Wednesday, 24 February 2021

Hikayar Sagardatta, Ɗa ga wani Ɗankasuwa

 Hikayar Sagardatta, Ɗa ga wani Ɗankasuwa 


Daga littafin Khalila wa Dhimna, wanda Vishnu Sharma ya rubuta shekaru sama da dubu biyu da suka gabata (300 BC) domin koyar da mabiyan sa sirrikan zaman duniya.


Sadiq Tukur Gwarzo


Sadaukarwa gareku don neman albarkar ku bisa murnar raɗin sunan yaron waje na Muhammad Tukur wanda akayi ayau Laraba 23/2/2021.

Sagardatta shine sunan wani kyakkyawan matashi, ɗa ga wani ɗan kasuwa da aka taɓayi a wani daga garuruwan tsohuwar daular Hindu.

  Wata rana, sai wannan ɗan kasuwa ya samu labarin cewa ɗansa Sagardatta ya siyi wani littafi mai tsada sosai, wanda saɗara ɗaya ce tal a cikin sa watau "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu". 

  Ko da wannan attajiri ya ji haka, sai hasala matuƙa. Ya kira ɗan nasa yana masa faɗa, ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba, yana cewe "Ta yaya zaka yi nasara a harkar kasuwanci, alhali zaka iya ɓannatar da kuɗaɗe masu tarin yawa haka wajen siyen littafi ɗaya tal mai ƙunshe da saɗara ɗaya tal ajikin sa?! Fitar mini daga gida, kada na sake ganin fuskar ka anan!"

  Daga nan Uban ya kori ɗan nasa daga gidan sa.

Wannan matashi ya shiga tsananin baƙin ciki bisa korar sa da mahaifin sa yayi daga gabansa, amma babu yadda ya iya, sai ya ɗauki littafin sa tare da  kama hanya yana tafiya ba tare da yasan inda yake nufa ba. Ya haddace wannan saɗarar dake cikin wancan littafi, don haka yana tafe yana maimaita ta a cikin zuciyar sa.

Akan hanyar sa ya riski wani babban gari, sai ya nemi abashi masauki, mutanen garin suka tambaye shi sunan sa, sai ya amsa musu da waccan saɗara da yake ta faman maimaitawa a zuciyar sa, watau ""Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu". Shikenan, sai aka rinƙa kiran sa da wannan suna.

Wata rana, sai ƴar sarkin garin ta ziyarci wani bikin al'ada na shekara-shekara da akeyi a wannan gari, anan kuma sai ta haɗu da wani kyakkyawan ɗan sarki baƙo wanda shima yazo kallon bikin daga ƙasar su, sai ya kasance ta kamu da sonsa nan take. Sai ta umarci kuyangarta ta bincika hanyar da zasu aika masa da saƙo.

Daga nan Gimbiya ta rubuta ɗan jawabi a takarda, ta baiwa kuyangarta don ta isar a gareshi.

 Sai dai bisa kuskure, wannan kuyanga  ta baiwa matashi Sagardatta wannan wasiƙa a maimakon wancan ɗan sarki, Sagardatta ya karɓaa ya buɗeta, ya soma karantawa kamar haka:-

"Na kamu da sonka tun sa'ar da na soma ganin ka. Ina rokon ka same ni a fadabta. Da zarar ka shiga, za ka samu igiya sarƙafe a ɗaya daga tagogin wajen wadda zata kawo ka kai tsaye zuwa inda nake. Daga Gimbiyar wannan birni”

Ya raya a zuciyar sa da cewa “Tabbas zan amsa gayyatar gimbiya tunda ta buƙaci haɗuwa dani.”

Da zuwan sa ya ga igiya an zirota daga tagar wani ɗaki can a bisan bene, ya kama ta ya soma ɗaɗɗafewa har ya riski ɗakin da gimbiya take. Ɗakin ɗan duhu, kuma gimbiyar tayi tsammanin Yariman nan data gani ne a wajen biki, don haka cikin rawar jiki ta shiga yi masa karɓa cikin girmamawa. Ta gabatar masa da abinci da abinsha kala-kala cikin karramawa.

 Bayan sunci sun sha, sai ta shiga yi masa zantuka tana mai cewa “Nayi matukar kamuwa da sonka. Hakika babu wanda ya kamaci zama miji na sama da kai, ina rokon ka sanar dani menene ra'ayin ka game dani”

Sagardatta yace "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"

Sai tayi mamakin yadda Yarima ɗan sarki zai amsa maganar ta da wannan maganar, da hanzari ta kunna manyan fitulun ɗakin waɗanda suka haskaka shi sosai. Ranta ya ɓaci matuƙa yayin da ta gane ashe ba wanda ta buƙata bane a gabanta, nan take ta fatattake shi tare dayi masa korar kare daga gareta.

