TARIHIN NUFE: LABARIN SHEHU ABDURRAHMAN SHERIF
Kashi na uku
SADIQ TUKUR GWARZO
Ko da Manmachu (Etsun Nufe Ikaku) yaji labarin yaƙin Shehu Abdurrahman, sai ya ɗaura yaƙi da dawaki dubu talatin da biyu da ɗari biyu ya tunkare shi, suka buga yaƙi, nan ma Shehu Abdurrahman yaci galaba akansa.
Sa'an nan yaƙi ya sake aukuwa tsakanin su misalin wata biyu ba tare da sunyi galaba akan sa ba.
Shaihu Abdurrahman ya sauka da sansaninsa a ƙofar Daba, yace musu "Ku bi Allah, ku bi manzon Allah, ku bi ni". Suka bi shi zamani ƙanƙane. Sannan suka sake tayar da ƙayar baya, inda suka ce "Mu bamu bin Sarki mai zane da yawa a fuska tasa"
Shaihu ya taso da sansanin sa a Daba, ya tafi garin da ake kira Kere ya zauna acan. Yayi sarauta kamar shekaru uku, sannan ya ƙuduri gina gari.
Yana cikin wannan shawara sai Sarki Majiya ya amshi sarauta bayan mutuwar Etsu Ikaku. Ai kuwa ya taho da jama'a mai yawa don ya yaƙi Shaihu Abdurrahman.
Jama'ar Shehu Abdurrahman suka ce masa "Haƙiƙa Sarki Majiya ya zo da mutane masu yawa don su yaƙe mu". Sai ya ce musu "Ku rabu dashi"
Shaihu Abdurrahman ya zauna daga shi sai rigarsa a bisa tudu, cikin kasuwar Kere, yana karanta wasu takardu. Yaƙi ya auko Kere har ya shigo cikin gari, dakarun Majiya suka ƙwace ikon garin duka.
Sa'an nan sai Shehu Abdurrahman ya tashi daga kan tudun ya kwashe iyalin sa da dukkan dukiyar dake damfamin sa, ya fita izuwa wata fadama a wajen gari kusa da Kere wadda ake ce mata Jigi, ya ajiye iyalin nasa acan sannan ya koma gari.
Yace "Ba na son jama'ar musulmi masu yawa su halaka domina. Ina tsoron Ka da zunubinsu ya taru a wuyana, wannan al'amari dai daga ikon Allah ne maɗaukakin Sarki. Amma abinda nake roƙo a wurin Allah shine wani mutum ya kashe ni. In mutu dalilinsa."
Shaihu ya zauna har dakarun Majiya suka kewaye shi, amma babu wanda ya matsa kusa dashi saboda tsoro, bashi da wani makami sai takardun sa da yake karantawa. Kafin nan dama sai da yayi taimama yayi sallah raka'ah biyu ta fuskar gabas, yayi raka'o'i biyu a fuskokin yamma, kudu da arewa, sannan bayan sallama ya kwanta, ba riga jikinsa sai mayafi, yace musu "Ku zo ku kashe ni domin Allah".
Wani mutum da ake cewa dashi Chado shine ma'abocin magani, shine dogarin Sarkin Nufe Majiya, ya kusanci shehu Abdurrahman ya yanka shi, har ya datse kansa. A wannan lokaci ciwo ya sami hannunsa domin kisansa, idanuwansa sukayi cizara.
A wata maganar ance wanda ya ɗauko kan Shehu Abdurahman ya kaiwa Sarki Majiya albaras ta ɓata hannuwansa.
Shikuwa Sarki Majiya sai ya sanya Kan cikin farin bargo mai geza, ya tafi ya ajiye shi ajiya mai kyau, daga baya ya umarci mutanen sa su jefa shi a kogin kaduna.
An kashe Shehu Abdurrahman ranar alhamis, da hantsi, shekarar hijirar Annabi Muhammadu s.a.w dubu da metan da talatin da huɗu. Shi yana cikin turbar ƙadiriyya ne, ya zama sarki waliyyi maɗaukaki.
Daga nan sai Sarki Majiya ya rinƙa ɗaukaka kansa, yana hura hanci, yana baiyana girman kai domin kisan sa ga Shehu Abdurrahman. A lokacin kuwa Mallam Dando (wanda za a ji labarin sa nan gaba kaɗan) yana cikin tawagar sarkin. Don haka da yaga abinda aka yiwa Shaihu Abdurrahman, sai ya gudu ya tafi cikin Juguma ya zauna acan. A zamanin girman waliyyantakarsa bai bayyana ba a ƙasar Nufe".
