ayi", a haka zasu wakana har huduwor alfijir sa'annan su tsaya suci abinci.

  Daga nan sai Barbushe ya fito ya basu labarin dukkan abinda zai faru acikin shekarar da zasu shiga, har ma da baƙon da zai shigo ƙasar su na alheri ko na sharri.

  Shine ma ya basu labarin gushewar mulkin su, da sarewar itaciyar shamus da suke yiwa bauta har ma da ƙonewar ta, da kuma gina wani masallaci a jikin dutsen Dala.

  Kuma yace musu "Wani mutum zai zo wannan gari tare da rundunarsa, ya mallakemu". 

Sai suka ce masa "Don me ka faɗi haka? wannan magana ce fa mummuna".

  Sai yayi shiru, sannan yace "da sannu zaku ganshi da alfarmar Tsumburbura! idan bai zo a zamanin ku ba, zai zo a zamanin ƴaƴanku, ya mallaki dukkan wanda ya samu a cikin wannan ƙasa dukkan ta, ya sa a manta daku duk da jama'ar ku, zai bayyana da ƙabilar sa zamani mai tsawo".

  Jama'ar Barbushe suka yi baƙin ciki ƙwarrai, suka gaskata abinda ya faɗa domin sun san baya musu ƙarya. Har ma suka ce "yaya za muyi mu kawad da wannan lamari?"

  Sai yace dasu " Babu yadda za ku yi sai haƙuri!".

   A haka suka wanzu cikin nadama bisa gushewar da mulkin su zaiyi mai tsawo har sa'ar da Bagauda yazo kano tare da runduna tasa a zamanin ƴaƴan waɗancan mutane na lokacin Barbushe, (amma wasu sunce zamanin jikoki ne), bai samu kowa ba daga makusantan Barbushe sai Janberi, da Hamɓarau, da Gardangi, da Jandamisa, da Kamfatau.

  Da waɗannan mutanen suka ga lamarin Bagauda sai suka ce "wannan mutumin shine wanda Barbushe ya bamu labari".

  Jamberi yace " Na rantse da Tsumburbura idan aka bar su a cikin wannan ƙasa, da sannu zasu mallake mu har mu zama kamar ba kome ba".

Mutane suka ƙi jin maganar sa, suka bar su suka zauna, suka ce "A ina Bagauda zai samu ƙarfin da zai rinjaye mu?"

     Bagauda ya zauna da rundunar sa a Gazarzawa, suka gina gidaje a cikin ta, suka zauna watanni bakwai, sannan suka tafi Sheme.

  A wancan zamani, daga Jakara zuwa Damargu, ana giran sa da suna Gazarzawa. 

  Daga Jakara zuwa Santolo, ana kiran sa da suna Zadawa.

  Daga Santolo zuwa Barku, sunan sa Fankui.

  Daga Bampai zuwa Wasai ana kiran sa da Raura.

  Daga Watari zuwa dutsin karya sunan sa Dundunzuru.

  Daga Santolo zuwa shike sunan sa Sheriye.

 Daga Damargu zuwa Kazaure sunan sa Sheme.

Daga Barku zuwa Kara sunan sa Gauɗe.

Daga Kara zuwa Amnago shine Gaji.

Sai kuma daga Mashi zuwa Ringim da ake kira Tokawa.

  Ma'abotan wannan ƙasa wanda Bagauda ya same su a cikinta suna mulkin garinsu, ba su bin kowa sai Tsumburbura da duhuwar sa Jakara.

Ana ambaton ta (jakara) da suna Kurmin baƙin ruwa, domin shi ruwa ne baƙi, duhuwa ta kewaye shi, ana kiyaye dukkan musiba da ita da gunkin su. Ta faro ne tun daga Gurgumasa har zuwa Dausara.

  Ƙiraranta da zartakenta basa yin motsi har sai idan musiba ta gabato garin kano, sai aji tayi kururuwa sau uku, hayaƙi ya rinƙa fitowa daga cikin Tsumburbura, wanda ke cikin tsakiyar ruwa. 

Daga nan sai su nemi baƙin kare su yanka a ƙarƙashin Tsumburbura, kuma su yanka baƙin bunsuru a cikin duhuwar.