  Wannan matashi ya cika da baƙin ciki bisa wannan abu da ya sake samun sa ba bisa laifin sa ba, sai yayi shawarar tafiya wani wajen bauta dake kusa da wajen domin shafe yammaci da daren sa acan, jim kaɗan da isar sa sai bacci ya kwashe shi.

Da lokacin rufe wajen yayi,  masu zuwa bauta duk sun gama tafiya gida, sai wani maigadin dare ya hango matashi na bacci, don haka yazo ya tashe shi yana mai umartar sa da barin wurin, yace masa "Wannan wajen bauta tsoho ne kuma talautacce, idan kai baƙo ne zo muje ka kwana a gida na"

Shikenan, matashi Sagardatta ya bi maigadi zuwa gidan sa dake kusa da wajen, daga nesa ya nuna masa ɗakin da zai shiga ya kwanta kafin safiya. Sai dai cikin kuskure, wannan matashi ya shiga wani ɗakin saɓanin wanda aka nuna masa, wanda aciki ɗiyar wancan maigadi taci ado tana sauraron saurayin ta.

  Mai gadin ya kasance yana da ɗiya wadda take soyayya da wani mutumi, amma ba bisa  son  ran sa ba, har ma ya hana shi kusantar duk inda take. To amma saboda tsabar soyayya, sai wannan ɗiya ta shirya da masoyin nata yin aure a wannan dare yayin da mahaifinta ya tafi gadi a wurin bauta da dare, ta yadda wajibin sa ya amince da matashin a matsayin surukin sa.

Kasancewar akwai duhun dare, da shigar Sagardatti ɗakin, sai ɗiyar maigadi tayi tsammanin masoyin nata ne ya gabato, nan take ta tarbeshi da murna, taje gaban gunkin su  ta ɗauko awarwaron ƙulla aure ta sanya a hannun ta, sannan ta sanya a na Sagardatti. A bisa al'ada, ta ƙulla aure tsakanin su kenan.


Matashi Sagardatti cike da mamaki yace "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"

Ko da taji haka, sai nan take ta gane ashe ta tafka babban kuskure, sannan nadama ta dabai-baye ta tana mai rayawa a zuciyar ta cewa 'dama aduk sanda mutum yake gaggawar aikata wani lamari ba tare dogon nazari ba, tabbas yana iya tafka babban kuskure.'

Nan take ta shiga masa masifa da ci masa mutunci tare da korar sa daga gidan ma baki ɗaya.

Har ila yau dai, Sagardatta ya fito daga wannan gida tare da kama hanya a cikin daren sannu a hankali cike da tsananin ɓacin zuciyar faruwar wannan abu ba tare da ya aikata wani laifi ba, yana cikin tafiya ne ya ga wata tawagar masu ɗaura aure a gefen hanya suna tafiya ana kaɗe-kaɗe da bushe-bushe.

Mutanen suna sanye da kayayyaki na ƙawa, sunyi kwalliya sanye da jawhari da azurfa. Kawai sai ya yanke shawarar shiga cikin su. Yabi bayan ango da tawagar sa, wanda a kusa dashi amaryar sa ce da zai aura ba da jimawa ba, kuma a lokacin suna kan hanyar su ne ta zuwa gidan kawunnan amarya  a inda za ayi ƙwarya-ƙwaryan bikin ɗaurin aure.


Ana cikin haka, Kwatsam sai ga mahaukaciyar giwa ta kutto  tare da tunkaro wannan tawaga, cikin firgici kowa ya dare tare da arcewa, amarya kaɗai tayi tsira yayin da ta gurɗe ta faɗi ƙasa a tsorace tana maƙyarkyata cikin firgici. 


Ko da ganin haka, sai matashi Sagardatti ya zaro wani kullin kusoshi dake rataye dashi, sannan yabi bayan giwa ya buga mata, giwa ta tsorata tare da rugawa da gudu.

Bayan ɗan lokaci tawaga ta dawo, ƴanuwa da abokan arziki suka shiga yiwa amarya jaje da barka da auna arziki, ita kuwa sai ta murtuke fuska, shine ma take cewa "Ayanzu na sauya shawara, domim a lokacin da rayuwata ta shiga cikin haɗari, an rasa wanda zai cece ni sai wannan baƙon, don haka babu wanda zan aura sai shi. Wannan shine abinda na yanke"

 

Wannan mataki na Amarya ya ɓatawa mutane da yawa na cikin wannan tawagar zuciya.  Nan take sai gaddama da cece kuce ta ɓarke a cikin su.. 


Da muhawara tayi tsanani, hayaniya yayi yawa, duk mutanen kewayen wajen suka firfito don ganin abinda ke faruwa. Sai kuma ga Sarkin garin shima ya fito, ashe yaji labarin abinda ya farundon haka ya taso domin yin hukunci. A cikin mutanen dake wannan waje har da gimbiya ɗiyar sarki da kuma budurwa ɗiyar maigadi.


