HIKIMAR IYA MULKI: LABARIN MADAKIN KANO MAHMUDU
Marigayi Mallam Aminu Kano ya ruwaito a littafinsa 'Hikayoyin Kaifafa Zukata' cewa:
An bamu labari cewa a zamanin marigayi madakin Kano Mahmudu, talakawan wani ƙauye a ƙasar Bichi sun yi bore bisa biyan haraji.
Bayan sun ƙi biyan harajin, har ma dagacin ƙauyen suka kora da jifa.
Lokacin da dagacin ya isa ga Hakimin Bichi, sai nan da nan Hakimi ya aike dogari da yaran hakimi don a binciko masa lamarin.
Ai kuwa dogari da yaran hakimi suma basu tsira ba, domin da zuwan su sai suka tarar mutanen garin sunyi shirin yaƙi mazansu da matansu, sun fito da karnukan su na farauta, suna masu riƙe da masu, kwari da baka da gatura. Don haka ba jimawa suka ranta a na kare zuwa gaban Hakimi.
Ganin abu ya kai haka sai hakimi ya aika zuwa ga Sarkin Kano. Daga nan kuwa aka sanar wa Razdan na kano.
Shi Razdan bai yi wata-wata ba sai ya gayawa baturen ƴansanda cewa a tafi da shiri zuwa ƙauyen a kamo masu boren.
Amma da wannan magana ta dawo gaban Sarki, sai Madakin Kano Mahmudu ya yi wuf ya ce yana roƙon Sarki ya bashi dama ya soma zuwa da kansa kafin a je da ƴan sanda.
Da turawa suka ji wannan sai suka ce fau-fau haka ba zata yiwu ba. Tun da har mutanen sun ɗauko makamai, maganin su ƴan sanda masu bindiga.
Duk da haka, Madaki ya dage cewa yana roƙo a bari ya fara zuwa tun da shine Kansila mai kula da hakimai, haraji da sauran irin su. Kuma mutanen ƙauyen suna tare ne da matansu da ƴaƴansu duk a garin.
Da ƙyar dai turawa suka yarda ya je.
Ai kuwa da zuwan sa garin Bichi, sai ya aika ƙauyen da saƙo cewa Sarki ya aiko shi gare su, don haka yana so su taru dukkansu a cikin shirinsu, kada a rage kowa.
Kafin a ce mene ne wannan, mutanen sunyi cincirindo a bakin kasuwar ƙauyensu mazansu da matansu. Suna cike da fushin komai zai faru sai dai ya faru.
Ba jimawa sai ga Madaki tare da Hakimin Bichi, da dagacin ƙauyen, da malaman hakimi sun ƙaraso wurin. Wuri yayi tsit ana sauraron aji saƙon Sarki.
Sai Madaki yace "Jama'a Sarki ya gaishe ku, ya kuma ya gaishe ku. Ya ce in gaya muku cewa ya sami labarin abinda ya faru tsakanin ku da mai garinku wanda har abu ya kai da tashin hankali.
To kuyi sani, abinda Sarki yace in faɗa muku shine Sam bai taɓa cewa ku biya haraji ba. Saboda haka kun yi gaskiya da kuka ƙi biya."
Nan take wuri ya ɓarke da sowa ta godiya da cewa 'Allah ya bar Sarki, Allah ya bar Sarki'.
Sai Madaki ya cigaba da cewa "Amma abinda Sarki ya gaya wa mai garinku ya karɓa gare ku shine kuɗin arziƙi. Don haka ya turo ni in ware masu arziƙin cikin ku da matsiyatanku don mu sallami matsiyatan, masu arzikin su biya".
Nan fa wuri yayi tsit. Sai wannan ya dubi wannan yace "yo waye zai yarda a kira shi matsiyaci?".
Daga can sai wani dattijo yace "Ranka ya daɗe duk cikin mu ba matsiyaci, saboda haka muna so mu je mu kawo".
Madaki ya basu lokaci aka tattaro harajin ƙauyen tsaf ba tare da anje da bindiga ba, wanda a wancan lokacin yawan harajin bai kai ya kawo ba.
Don haka Sahabi Mu'awiyya ya taɓa faɗawa ɗansa Yazidu cewa "Idan za ka biya buƙata da harshe, kada ka sa alƙalami. Idan kuwa da alƙalami ne, to kada ka sa takobi".
