TARIHIN NUFE: LABARIN SHEHU ABDURRAHMAN SHERIF
Kashi na biyu
SADIQ TUKUR GWARZO
Daga nan sai Shehu Abdullahi ya sallami Shehu Abdurrahman don ya koma wurin Shehu Usmanu.
Da ya ƙarasa wurin sa, sai yace masa "ban sami karatu ba a wurin ɗan uwanka".
Babu jimawa kuma akace sai ga Shehu Abdullahi Gwandu ya iso wurin Shehu Usmanu. Inda yace masa "Ya hasken zamani, ya shugaban addini, ka aika mini da baƙo Banufe, baubawa mai zane da yawa a fuskarsa domin ya wulaƙanta ni ne?"
Sai Shehu Usmanu yace "Wannan magana ba haka bame kamar yadda ka faɗa"
Ana haka sai Abdurrahman ya nufi shehu Usmanu domin ya zauna tare dashi akan gadon sa. Sai kuwa Abdullahi Gwandu ya janyo shi, domin hana shi zama tare da shehu.
Sai Shehu Abdullahi ya faɗi ga shehu Usmanu " Ya shugaban addini mai sabunta addini, hasken zamani, fitilar addini, kambin yamma, babban waliyyin yamma, wannan Banufe yana da wata karama ne ta masu girma har da ka girmama shi?"
Sai Shehu Abdurrahman ya umarci wani yaron sa ya kawo buzun rago. Ko da aka kawo masa sai nan take ya jefa shi sama a matsayin shimfiɗa, sannan ya hau kai ya zauna a kansa.
Ganin haka sai Shehu Usmanu yace da ɗanuwansa Abdullahi "Ya ɗanuwana ko kaga girman da Allah ya bashi? Don haka nace maka ka bar magana dashi. Ni haƙiƙa na ganshi da malami na Mala'ika Jibrilu suna karatu cikin sama tare".
Bayan wannan sai Shehu Abdurrahman yace "Ya Shaihu Usmanu, ko kana da wata ƙasa ta abokan gaba wadda ka yaƙe ta amma baka ci ta ba?"
Sai Shehu yace masa "Ina da ita, na yaƙe ta har sau uku ban sami buɗinta ba har yanzu. Ita ce Gobir"
Sai Abdurrahman yace masa "Ka yarda mini in tafi in yaƙe su?"
Shehu Usmanu yace masa "na yardar maka"
Sai kuwa Shehu Abdurrahman ya fidda yaƙi gareta, yaje ya yaƙeta, yaci nasara, ya sami ganima, kuma dukkan fulani ma suka sami ganima.
Sa'an nan mutane suka cewa Shehu Usmanu "In ka bar Abdurrahman anan zai karɓe mulkin ƙasa duka daga hannun ka in baka maishe shi Nufe ba"
Sai kuwa Shaihu ya sallameshi bayan ya roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa.
Sa'an nan Allah ya fishshe shi daga ƙasar Hausa ya maishe shi ƙasar Nufe, ya fita daga gareta ranar laraba.
A zamanin da ya fita yana tare da dawaki saba'in, ya tasamma wani gari da ake ce masa Adusa. Ya gamu da jama'ar garin a Gabi ya yaƙe su, ya samu ganima dasu. Daga nan suka sake shiryawa suka tarbe shi gamuwa ta biyu a Adogudawa suka buga yaƙi, nan ma yaci su da yaƙi.
A wannan zamanin kuwa Sarkin Nufe da ake kira Etsu Ikaku bai fara sarauta ba, ana kiran sa da suna Manmachu. Kuma yana zaune a wani wuri da ake kira Kodagi bayan an tura shi yaƙi baici nasara ba yaƙi komawa gida, har ya gina babban gari a wajen ya zama sarki mai ƙarfin gaske.
Kashi na biyu
SADIQ TUKUR GWARZO
Daga nan sai Shehu Abdullahi ya sallami Shehu Abdurrahman don ya koma wurin Shehu Usmanu.
Da ya ƙarasa wurin sa, sai yace masa "ban sami karatu ba a wurin ɗan uwanka".
Babu jimawa kuma akace sai ga Shehu Abdullahi Gwandu ya iso wurin Shehu Usmanu. Inda yace masa "Ya hasken zamani, ya shugaban addini, ka aika mini da baƙo Banufe, baubawa mai zane da yawa a fuskarsa domin ya wulaƙanta ni ne?"
Sai Shehu Usmanu yace "Wannan magana ba haka bame kamar yadda ka faɗa"
Ana haka sai Abdurrahman ya nufi shehu Usmanu domin ya zauna tare dashi akan gadon sa. Sai kuwa Abdullahi Gwandu ya janyo shi, domin hana shi zama tare da shehu.
Sai Shehu Abdullahi ya faɗi ga shehu Usmanu " Ya shugaban addini mai sabunta addini, hasken zamani, fitilar addini, kambin yamma, babban waliyyin yamma, wannan Banufe yana da wata karama ne ta masu girma har da ka girmama shi?"
Sai Shehu Abdurrahman ya umarci wani yaron sa ya kawo buzun rago. Ko da aka kawo masa sai nan take ya jefa shi sama a matsayin shimfiɗa, sannan ya hau kai ya zauna a kansa.
Ganin haka sai Shehu Usmanu yace da ɗanuwansa Abdullahi "Ya ɗanuwana ko kaga girman da Allah ya bashi? Don haka nace maka ka bar magana dashi. Ni haƙiƙa na ganshi da malami na Mala'ika Jibrilu suna karatu cikin sama tare".
Bayan wannan sai Shehu Abdurrahman yace "Ya Shaihu Usmanu, ko kana da wata ƙasa ta abokan gaba wadda ka yaƙe ta amma baka ci ta ba?"
Sai Shehu yace masa "Ina da ita, na yaƙe ta har sau uku ban sami buɗinta ba har yanzu. Ita ce Gobir"
Sai Abdurrahman yace masa "Ka yarda mini in tafi in yaƙe su?"
Shehu Usmanu yace masa "na yardar maka"
Sai kuwa Shehu Abdurrahman ya fidda yaƙi gareta, yaje ya yaƙeta, yaci nasara, ya sami ganima, kuma dukkan fulani ma suka sami ganima.
Sa'an nan mutane suka cewa Shehu Usmanu "In ka bar Abdurrahman anan zai karɓe mulkin ƙasa duka daga hannun ka in baka maishe shi Nufe ba"
Sai kuwa Shaihu ya sallameshi bayan ya roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa.
Sa'an nan Allah ya fishshe shi daga ƙasar Hausa ya maishe shi ƙasar Nufe, ya fita daga gareta ranar laraba.
A zamanin da ya fita yana tare da dawaki saba'in, ya tasamma wani gari da ake ce masa Adusa. Ya gamu da jama'ar garin a Gabi ya yaƙe su, ya samu ganima dasu. Daga nan suka sake shiryawa suka tarbe shi gamuwa ta biyu a Adogudawa suka buga yaƙi, nan ma yaci su da yaƙi.
A wannan zamanin kuwa Sarkin Nufe da ake kira Etsu Ikaku bai fara sarauta ba, ana kiran sa da suna Manmachu. Kuma yana zaune a wani wuri da ake kira Kodagi bayan an tura shi yaƙi baici nasara ba yaƙi komawa gida, har ya gina babban gari a wajen ya zama sarki mai ƙarfin gaske.
No comments:
Post a Comment