Sarki ya tambayi matashi Sagardatti da cewa "Kana cikin tawagar  biki wannan ibtilai ya auku, sannan kai ne ka kuɓutar da wannan yarinya da ake gab da ɗaura mata aure daga cutarwar giwa, Ina so kayi mana bayanin yadda wannan abu ya faru!"

  Ko da matashin Sagardatti ya yunkura don yin magana, kaɓar kulluɓ, maganar sa dai itace karatun nam da ya haddace, watau  "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu".

 Gimbiya da ɗiyar maigadi duk sunji maganar sa, kuma sun tsargu da ita. Sai suka shiga cikin nadama da damuwa, har sai da Sarki ya lura da hakan.


Koda sarki yaji haka, kuma ya lura da alamar damuwa a fuskokin waɗannan mataye biyu, sai ya ƙara neman cikakken bayani na gaskiya game da wannan lamari. 


Ɗiyar maigadi ta bayar da labarin yadda  ta ɗaurawa kanta aure cikin kuskure da wannan matashi, sannan ta rufe cewa "Ƙaddara ta kenan, kuma bana tuba game da faruwar hakan"

Gimbiya ma ta yiwa sarki bayanin yadda ta shafe lokaci da matashin cikin kuskure, tare da rufewa da faɗin "Ƙaddara ta kenan, bana da-na-sanin faruwar hakan!"

Ko da jin haka, sai wannan budurwa da za a ɗaurawa aure tace "Ya sarkin duniya, abinda ƙaddara ta bani fa, babu mai karɓe mini shi daga gare ni!"

Sarki ya cika da mamakin wannan abu, sannan ya shiga shawarwari da na kusa dashi, daga nan sai ya yanke ɓatsayar sa game da abin, ya sallami mutane.

   Da gari ya waye, ya shirya biki. Ya yiwa matashi Sagardatta kyautar ƙauyuka dubu na ɓasarautar sa baya da zinariya da tarin dukiya. Sannan ya aurar dashi ga ɗiyar sa Gimbiya, tare da naɗa shi a matsayin magajin sarautar sa bayan rasuwar sa.

Ita ma waccan amarya da ɗiyar wancan maigadi, duk sun samu cikar burikan su na auren matashi Sagardatta daga iyayen su bayan an shirya biki gwargwadon ƙarfin n su.


Daga nan matashin yasa aka  gina masa gagarumar fada, sannan bai yi fushi da mahaifan sa ba kasancewar ya gamsu da karatunsa cewa"Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu",  ya gayyato iyayen tare da yanuwan sa zuwa wannannfada dominmsu rayu tare dashi, haka suka wanzu cikin farin ciki.


Darasi: Akwai darussa masu yawa a hikayar gwargwadon fahimtar makaranci, amma dai kaɗan daga ciki sun haɗar da:-

Duk abinda aka ɓatar wajen samun ilimi (hikima) matsawar anyi aiki dashi za a ci riba a gaba, haka kuma a sani cewa sai ansha wuya akan sha daɗi. Sannan, yana da kyau Kayi iya kokarin ka akan lamurorin rayuwa, amma ka barwa ƙaddara dama tayi aikin ta.. domin "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"

Sunday, 21 February 2021

GARIN DANMAJE

 Garin Ɗan Maje


Sadiq Tukur gwarzo

A yankin Dawakin Kudu, cikin ƙasar Kano, akwai wani tsohon gari da ake kira Ɗan maje.

Babu takamaimen lokacin da garin ya kafu, amma an tabbatar da cewa sa'ar da mutane suka soma zama a wannan gari garin kano bai samu kafuwa ba.

 Wani mai suna Maje daga maguzawan farko ne yafi shahara acikin mazaunan garin na farko, shine kuma ya zama shugaba a garesu, daga bisani sai ɗansa  ya gajeshi wanda ake kira Ɗan Maje.

Daga nan garin ya samo asalin sunan sa.

Labarin Rijiyar Gidan Matage

Akwai babban abin mamaki game da wannan rijiya. Ana iya cewa itace silar kafuwar garin.

Wannan rijiya ta samu kafuwa shekaru masu tarin yawa da suka gabata, babu labarin wanda ya haƙe ta, amma ana danganta ta da ƙwanƙwamai wajen bayyanuwar wasu ababen mamaki, ana kuma haɗata da rijiyar Kusugu ta Daura wajen nuna tsufan ta,  sannan har yanzu babu wani abu na zamani da take karɓa.

Ba'a ɗebo ruwa da gugan ƙarfe ko na fata har yau daga cikin wannan rijiya, idan kuwa mutum ya so jarraba haka, anan take zai ji an fisge gugan daga cikin ta, idan akayi rashin sa'a ma har da shi kansa za a haɗa a fizga daga cikin rijiyar.