  Idan har hayaƙin da kururuwar suka ƙaru to tabbas sai wannan musibar ta sadu dasu, idan kuwa basu daɗu ba to musibar ta kau kenan. Sunan wannan duhuwar 'Madama', kuma sunan Tsumburbura Randaya.

  Ga sunayen waɗanda suka soma riƙe sarautar kano tun a zamanin farko:-

- Mazauda, shine babbansu, shine kuma kakan sarkin Makafi.

- Giji-giji shine sarkin Maƙera.

- Bugazau sarautar sa dafa giya.

- Hamburki sarkin magani kenan mai warkar da dukkan cututtuka.

- Ɗan ɓuntiya shine mai yawan tafiya cikin garuruwa da daddare, shine kakan kurmawa (sarautar kama masu laifi kenan) 

- Doron-maje shine sarkin Samari.

- Jandodo shine sarkin makaɗan gunduwa da kuru.

-Magaji shine kakan Maguzawa, shine mai fitar da ƙarfe daga ƙasa ya narka shi.

- Asanne shine kakan mawaƙa, shine sarkin Rawa.

- Bakwanyaƙi shine sarkin Maharba.

- Awar shine kakan Awarawa, shine mai yin gishirin Awar, kuma sarkin Ruwan dukkan ƙasar.

Dukkan waɗannan su goma sha ɗaya, kowannen su yana da ƙabila tasa  daban da jama'a mabiyan sa masu yawa, kuma dukkan su sune asalin KANO..

TARIHIN GARIN GWARZO

 TARIHIN SAMUWAR K'ASAR GWARZO


Gabatarwa


Littafin 'Mazan Kwarrai' shine wanda Marubuci IBRAHIM BALA GWARZO ya k'addamar dashi a wajajen shekara ta 2000, wanda ya tattaro tarihin kafuwar garuruwa kimanin talatin da suke a tsohuwar K'asar Gwarzo. Bisa bukatuwar wannan tarihi da muke dashi, kuma bisa bukatar yad'a Ilimi, yasa na nemi (Sadiq Tukur Gwarzo) sahalewar Marubucin (wanda yake Uba gareni) domin rubuta wani yanki gami da yadashi ga al'umma. Hakika marubucin yaji dadin haka, ya kuma sahale min izinin yin hakan. Godiya da fatan alheri a gareshi. 


TARIHIN SAMUWAR GARIN GWARZO


Kamar yadda tarihi ya nuna mana, akasarin garuruwan Kano Maguzawa ne suka Kafasu. Wannan gari na Gwarzo mai tsohon tarihi ya samu kafuwa ta hannun wani Bamaguje wanda ake kira 'GWARZO'. 

A zamanin da, zakaga mutum ya samu guri ya kafa gida shi kadai, wanda daga baya idan mutane suka fuskanci wurin yana da yalwa sai kaga suna zuwa da kadan_da_kadan domin zama. 

Ga al'adar mutanen da, wanda ya fara zuwa guri ya kafa gari shine sarkin garin. 

Bayan wannan Bamaguje mai suna Gwarzo (wanda akace yazo ne daga arewa a wuraren K'arni na Sha shidda zuwa na sha Bakwai) Ya kafa 'yan tsangayunsa ya zauna a wannan guri, sai wani Malami yazo daga kasar Sakkwato wanda ake kira Malam Rashidu ya sauka a gurin shima. Sai Mallam Rashidu ya shiga rokon Allah subhanahu wata'ala ya albarkaci wannan guri da suke zaune, ya kuma kareshi. Ai kuwa hakan ya samu, domin har lokacin yake-yake yayi k'aura ba'a taba cin k'asar Gwarzo da yaki ba. 

Bayan wani lokaci sai wani mutum da ake kira Isau yazo shima ya kafa bukkarsa ya zauna tare da Bamaguje Gwarzo da kuma Mallam Rashidu. Suna nan zaune abinsu sai ga wani Bamaguje ya risko wajen, sunan sa Kutunku, amma anfi kiransa da Riji. 