Marigayi Mallam Aminu Kano ya ruwaito a littafinsa 'Hikayoyin Kaifafa Zukata' cewa:
An bamu labari cewa a zamanin marigayi madakin Kano Mahmudu, talakawan wani ƙauye a ƙasar Bichi sun yi bore bisa biyan haraji.
Bayan sun ƙi biyan harajin, har ma dagacin ƙauyen suka kora da jifa.
Lokacin da dagacin ya isa ga Hakimin Bichi, sai nan da nan Hakimi ya aike dogari da yaran hakimi don a binciko masa lamarin.
Ai kuwa dogari da yaran hakimi suma basu tsira ba, domin da zuwan su sai suka tarar mutanen garin sunyi shirin yaƙi mazansu da matansu, sun fito da karnukan su na farauta, suna masu riƙe da masu, kwari da baka da gatura. Don haka ba jimawa suka ranta a na kare zuwa gaban Hakimi.
Ganin abu ya kai haka sai hakimi ya aika zuwa ga Sarkin Kano. Daga nan kuwa aka sanar wa Razdan na kano.
Shi Razdan bai yi wata-wata ba sai ya gayawa baturen ƴansanda cewa a tafi da shiri zuwa ƙauyen a kamo masu boren.
Amma da wannan magana ta dawo gaban Sarki, sai Madakin Kano Mahmudu ya yi wuf ya ce yana roƙon Sarki ya bashi dama ya soma zuwa da kansa kafin a je da ƴan sanda.
Da turawa suka ji wannan sai suka ce fau-fau haka ba zata yiwu ba. Tun da har mutanen sun ɗauko makamai, maganin su ƴan sanda masu bindiga.
Duk da haka, Madaki ya dage cewa yana roƙo a bari ya fara zuwa tun da shine Kansila mai kula da hakimai, haraji da sauran irin su. Kuma mutanen ƙauyen suna tare ne da matansu da ƴaƴansu duk a garin.
Da ƙyar dai turawa suka yarda ya je.
Ai kuwa da zuwan sa garin Bichi, sai ya aika ƙauyen da saƙo cewa Sarki ya aiko shi gare su, don haka yana so su taru dukkansu a cikin shirinsu, kada a rage kowa.
Kafin a ce mene ne wannan, mutanen sunyi cincirindo a bakin kasuwar ƙauyensu mazansu da matansu. Suna cike da fushin komai zai faru sai dai ya faru.
Ba jimawa sai ga Madaki tare da Hakimin Bichi, da dagacin ƙauyen, da malaman hakimi sun ƙaraso wurin. Wuri yayi tsit ana sauraron aji saƙon Sarki.
Sai Madaki yace "Jama'a Sarki ya gaishe ku, ya kuma ya gaishe ku. Ya ce in gaya muku cewa ya sami labarin abinda ya faru tsakanin ku da mai garinku wanda har abu ya kai da tashin hankali.
To kuyi sani, abinda Sarki yace in faɗa muku shine Sam bai taɓa cewa ku biya haraji ba. Saboda haka kun yi gaskiya da kuka ƙi biya."
Nan take wuri ya ɓarke da sowa ta godiya da cewa 'Allah ya bar Sarki, Allah ya bar Sarki'.
Sai Madaki ya cigaba da cewa "Amma abinda Sarki ya gaya wa mai garinku ya karɓa gare ku shine kuɗin arziƙi. Don haka ya turo ni in ware masu arziƙin cikin ku da matsiyatanku don mu sallami matsiyatan, masu arzikin su biya".
Nan fa wuri yayi tsit. Sai wannan ya dubi wannan yace "yo waye zai yarda a kira shi matsiyaci?".
Daga can sai wani dattijo yace "Ranka ya daɗe duk cikin mu ba matsiyaci, saboda haka muna so mu je mu kawo".
Madaki ya basu lokaci aka tattaro harajin ƙauyen tsaf ba tare da anje da bindiga ba, wanda a wancan lokacin yawan harajin bai kai ya kawo ba.
Don haka Sahabi Mu'awiyya ya taɓa faɗawa ɗansa Yazidu cewa "Idan za ka biya buƙata da harshe, kada ka sa alƙalami. Idan kuwa da alƙalami ne, to kada ka sa takobi".