Sannan duk wani yunkurin da akayi wajen yi mata ɗaurin baki da bulon siminti na zamani yaci tura.

 Ance sau tari idan abu ya ɓata a kogin wudil, har akayi nema aka rasa, wannan rijiyar ake zuwa a bincika sannan a ganshi. 

  Akwai labarai mabanbanta da aka ji dangane da ɓullar kwale-kwale a ƙasan rijiyar a lokuta daban-daban, wanda hakan ke nuna kai tsaye idon rijiyar haɗe yake  yake da kogi.

  Akan jiyo kaɗe-kaɗe da bushe-bushe a wasu lokutan daga cikin wannan rijiya, da kuma wasu abubuwa na mamaki masu hana bacci da bada firgici.

Babu ganuwa irin ta kano a garin Ɗanmaje wanda ke nuni da raahin tumbatsar sa a tsawon lokaci, amma dai idan labarin yaki ya iso garin, Dawakin kudu, Tamburawa da Kano mutane ke guduwa domin tsira.

Akwai abubuwa masu yawa a tattare da ita wanda sannu a hankali bincike zai fito dasu


 

Monday, 15 February 2021

05. ZUWAN TURAWA KANO: MAHANGA TA 2

 Yaki ya Kare da Turawa

Kamar yadda aka nuna a baya kadan, bayan da aka kashe Waziri Amadu, sai dakarun yakin Kanawa suka rarrabu. Wasu suka bi Galadima Mamuda, wasu Wambai Abbas, wasu kuma Madaki Kwairanga, dukkansu suka nufi Kano.

Shi kuwa jagoran yakin Turawa Lugga ya umurci sojoJin sintiri kada su sake auka wa jama'a masu dawowa Kano daga

Sakkwato, domin yana kokarin daidaitawa da Wambai Abbas wanda zai 6ullo ta wajen Gwarzo. Dama can Wambai Abbas ya aika wa Lugga takarda cewa zai dawo gida Kano. Nan da nan Lugga ya amince da wannan takarda cikin gaggawa wadda aka rubuta ranar 6 ga watan Maris 1905. Abbas ya shigo birni tare da mabiyansa ta kofar Kansakali. An kiyasta Wambai ya shiga Kano da kusan mutane dubu goma (10,000) har gami da wasu ragowar mutanen Waziri Amadu wadanda suka tsira.

Da suka iso suka sauka daga kan dawakinsu, sai suka isa damfamin Gwamna da farin ciki, Gvwamna Lugga ya fada wa Abbas shi fa ba ya fushi da wadanda suka yi yaki da mutanensa, muddin dai sun yi wannan yaki a kan gaskiyarsu. Nan da nan Lugga ya yi taron gaggawa shi da sauran mutanensa, sai ya umarci Wambai ya je ya zo da magoya bayansa wadanda suka mika wuya ga Turawa, kuma su bayar da kayan fadansu. A wannan taron ne Gwamnan farko a Nijeriya "Lord Luggard" ya tabbatar wa da Abbas ya zama sarkin kano na riko. 

A nan kuma ya sanar da su matsayin Turawa a cikin mulkinsu da cewa, Turawa ba za su shiga harkar addininsu ko

al'adarsu ko dokokinsu ba, muddin dai ba su kauce wa tsarin Turawa ba. Lugga kuma ya tabbatar musu da cikakken mulkin Ingila a kan mulkin kasar gaba daya. Bayan Gwamna Lugga ya ba Wambai Abbas shugabancin Kanawa kafin a zabi sabon sarki, sai Wambai da jama'arsa suka

shigo cikin birnin Kano tare da wake-wake. Kidan badujalar soja ya koma kidan kamar haka:

Gajere bakin cikí,

An kirga kudi,

Ga mai su ya iso.

Tana kasa tana dabo,

An ki shukar maiwa,

Ga maiwar ta fito!

A lokacín da Gwamna Lugga yake nada Wambai Abbas ya zama Makaddas, ya karanta masa wasu sharuɗɗa na zama tsakanin su da turawa (Mani, 1978: 98-100).

  Gwamna Lugga yace, "'yanzu tun da Turawa ke mulki a ƙasar nan, kuma sune zasu zaɓi wanda zai yi kowacce irin sarauta, amma za a bar mutame su yi abinsu kaɓar yadda suka gada. Zartar da al'amura duka yana wurin Gwamna kuma Gwamna yana iya tube sarki saboda rashin iya mulki.