Ganin haka sai Bamaguje Gwarzo yayi murna, ya samu danuwa. Wannan yasa yayi tunanin raba wannan wuri da suke zaune biyu b'angaren gabas da yamma masu kudu, sannan ya baiwa Bamaguje Riji mulkin barin gabas, shikuma yaci gaba da mulkin b'angarensa. Sai ya kasance duk bak'on da yazo ya zauna a b'angaren yamma maso kudu (wanda daga bisani ake kiran wurin da suna Gwarzo), to ya zama talakan Gwarzo, wanda kuma ya zauna a barin gabas (shima daga bisani Riji ake kiran wurin), Riji ne shugabansa. 

A iya wannan lokaci, mutane sun rinka zuwa suna zama a wannan yanki. Akwai misalin wani hab'en mutum mai suna Katamba, wanda Gwarzo ya bashi wuri a inda ake kira Katambawa a yanzu, sannan da misalin wasu mutane da suma suka zo shigewa suka nemi a basu matsuguni, sai Gwarzo ya basu wani wuri a gabas dashi, inda a yanzu ake kira da Tsohon Garu. A wancan lokaci, ba iya wurin da mutum zaiyi gida kadai ake baiwa bako ba, A'a, ana bashi ne har ma da inda zai noma domin ya ciyar da kansa da kuma iyalinsa. 

A kwana-a-tashi, sai Allah ya kawo wani dan-fulani mai suna Baba. Daya zo sai ya sauka a yankin da Gwarzo yake iko dashi. Shikuwa wannan bafullatani ance yazo ne daga Musawa ta k'asar Katsina, kiwon shanu da dabbobi itace sana'ar sa. 

Ance wata rana sai dabbobin Bafullatani Baba suka shiga cikin gonar wani Bamaguje mai suna Rijau tare da tafka masa b'arnar amfanin gona, wannan yasa ya kai k'ara ga Sarkin wurin watau Gwarzo. Da aka kira Baba dan fulani sai aka tsareshi sai daya biya kimanin b'arnar da dabbobinsa sukayi, sannan aka yanka masa tara ya biya. 

Ganin haka sai wannan bafullatani Baba ya sayar da dabbobinsa ya k'ulle kudinsa ya tafi kano wajen d'an iyan Kano domin lokacin shine mai kula da yammacin kano, inda ya nemi sarautar Gwarzo, wadda akewa lak'abi da 'd'an Gwarzo'. Sai kuwa yayi dace aka bashi. Aka tanaji dawakai daga kano bayan nad'insa, aka rakoshi zuwa garin Gwarzo ana kad'e-kad'e da bushe-bushe. 

Koda Bamaguje Gwarzo, wanda yake sarkin Gwarzo (d'an Gwarzo mai ci) yaji kade-kade da bushe-bushe, sai ya aika aje a gano masa menene ke faruwa. Inda aka zo aka sanar masa cewa bafullatanin nan Baba da aka yiwa tara aka nad'o daga kano a matsayin sabon d'an Gwarzo. Jin haka keda wuya sai Bamaguje Gwarzo da Mallam Rashidu suka shiga gidajen su, tun daga nan ba a sake jin ɗuriyar su ba.

Friday, 4 September 2020

YADDA AKE KITSO A KASAR HAUSA A ZAMANIN DA

 YADDA AKE YIWA MATA KITSONA ZAMANIN BAYA

Yazo a cikin littafin 'Labarun da dana yanzu', babin farko mai suna 'Labarin sana'o'in Hausa' cewa :- Idan mace za tayi kitso (a zamanin da), sai ta nemi rama, da mai, da shuni.

   Sa'an nan sai ta tafi gidan makitsiya, ta ba ta tsinke ta kwance kanta, watau ta tsefe gashin ta ya tashi. San nan sai ta kwanta rub da ciki a gaban makitsiya. Makitsiya zata sharce gashi da tsinkenta ta rarraba shi kashi-kashi; wajen doka daga tsakiyar kai, wajen kaikainu daga sashen kai, kai-kainiya ta dama data hagu, da wajen ɗan ƙeya daga can wajen ƙeya.

  Idan ta gama karkasa kan haka, sai ta shafe shi da man shanu, sai kuma ta soma kitse wajen kaikainu, sannan ta kitse wajen ɗan keya. San nan sai ta faɗa tsakar ka, ta sanya doka (wani tsumma ne ko kaɗi da ake nannaɗewa da zare sai a cusa) sai a kitse duka, tana mai sanya rama tare da gashin. 

