TARIHIN ƘASAR BAUCHI
SADIQ TUKUR GWARZO
Kashi na biyar
A lokacin da rundunoni biyu suka fuskanci juna, watau rundunar Sarkin Bauchi Yakubu da ta Mayaƙi Kalumba, sai kowannen su ya buga tambarinsa, mayaƙa suka faɗawa juna da sara da suka, ƙura ta turnuƙe sama, sama ta cika da hayaƙi, yaƙi yayi zafi, ya huru, rana ta zama misalin dare, ba a jin kome sai ƙarar ƙarfe da tsarkiyar baka.
Sannu a hankali sai duhu ya ƙara duhu, har ya zama abokin gaba baya ganin wanin sa. Sai Sarkin Bauchi yakubu ya baiwa jama'ar sa umarnin suyi ta harbin duhun har sai da duhun ya yaye aka ga Kalumba ya gudu, taron sa kuma ya watse, ya bar tambarinsa da tutarsa da laimar sa da tarkacensa da dukkan wani abu da yake mai nauyi anan suka bar shi suka gudu.
Daga nan sai Yakubu ya tatttara kayayyakin na su ya aike da su wurin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, sannan ya koma gida Bauchi cikin farin ciki saboda taimakon da Allah Ta'ala yayi gare shi.
Bayan wannan sai Yakubu ya sake tashin yaƙi zuwa Misau, ya yaƙe su, ya zauna a ƙofar garin su kwana talatin, ya hana su fita har sai da yunwa ta tsananta garesu ya zama suna cin dawakai da jakuna da sauran ababen dake hannunsu.
Da abin yayi tsanani sai suka watse, Yakubu ya kama na kamawa saura kuma suka ɗai-ɗaice a duniya, suka bar birnin su wofi babu kowa.
Yakubu ya koma gida ɗauke da ganima mai yawa, ya zauna tsawon wasu shekaru a gida, sannan ya tashi da yaƙi zuwa Tsaure, shikuwa gari ne a arewacin Bauchi, ya iske su suna sauraron sa, alhali bai san sunyi dakon zuwan sa ba, har sai da ya zo kan kan kan da su, sannan suka faɗa masa da yaƙi, ya yaƙe su da yaƙi mai tsanani har sai da ya kore su, ya kashe na kashewa, saura suka gudu suka bar gidajensu, shi kuwa ya ƙone gidajen sannan ya koma Bauchi tare da jama'ar sa
Bayan wannan sai ya ƙara yin shirin yaƙi zuwa Tufi, nan ma ya same su sun taru a bakin babban dutsen su, ya hau su da yaƙi. Amma sai da yayi yaƙi dasu tsawon shekaru biyar sannan yaci galaba akansu.
Wannan kuwa shine ƙarshen yaƙe yaƙen Sarkin Bauchi na farko Yakubu, domin daga shi bai sake fita yaƙi ba Allah yayi masa rasuwa. Dafatan Allah ya jiƙansa amin
SADIQ TUKUR GWARZO
Kashi na biyar
A lokacin da rundunoni biyu suka fuskanci juna, watau rundunar Sarkin Bauchi Yakubu da ta Mayaƙi Kalumba, sai kowannen su ya buga tambarinsa, mayaƙa suka faɗawa juna da sara da suka, ƙura ta turnuƙe sama, sama ta cika da hayaƙi, yaƙi yayi zafi, ya huru, rana ta zama misalin dare, ba a jin kome sai ƙarar ƙarfe da tsarkiyar baka.
Sannu a hankali sai duhu ya ƙara duhu, har ya zama abokin gaba baya ganin wanin sa. Sai Sarkin Bauchi yakubu ya baiwa jama'ar sa umarnin suyi ta harbin duhun har sai da duhun ya yaye aka ga Kalumba ya gudu, taron sa kuma ya watse, ya bar tambarinsa da tutarsa da laimar sa da tarkacensa da dukkan wani abu da yake mai nauyi anan suka bar shi suka gudu.
Daga nan sai Yakubu ya tatttara kayayyakin na su ya aike da su wurin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, sannan ya koma gida Bauchi cikin farin ciki saboda taimakon da Allah Ta'ala yayi gare shi.
Bayan wannan sai Yakubu ya sake tashin yaƙi zuwa Misau, ya yaƙe su, ya zauna a ƙofar garin su kwana talatin, ya hana su fita har sai da yunwa ta tsananta garesu ya zama suna cin dawakai da jakuna da sauran ababen dake hannunsu.
Da abin yayi tsanani sai suka watse, Yakubu ya kama na kamawa saura kuma suka ɗai-ɗaice a duniya, suka bar birnin su wofi babu kowa.
Yakubu ya koma gida ɗauke da ganima mai yawa, ya zauna tsawon wasu shekaru a gida, sannan ya tashi da yaƙi zuwa Tsaure, shikuwa gari ne a arewacin Bauchi, ya iske su suna sauraron sa, alhali bai san sunyi dakon zuwan sa ba, har sai da ya zo kan kan kan da su, sannan suka faɗa masa da yaƙi, ya yaƙe su da yaƙi mai tsanani har sai da ya kore su, ya kashe na kashewa, saura suka gudu suka bar gidajensu, shi kuwa ya ƙone gidajen sannan ya koma Bauchi tare da jama'ar sa
Bayan wannan sai ya ƙara yin shirin yaƙi zuwa Tufi, nan ma ya same su sun taru a bakin babban dutsen su, ya hau su da yaƙi. Amma sai da yayi yaƙi dasu tsawon shekaru biyar sannan yaci galaba akansu.
Wannan kuwa shine ƙarshen yaƙe yaƙen Sarkin Bauchi na farko Yakubu, domin daga shi bai sake fita yaƙi ba Allah yayi masa rasuwa. Dafatan Allah ya jiƙansa amin
No comments:
Post a Comment