Haka kuma a game da addinin Musulunci, Turawa ba zasu hana ci gaba da yadda ake yi ba. Dukkan gidajen shari'a da majalisar sarakuna za a tabbatar da ikonsu bisa ga yadda Razdan ya ga ya kyautu. Yi wa mutane azaba da tura daruruwansu cikin kurkuku  ba imani, duk ba za a yarda da wannan ba. Kuma ba za a yarda akashe kwabo ba sai da sanin Razdan. Za a hana toshiya da cin hanci da mummunan zalunci duka. Wadansu irin laifuffukan kuwa a

hukunta su a dakin shari'a na lardi, wato shari'ar da ta shafi mutane da su ba 'yan kasar nan ne ba, ko ma'aikatan gwamnati duka can zaa kai su a yi musu shari'a. Gwamnati kuma za ta aza kudin harajin ta

bisa ga yadda Gwamna ya ga ya dace, sai dai harajin da Za a saka, ba za a bar zalunci ya shiga cikinsa ba. Masu fatauci da 'yan kasuwa duk za a taimake su yadda za su ci gaba da sha'anoninsu, arziki ya karu. Sarki ba zai saka musu harajin kome ba, sai irin abin da Gwamna ya ce ga yadda za a aza musu. Za a bar kowa ya yi anfani

da wurin da yake rike da shi, in gona ce ko gida, sai fa in gwamnati ta ga tana da bukatar wurin don yin wani aiki wanda zai amfani kasar baki daya.

Gwamna Lugga ya ci gaba da cewa, "Na ba da karfí a kan hana cinikin bayi, balle fa zuwa harinsu, amma ba zan ce kome akan

bayin da kowa yake da su a yanzu ba." Sai dai su ma wadanda suke bautar yanzu, in sun ga ana kwarar su, to, suna iya kai kara wurin Razdan. In an tabbatar lallai ana kwarar su, sai a kubutar da su a yanta su dole".

Gwamna Lugga ya kara bayyanawa Wambai cewa, ba yaso yaga masu zaman banza, kowa ya yi aiki. Ba ya kuwa son bara irin duk mai jin karfi lalle ne ya yi aiki, kuma a biya shi lada a aikinsa. Kuma zuwa gaba, ba sarkin da aka yarda ya ajiye rundunar masu yaki. ldan har sarki ya sa talakawansa su yi wani abu, sa an na ya ga sun ki bin umurninsa, to, abin da zai yí shi ne ya je ya fada wa Razdan. Kuma duk makamai ba a son a ga kowa da su, sabodahaka KOwa sal ya mika nasa a tara wuri daya.

 Kuma wanda duk aka gani da makami muddin bai sami izini daga wurin Razdan ba, to, a a hukunta shi. Kuma duk irin abin da aka kai don sayarwa ga soja, to Su saya su biya dole. Ita Sakkuwato kuwa ita ce gaba, amma ba Za akai mata gaisuwar bayi ba.

Gwamna Lugga ya rufe jawabinsa da cewa, "Gwamnati ba ta da niyyar tayar da mutane daga kan al'adunsu." Ya ce burinsu shi ne

su yi kokarin yadda za su san al'adun wannan kasa har su fahimce su

SOsai, su gane abin da jama'a suke so da wanda ba su so. A nan ne Gwamna Lugga ya tabbatar wa da Wambai cewar Turawa fa sun zo kenan ba kuwa za su tafi ba."

04. ZUWAN TURAWA KANO: MAHANGA TA 2

 Kanawa sun Gwabza da Nasara

Tuni an ba da labarin zuwan Turawa na farko a zamanin Sarki Ibrahim Dabo, an kuma yi bayanin zuwan Dakta Miller da zimmar ya yaɗa addinin Kirista a kasar Kano. A wannan dan karamin sashe kuma an samu jin yadda Turawan Mulkin Mallabe suka gwabza gwagwarmayar

da irin kokarin Turawa wajen ganin sun ci Kwantagora da Bidda da yaƙi, nan da

labarun yadda aka ci wadannan birane ya bazu a ko'ina a kasar Hausa.

   Saboda haka dole babban birni irin na Kano su ma su shiryawa zuwan Turawa. Turawa sun iso kogin kofar Zariya sun sauka, Kanawa sun sami labari akan haka.

Kuma dukkan kasashen Arewa dole su zuba wa Kano ido wadda itace babbar cibiyar Arewacin Nijeriya. Domin babu wani gari mai cikakkiyar ganuwa da tsaro da dakaru masu yawa da kuma

kayayyakin yaki irin na Kano. To, amma abin da ya kawo zuwan

Turawa Kano da wuri shi ne, Magajin Garin Kafin Ɗanyamusa ne ya

kashe Rasdan din garinsa wanda ake kira Kyaftin Maloney. 

To, sai ya gudo Kano inda Sarkin Kano ya karbe shi, ya ba shi mafakar siyasa. 