  Daga nan sai ayi fishi ko roriya; watau abi sauran ƙananun gashin gefen kaikainu dana tsakankanin kaikainu dana doka a gama da rama a kitse, duka da ƙayar bushiya ake tattara gasun nan. 

  Daga nan kuma sai a kawo mai a labta ga kan, sa'annan a kuma shafe shi da shuni. 

  Kitso ba doka akan ce masa 'juye', kitso wanda aka jera ƙananan kaikainu a tsakar kai har ga ƙeya maimakon doka ana ce masa 'kumbuche'. Kitso mai ɗan ƙeyi biyu ana ce masa 'mace-da-goyo'. Akwai kitso mai suna 'barikanchi' wanda ake yinsa yayi tuk-kaye. Bayan waɗannan, akwai kitson Yorubawa da kitson fulani da ake ce masa 'bijaji'. 

Saturday, 22 August 2020

ILIMIN SANIN RUBUTACCIYAR WAƘA

 ILIMIN SANIN RUBUTACCIYAR WAƘA

  Ita dai rubutacciyar waƙar hausa ta samu tasiri ne daga waƙoƙin larabci, domin kuwa ba a san ta ba sai da musulunci da ilimin larabci suka shigo ƙasar nan, watau musamman lokacin jihadin Shehu Usmanu.

   Tun daga nan har zuwa yau, idan aka bincika marubuta waƙoƙin hausa za a tarar ba zasu rasa wani tasiri na harshen larabci ko addinin musulunci ba.

   Wani abin ban sha'awa kuma shine, harshen Hausa harshe ne mai iya karɓar kowanne irin salo da harshen larabci yazo dashi, ya zauna daram kamar dama anan aka halicce shi.

   Bugu da ƙari, ma'aunin waƙar hausa rubutacciya da amsa amon ta duka irin na waƙoƙin larabawa ne, sai fa daga bisani ne mawaƙan hausa suka saɓa da irin waƙoƙin larabci, har ma aka samu sabbin jigogi waɗanda suka shafi lamuran yau da kullum.

    Abubuwan da ake sa rai aga sun tabbata kafin a hukunta cewa rubutacciyar waƙar hausa tayi yadda ake sonta guda 9 ne, amma na ƙarhen bai zama tilas ba. 

Ga abubuwan kamar haka:-

1. Buɗewa da rufewa da yabon Ubangiji da Salatin Annabi (S.A.W).

 Misali: Na fara da sunan Zuljalali maƙagin duniya,

   Ina salati ga Khairul Anami hasken idaniya.

2. Ma'auni; ta yadda za a iya yanyanke ta kuma baitocinta su zamo kai-da-kai.

  Misali: 

*Dawil:

 Mutum haka ma in yaga bashi da ko zare,

Ya kan roƙi Allah safe da daddare.

*Madid:

Ko ina, duk an sani kai ka mulki,

Duk ƙasar nan babu mai arziƙin ka.

*Da sauran su; kamar su Basiɗ, Watir, Kamil, Hazaj, Rajaz, Ramal, Mumsarih, Hafit, Muƙtabib, Mutaƙarrab, Muɗarid.

3. Waƙa ta kasance tana amsa amo, tana kuma da ƙafiya.

4. A shirya baitocin waƙa dai-dai da ɗangogin waƙa guda bakwai.

   Misali: Gwauruwa itace mai baiti ɗango ɗaya.

Ƴar tagwai mai ɗango biyu,

Ƴar uku mai uku,

Ƴar huɗu mai guda huɗu,

Ƴar biyar mai biyar,

Tahamsi mai shidda,

Sai Tarbi'i mai guda bakwai.

5. Ambaton jigon waƙa tun daga farkon ta.

  Misali: "Nayi shiri tsaf zan ja hankali,

                Akan mata masu yawon dandali".

6. Warwarar jigon waƙa

Watau a kawo ɗangogi waɗanda suka tafi dai-dai da jigon da ake waƙar akan sa.