Kashi na uku
SADIQ TUKUR GWARZO
Ko da Manmachu (Etsun Nufe Ikaku) yaji labarin yaƙin Shehu Abdurrahman, sai ya ɗaura yaƙi da dawaki dubu talatin da biyu da ɗari biyu ya tunkare shi, suka buga yaƙi, nan ma Shehu Abdurrahman yaci galaba akansa.
Sa'an nan yaƙi ya sake aukuwa tsakanin su misalin wata biyu ba tare da sunyi galaba akan sa ba.
Shaihu Abdurrahman ya sauka da sansaninsa a ƙofar Daba, yace musu "Ku bi Allah, ku bi manzon Allah, ku bi ni". Suka bi shi zamani ƙanƙane. Sannan suka sake tayar da ƙayar baya, inda suka ce "Mu bamu bin Sarki mai zane da yawa a fuska tasa"
Shaihu ya taso da sansanin sa a Daba, ya tafi garin da ake kira Kere ya zauna acan. Yayi sarauta kamar shekaru uku, sannan ya ƙuduri gina gari.
Yana cikin wannan shawara sai Sarki Majiya ya amshi sarauta bayan mutuwar Etsu Ikaku. Ai kuwa ya taho da jama'a mai yawa don ya yaƙi Shaihu Abdurrahman.
Jama'ar Shehu Abdurrahman suka ce masa "Haƙiƙa Sarki Majiya ya zo da mutane masu yawa don su yaƙe mu". Sai ya ce musu "Ku rabu dashi"
Shaihu Abdurrahman ya zauna daga shi sai rigarsa a bisa tudu, cikin kasuwar Kere, yana karanta wasu takardu. Yaƙi ya auko Kere har ya shigo cikin gari, dakarun Majiya suka ƙwace ikon garin duka.
Sa'an nan sai Shehu Abdurrahman ya tashi daga kan tudun ya kwashe iyalin sa da dukkan dukiyar dake damfamin sa, ya fita izuwa wata fadama a wajen gari kusa da Kere wadda ake ce mata Jigi, ya ajiye iyalin nasa acan sannan ya koma gari.
Yace "Ba na son jama'ar musulmi masu yawa su halaka domina. Ina tsoron Ka da zunubinsu ya taru a wuyana, wannan al'amari dai daga ikon Allah ne maɗaukakin Sarki. Amma abinda nake roƙo a wurin Allah shine wani mutum ya kashe ni. In mutu dalilinsa."
Shaihu ya zauna har dakarun Majiya suka kewaye shi, amma babu wanda ya matsa kusa dashi saboda tsoro, bashi da wani makami sai takardun sa da yake karantawa. Kafin nan dama sai da yayi taimama yayi sallah raka'ah biyu ta fuskar gabas, yayi raka'o'i biyu a fuskokin yamma, kudu da arewa, sannan bayan sallama ya kwanta, ba riga jikinsa sai mayafi, yace musu "Ku zo ku kashe ni domin Allah".
Wani mutum da ake cewa dashi Chado shine ma'abocin magani, shine dogarin Sarkin Nufe Majiya, ya kusanci shehu Abdurrahman ya yanka shi, har ya datse kansa. A wannan lokaci ciwo ya sami hannunsa domin kisansa, idanuwansa sukayi cizara.
A wata maganar ance wanda ya ɗauko kan Shehu Abdurahman ya kaiwa Sarki Majiya albaras ta ɓata hannuwansa.
Shikuwa Sarki Majiya sai ya sanya Kan cikin farin bargo mai geza, ya tafi ya ajiye shi ajiya mai kyau, daga baya ya umarci mutanen sa su jefa shi a kogin kaduna.
An kashe Shehu Abdurrahman ranar alhamis, da hantsi, shekarar hijirar Annabi Muhammadu s.a.w dubu da metan da talatin da huɗu. Shi yana cikin turbar ƙadiriyya ne, ya zama sarki waliyyi maɗaukaki.
Daga nan sai Sarki Majiya ya rinƙa ɗaukaka kansa, yana hura hanci, yana baiyana girman kai domin kisan sa ga Shehu Abdurrahman. A lokacin kuwa Mallam Dando (wanda za a ji labarin sa nan gaba kaɗan) yana cikin tawagar sarkin. Don haka da yaga abinda aka yiwa Shaihu Abdurrahman, sai ya gudu ya tafi cikin Juguma ya zauna acan. A zamanin girman waliyyantakarsa bai bayyana ba a ƙasar Nufe".
No comments:
Post a Comment