Dadin dadawa, Turawa sun sami labarin wai Kano tana ta shirye-shirye ta afka musu da yaki. Wannan shi ne dalilin da yasa hankalin Turawa ya koma kan Kano kurum, kuma suna tsammanin

yakin Kano zai fi na ko'ina wahala, saboda  girman mayakanta. Turawa sun dakata a Zariya sai da suka haɗa

babbar runduna mai yawan hafsoshi ashirin da shida (26)  da kanana(13) da likitoci (2) da dakaru bakar fata (800)

dabindigogi hudu (4) masu karfin milimita (75) da manyan bindigogin yaki biyar (5), sannan suka nufo Kano da sanyin Safiya.

To, a ranar 29 ga watan Janaiu 1903, Kanar Morland wanda ake kira Maimadubi ya jagoranci wadanda za su yi yaki da kano.

A ranar da sukanfara tahowa daga wannan ƙauye zuwa wannan kauye, har suka iso Bebeji wani gari wanda bashi da nisa da iyakar  Zariya zuwa Kano. Daga nan Turawa suka fara fahimtar ba a yi maraba da zuwan su ba.

  Da ma Sarki ya umarci sarakunansa da kada wanda ya buɗewa Nasara kofa idan sunzo garin sa. Da isowar Turawa Bebeji aka soma faɗa dasu, suka kashe sarkin BABEJI JIBIR.

Da jin abin da ya faru a Bebeji, saindukkan kauyukan da ke kan hanyar zuwa birnin kano suka karaya, sai suka rika gudu suna shiga cikin Birnin Kano.

 Kanar Morland da dakarunsa sun yi kokarin su karya kofar birni abin ya fasKare su. To, sai suka ci gaba  zuwa wata kofar wadda  da ma wani Bature soja, Laftana Gyar, ya isa tare da jama'arsa. Ita ma ta gagare su budewa. Ana nan a kan haka, sai wani soja ya yi dabara ya jefa igiya

kan garun badala saboda ya yi kokari ya leka cikin gari. Da dai jama'a suka hangi jar hularsa, sai suka rika shekawa a guje cikin gari.

Da soja suka ga banza ta fadi sai suka harbe kyauren ya fadi, suka

rika bin mutane suna harbewa. Mutane suka rude, garin gudu wannan ya buge wannan, da haka su da kansu suka rika yi wa junansu rauni.

 Sallama Jatau da Sarkin Shanu Dangwari, wadanda Sarki ya bar wa jiran gari, suka fito suka tari Turawa. Da suka

fahimci abin ba mai sauki ba ne, sai Sallama Jatau ya nufi gidan

sarki inda ya debe wasu daga cikin iyalin sarki ya fita da su. Sarkin

Shanu kuwa ya hau kan bene ya dinga harbin Turawa, su ma suna

harbin sa har dai suka yi nasarar harbe shi. Sannan soja suka wuce, suka isa har gidan sarki, amma sai Sarkin Gida ya ce, babu wanda ya isa ya shiga gidan. Ana cikin

Wannan ja-in-ja sai Sarkin Gida ya zare takobi ya sari wani Bature a

hannu ya yi masa mummunan rauni. Nan take aka harbe Sarkin Gida

ya mutu. Da ganin Turawa sun shiga cikin gidan, sai wata kuyanga ta

yi kokarin ta sanya wuta a taskar sarki, inda yake ajiye kayan

yakinsa, amma sai wata 'yar'uwarta ta hana ta. Haka dai sojan nan suka bi ko'ina cikin gidan sarki suka bincike, sannan suka je suka bude gidan yari duka fursunoni suka fita. Turawa suka kame Kano ta koma karkashinsu.

03. ZUWAN TURAWA KANO: MAHANGA TA 3

 Dokta Miller Kano

Bayan yakin Basasa da yakin Damagaram na daya da na biyu, Dakta Miller ya iso  Kano, Babu ma wanda ya gane Bature ne, domin ya yi shigar tufafi irin na mutanen wannan kasa. Dokta Miller

shi ne Wanda ya kawo addinin Kirista nan Kano har kuma ya tsufa ya mutu a Ɓukur, Miller sanannen Baturen Mishan ne a Kano. Miller ya iso ne tare da wasu Turawa da ayarin wasu 'yan kasa suka taso tun

daga Ikko da nufin zuwa Kano. Tafiyar wata biyu suka yi da Kafafuwansu, sannan suka iso Kano da bazara, Sarkin Kano Aliyu ya sauke su a gidan baki, A yayin da suka zo Kano sun yi murna da

ganin ganuwar birni mai girma fiye da yadda ma aka ba su labari.

Dokta Miller ya ce har da dai Sarki ya sauke su, amma bai yi musu karɓar kirki ba. Sun gaya wa Sarki cewa su masu wa'azi ne na Kirista kuma zasu gina makarantu da dakin shan magani. Sarki ya ce bai yarda ba, domin kuwa kowane irin magani akwai shi a Alkur'ani. 