7. Ambaton sunan mawaƙi da tarihin yin waƙar a ƙarshen ta.

8. Salon mawaƙin ya kasance yana da ƙarfi, watau yana yin bayani mai gamsarwa.

9. Gwanin ta da iya sarrafa harshe.

Sadiq Tukur Gwarzo ya ciro wannan bayanin daga littafin 'WAƘA A BAKIN MAI ITA' wanda kamfanim ɗab'i na NNPC ya wallafa a shekarar 1979.


Monday, 13 July 2020

ƘABILAR MAASAI: DALILIN SHAN JINI DA KIWON SHANU

ƘABILAR MAASAI: DALILIN SHAN JINI DA KIWON SHANU
Sadiq Tukur Gwarzo, GGA
Maasinta,  shine ake ɗauka Uba kuma wanda ya samar da tsatson ƙabilar Maasai, ance ya samu kyautar shanu ne daga Ngai – Ubangijin sama- wanda ya sauko da shanun daga sama zuwa ƙasa acikin salkar fata.
  Tun daga wannan lokacin suke kallon shanu a matsayin tsarkakku,  kuma darajar su tana kaiwa kafaɗa da kafaɗa data ƴaƴansu. Hakika yawan yara da yawan shanu ke nuni da tumbatsar mutumin ƙabilar Maasai.
Dajin da ya ratsa shahararrun yankunan Ngorongoro, Amboseli, Serengeti, Masai Mara da Tsavo dukkan su nan ne wuraren kiwon alummar Maasai. Kabilar Maasai na amfani da yaren Maa ne, kuma ana samun su a yankunan kasashen Kenya da Tanzania.
Haka Kuma duk da yadda sauyin zamani ke tunkuɗe al'adu ga ƙabilun duniya, amma kabilar Maasai suna yaƙi tukuru wajen kere al'adun su na kaka da kakanni, don haka suka yi shura a cikin ƙabilun kudancin afirka musamman wajen kiwon shanun su, tafiya bisa tituna ko rawar adumu.
Daga cikin shahararrun al'adun gargajiya na ƙabilar Maasai akwai rawar tsalle ta adumu, sanya tufar 'shuka' mai kaloli, da yin kaki ko kuma kwankwaɗar jini.
Adamu shine sunan rawar tsalle-tsalle da akeyi a matsayin biki yayin da yara matasa suka zama mahankalta waɗanda suka isa aure. Ana rera wakoki  nangargajiya yayin bikin, sannan wanda tsallen sa yafi na kowa shine yayi nasara, kuma shi ke samun macen aure da tafi ta saura.
Kalar tufafin shuka da suka fi sanyawa itace Ja, wadda take wakiltar jini, kuma take a matsayin kariya a garesu ga namun daji. Yayin da shuɗiya ke nufin sararin sama wadda ke samar da ruwan sama ga shanu. Kalar rawaya kuwa na nufin haihuwa da girma. Baki ɗayan waɗannan tufafi na su ke ƙara musu keɓantaka a cikin ƙabilun afirka.
Kasancewar a cikin wasu ƙabilun ana ƙyamar kaki, amma a Maasai shi abin so ne, domin babban abin girmamawa ne idan zaka gaisa da mutumin da kake girmamawa sai kayi kaki ka tofa a tafin hannu sannan ka miƙa masa hannun ku gaisa. Hakan na nufin share dukkan wani sharri daga tafin hannun, haka kuma idan kaje barka sai ka tofa kakin ka a goshin yaron sannan ka nuna soyayyar ka a gare shi. Shan jini kuwa wani abu ne da ya zama ruwan dare a garesu.
 Don haka alummar ƙabilar Maasai na shan jini ne a matsayin sinadarin ƙara lafiya da kuzari. Jinin da suka fi sha kuwa shine na saniya, wanda har sukan gauraya shi da madara su kwankwaɗa abinsu a duk sanda suke so.
   Zuwa yanzu kabilar ta rarrabu zuwa 21 kamar haka, kuma kowacce na da ɗan sirkin al'adu da saura:- Keekonyokie, Damat, Purko, Wuasinkishu, Siria, Laitayiok, Loitai, Kisonko, Matapato, Dalalekutuk, Loodokolani, Kaputiei, Moitanik, Ilkirasha, Samburu, Lchamus, Laikipia, Loitokitoki, Larusa, Salei, Sirinket and Parakuyo

Sunday, 5 July 2020



AL'ADA MAI BAN MAMAKI:  DALILIN RASHIN WANKA A KABILAR HIMBA 
Sadiq Tukur Gwarzo, GGA
08060869978
  Kabilar Himba da ke kasar Namibia rukunin wasu kaɗaitattun mutane ne waɗanda ɗabi'an su suka zamo bare, ko ace ababen mamaki ga sauran mutanen duniya.
 Akan kira su da suna Ovahimba ko Omhimba, suna rayuwa ne a yankin Kunene cikin kasar Namibia.
Daga cikin al'adun su da suka sha banban da mafi yawan sauran al'adu, akwai al'adar su ta tarbar baƙo da mata domin yin jima'i da su, da kuma sanyawa jarirai tsakiya a wuya tun suna zanin goyo. 
 Sannan basu cika cuɗeɗeniya da sauran kabilu ba balle har a samu sauyin al'adun da suka yi gado kaka da kakanni, waɗannan mutanen suna matukar kokari wajen ganin basu yi aron wata baƙuwar al'ada ba komai kyawunta, don haka muna iya cewa mafi yawan ababen da suka yi riko tun na kaka da kakanni ne.  
Sana'o'in da mazajen kabilar suka fi riko dasu  sune kiwo da noma, matan su kuwa sunfi damuwa da shiga daji samo itacen hura wuta don girka abinci da kuma jigilar samar da ruwan sha ga ahalin su.
  Suna bauta ne ga allolin iyayen su, sannan mazaje na auren mace sama da ɗaya, suna kuma yiwa yara mata aure tun da kuruciyar su.
Babban abin mamaki dangane dasu shine rashin yin wanka da ruwa. Yana daga al'adar da suka yi gado ta rashin wanka da ruwa kwata-kwata a rayuwar su, dalilin haka kuwa ance baya rasa nasaba da rashin kyawun yanayin yankin da suke raye. Yankin su ya shafi sahara ne, samun ruwa na da matukar wahala a tattare dasu. Don haka darajar sa ya sanya suke ganin tamkar asara ne a kwarar dashi wajen wanke gangar jiki.
  Sai dai kuma hakan bai sanya sun zama ƙazamai munana ba, ta yadda suka bullo da wata dabara wajen tsaftace jikin su wajen amfani da albarkatun dake zube a yankin nasu.
   Dabarun sune;  goge jikkunnan su da wata irin kuɓewa ja dake fito musu, sai kuma yin sirace a kullum don tsaftace jikkunan su.
   Yadda suke siracen shine, ana zuba garwashi a rufaffen mazubi mai cike da garin magani da kofa a sama, don haka da zarar hayaki ya soma tashi sai mutum ya durƙusa yana mai kara jikin sa ga tururin wanda zai rinƙa shiga sassa daban daban na jikin yana tsaftace shi. 
Ƙabilar Himba na da matukar son baƙo, tare da kyautata masa, amma fa basa bari baƙuwar al'ada ta gauraya da tasu.

Saturday, 30 May 2020

LABARIN DAN SANDAN CIKI NA INGILA

LABARIN WANI FASIHIN ƊAN SANDAN CIKI WANDA YA CIRI TUTA A YAƘIN DUNIYA NA BIYU

  Daga littafin Hikayoyin Kaifafa Zukata wallafar Marigayi Mallam Aminu Kano.