Da suka koma masauki, saboda ganin Sarki bai amince da zuwansu ba, mutanen gari suka rika tsammanin ma za a kai su Jakara a sare su.

Sai yaransu masu daukar musu kaya suka rika zare jiki sunna guduwa.

Anan Waziri Amadu ya baiwa Sarki shawara kada ya kashe su tun da

yake sun taho da amana, a bar su su koma inda suka fito. Sarki ya umarce su dasu bar masa ƙasar sa.  To, yaransu duka sun tsorata sun gudu. Waziri ya roƙar musu ka  Sarki ya ba su jakuna dari (100) masu daukar musu kaya.

02. ZUWAN TURAWA KANO: MAHAMGA TA 2

 A wannan kasuwa akwai kayan sayarwa irin na Masar da Mali da Libya da Moroko da na Aljeriya. Wadannan kaya na Kasashen waje suna tsakiyar kasuwa, kuma akwai kayan gida kamar wadanda aka saka ko aka kera, wadansu kuma aka rina da kuma kayan sawa wadanda aka dinka kamar riguna da taguwoyi. Kyallayen tufafi da 'yan turamen sukari da ake sayarwa da gishiri da manda da 'yan kayayyaki na gabas duk akwai su a kasuwar.

Ga kuma tukurwa da ake daura gadon amarya da dirkoki da zana da

ingirici da shuci duk suna a bangare daya. Ga kuma kayan aiki irin

su garma da fartanya da lauje da wuka jefi-jefi. Akwai awaki da

tumaki da shanu da dawaki har da rakuma na sayarwa. Ga tayakan

hatsi da dai sauran kayayyakin sayarwa da yawa ko'ina barkatai a

cikin kasuwa.

Har wa yau, a kasuwar Kurmi, akwai manya-manyan dillalai masu saye da sayar da kayan kasashen waje. Duk kayan da aka sayar

za a rubuta sunan dillalan a kan kayan da Arabiyya, bayan an tafi da

kayan idan an ga wani ha'inci sai a dawo wa da dillalin da ya sayar

da kayan ya biya kudin. Saduwa da sarki ta fi fatauci, ta fi a duƙawa gona noma.

Baturen ya ce, ya sadu da sarki ido-da-ido domin lokacin da suka isa

Kano Sarki ba ya nan, ya yi hawan salla ya tafi Dala. Bature ya ce,

lokacin da sarki ya dawo, sai ya tsaya a kan doki ya yi wa mutanensa

huduba. Sarki ya ce, lalle mutane su dage haikan kan daukaka

addinin Musulunci babu karkata, su yi imani da Allah daya, su fitar

da zakka su tsayar da salla su yi layya ga wanda ya sami iko. Bature

ya ce, bai ankara ba sai ya ji an sake cewa Sarki ba ya nan. Wato

Dayan hudubar da ya yi, ya juya ya tafi Fanisau, wani gida da ya

shirya a matsayin sansanin yaki, mil biyar daga birni. Bature ya nemi

abokan tafiyarsa wadanda suka rako shi, su ne El-Wardee da

latsallah wasu Larabawa, suka raka shi Fanisau. Ya ce da shigar sa

Cikin garin Fanisau sai ya fara ganin mayakan sarki sahu-sahu cike

da gari. Aka ce da shi idan Sarki ya gama hada rundunarsa ta yaki zai tafi domin yaƙar Malam Dantunku.

 Bature ya ce, haba! Tun kafin su iso nake

ganin gidajen mayaka na kan hanya cike da mayaka, idan dukkan mayakan da ya gani sun hadu za su bi sarki har ya yi mamakin ganin wasu daga cikin abokan ayarin su sun zo fanisau wurin sarki sun taho masa da dawaki na sayarwa. Su

Da isar wannan Bature aka fara kai shi gidan Wambai domin

masa iso a sada shi da Sarki. A nan ya dakata kafin ya sami ganin

Sarki, da ya bi Wambai gidan sarki kafin su shiga ya fara ganin gidajen masu gadi gefe da gefe daga waje. Yana shiga sai ya ga abin mamaki dukkan katangar gidan daga ciki an lullube ta da fatar garkuwar yaki. Kofar gidan kuwa akwai dubban jama'a suna harkokinsu. Ana ta kade-kade da bushe-bushe, bayan an wuce wani

fili akwai wani katon daki inda ya hangi mutane suna kewaye da

Sarki, an rataye takobi a bango, bayi suna yi masa fiffita. Da ganin

Sarki hakika ka san Bafulatani ne mai cika ido da kwarjini. Dogo ne kwarai, fari a jikinsa kamar tagulla. Hamshakin Sarki, kamilalle,yana sanye da kayan zina irin na Masar, A hagu da dama, bayi da

ya'yan sarki da manyan mutane suna zaune a kewaye da shi, 

shikuma yana zaune a kan gado. Baturen ya ci gaba da cewa, yadda yaga Sarki ya san malami ne masani, mai ilimi, yana ma ta Larabci tare da Larabawa da suka raka shi, Ya mika wa Wambai takardar Shehun

Barno tare da agogon da ya aiko wa Sarki. Sarki yana Karata takardar a zuciyarsa, sai ya ga yana ta murmushi da yake nuna Sarki yana farin ciki da aiken Shehu. Sai ya ce, agogon a ba wa wani balarabe don ya koyi sanin lokaci, shi kuma ya sanar da Sarki lokaci. Daga nan kuma baturen ya fito da tasa gaisuwar ta takobi da faranti na shan shayi da  kwanuka 5 na faranshi da yadin zani rawaya 25 da yadi 4 na siliki da kwanuka 5 da madubi mai kawo nesa da kananan akwatuna guda 3 da wukake 4 da reza 2 da da farin rawanl da

tagullolin wasan yara da karyayyen ma'aunin zafi 2 da sanyi da almakashi. Sarki yayi murna kwarai da gaske, ya yi godiya yi, Sarki yace da wambai a kai baturen  masauki, idan Allah ya dawo da shi lafiya da daga fagen gama zai haɗa shi da  Muhammadu Bello ya yi ziyara ya dawo lafiya.

 Da  Baturen Musulmi ya isa masaukin sa sai ya tarar har sarki ya sa an kai masa

shinkafa buhu 2 da raguna kiwatattu 2 da tandun mai 2 da sukari 2 da kayan cefane da kudi a matsayin shiɗa a gare shi.

  Da Sarki ya dawo daga yaki sai ya haɗa shi da jama'a suka kai shi Sakkwato suka dawo da shi Kano. Daga nan ne kuma ya tafi Borno zuwa Libya sai gida (Clapperton; 1829).

01. ZUWAN TURAWA KANO: MAHAMGA TA 2

 Zuwan Turawa na Farko Kano


Tun zamanin Sarkin Kano Ibrahim Dabo Turawa suka fara zuwa Njeriya ta Arewa domin wasu dalilai kamar sayen bayi da neman dukiya da mulki.

   Turawa Sun somashigowa Nijeriya ta ruwa ne ruwa ta Libya suka biyo ta Katsina suka zarce har suka iso Kano. Su ma TuraWasun zo Wannan kasa ne

Kungiyoyi daban- daban da kuma a daidaiku.

 Misalin-

Turawa da suka zo Kano akwai Dr. Barth da kuma Mr. Clappertom da Mr. Denham da Mr. Oudney, Wasu dag cikinsu ma sunzo ne da shiga irin ta Larabawa ta yadda ba za a gane su ba.

 Mr. Clapperton ya ce, da isowarsa kasaitacciyar ganuwar gari ta Kano, ya yi matukar murna da farin ciki. Amma ya yi mamaki, maimakon ya fara ganin manya-manyan gine-gine irin na Larabawa a cikin gari, tun daga shiga cikin badala, sai da ya yi tafiya mai nisa kafin ya isa ga gine-

ginen cikin gari. Ba kamar yadda ya sami labari ba, shi dai birnin (Kano) mai girman gaske ne, ga jama'a masu yawa, wasu suna shiga wasu suna fita, amma kuma ba su kula da shi ba, saboda irin shigarsa da launin fatarsa.

 Ya ce, saboda rashin kulawa da shi, shi ma bai kula da mutanen ba, ballantana ya ba da labarinsu. 

  Ya ci gaba da cewa, hakika ko a wancan lokacin akwai mutane masu yawan gaske da gine-gine a birnin Kano. Yawan mutane a Kano ya fi na kowanne daga cikin garuruwan da ya gani a Afirika, Akalla a cikin garin akwai mutum dubu talatin (30,000) ko dubu arba'in (40,000) a hautsine da bakin mutane daga nahiyoyin Afirika wadanda suka zo ciniki. 

   Garin kuma yana da yawan kududdufai. Daga Arewacin garin akwai wasu fitattun duwatsu guda biyu wato Dala da Goron Dutse, kowanne kuwa tsawonsa ya kai kafa 200. A dab da kofar gari kuwa wato à cikin badala akwai babban dakali wanda 'yangadi suke hawa su hango wajen gari.

  A tsakiyar gari cikin wani kurmi akwai wata ƙasaitacciyar kasuwa tana cike da manya-manyan fatake da dillalan bayi. Sannan  kuma suna yin ciniki ne ta hanyar furfure. Alal misali, wani ya zo da gishirinsa tafi daya, sai suka yi musaya da mai kifaye biyar. Wani kuma da ya kawo tunkiya aka saye ta da adadin wuri masu yawa."

Daga littafin

DAULAR FULANI A KANO, na   Alh Nasidi Umaru (Galadiman Daji)