 A zamanin yaƙin duniya na biyu, anyi abubuwan bajinta, ƙwazo da ƙuru marasa iyaka. Irin waɗannan abubuwa ya kyautu yara su sani don gaba. Saboda haka ne zamu ba da labarin bajinta, ƙwazo da basirar wani ɗan sandan ciki na Ingila.
  Lokacin da jamus suka cinye ƙasar sa suka mamaye ƙasar Turai, sai ya zamana aika saƙon hannu zuwa ga Rashawa abu ne marar yiwo domin duk hanyar da za a ratsa zuwa Rasha Jamusawa suna nan sun kuma sanya ido su ga wani baƙon abu.
Ƙasar Ingila na son aikawa da saƙon hannu zuwa ga kwamandan yaƙi na Rasha, amma kafin aje sai an bi ta ƙasar Faransa, an ƙetare Switzerland an ɓulla ta Yugoslavia kafin a tarar da Rashawa.
Akan haka sai hedikwatar ƴan sandan ciki ta Ingila ta zaɓi wani gwarzo a cikin jami'anta. Ranar da zai tashi sai shugaban hedikwatar ya kira shi yace da shi, "Gwamnati ta zaɓe ka ka kai saƙo wurin Marshal Timoshenko. Za a sanya ka a jirgin sama mai laima a kai ka kusa da Faris a jefa ka. Za ka sauka a wani daji mil goma daga Faris da ƙarfe ɗaya na dare. Da zarar ka sauka in ka duba na'urar gane kusurwa 'kanfas' ka ga gabas, sai kayi ta tafiya har zuwa yadi ɗari ko fin haka da kaɗan, a hagun ka zaka tarar da tsohon basukur. Akwai fitilar kalanzir ka kunna ka tura har kazo babbar hanya. Daga nan ka bi hanyar zuwa otal mai suna Edward Set. Ka jingine basukur ɗin ka shiga dai-dai ƙarfe biyu saura kwata. Idan ka kuskure abu ɗaya zaka shiga halaka.
Da zarar ka shiga, wanda yake aiki a lokacin zai kunna taba sigari da zarar ya ganka. Daga nan zai baka ɗaki. Bayan ƙarfe uku da kwata ka fito daga ɗakinka ka je cikin lambun otal ɗin kana shawagi. Wani mutum zai zo da jarida a hammatar sa ya zauna a kujera mai fitila. Bayan yayi karatu zai bar jaridar a nan ya tafi nasa zarafi. Kai sai ka ɗauki wannan jaridar kaje ɗakin ka ka duba shafin talla. Anan za ka ga abinda za ka yi. A dawo lafiya, Allah ya kiyaye. Kada ka mance da cewa sirrin aikin ƴan sandan ciki shine aiki da hankali".
Nan da nan aka ɗauki ɗan sandan, aka ya dashi a gefen Faris, ya tarar da komai yadda aka gaya masa, ya kuma yi duk abin da aka ce yayi.
Da ya duba shafin talla ya fassara saƙon dake ciki, sai ya ga ance dashi nan take ya je ƙofar otal zai tarar da mota sabuwa mai lamba kaza, a cikin ta akwai ƙatuwar jaka cike da kuɗin Ingila fam dubu ashirin. A cikin su guda ɗaya ce tak ke ɗauke da saƙon da ake so Marshal Timoshenko na Rasha ya samu.
Nan take ya fito da gaggawa, ya ɗauki mota ya kama hanya. Ya yi kamar awa ɗaya yana tafiya har ya zo wata kwana, sai ya ga mutum a kwance jina-jina. Ya ja birki don kada ya taka shi. Kuma ya tabbata an kaɗe shine aka bar gawar sa anan. Sai kawai ta fito ya kama ƙafar sa don ya janye shi ya samu hanya.
Ai kuwa sai wuf yaga mutumi ya miƙe ya zaro labarbar, ya auna shi da ita, sannan yace "Ni ɗan sandan ciki ne na Jamus. Sunan ka Robinson. Yau ka sauka daga Ingila. A motar ka akwai saƙo zuwa Marshal Timoshenko. Yanzu ba wata magana sai ka ba ni mota da kayan cikin ta ko in kashe ka".
Nan da nan ta ya sakar masa mota. Ya shige kenan zai tashe ta sai Robinson yace da shi, "Ina so ka taimake ni da abu guda". Wato zan buɗe hannayen kwat ɗita ka harba wurare daban daban don in koma gida a sani sai da tsiya tsiya aka karɓi kayan nan. In ba haka ba sai a zaci ƙarya nake".
Ɗan sandan cikin Jamus ya yi masa yadda yace. Daga gamawa sai Robinson ya zaro tasa labarbar ɗin yace "Harsashin ka ya ƙare, bani motata. Amma ni ba zan yi wauta in bar ka a raye ba". Sai ji ka ke fa! fa! fa! fa! ya harbe shi.
Ɗansandan Jamus ya mutu, Robinson ya shiga motar sa ya kai saƙo inda aka tura shi ko tsartse bai yi ba.

Sadiq Tukur Gwarzo