Friday, 8 March 2019

TARIHIN NUFE: LABARIN SHEHU ABDURRAHMAN SHARIFI 1

TARIHIN NUFE: LABARIN SHEHU ABDURRAHMAN SHERIF
Kashi na ɗaya
SADIQ TUKUR GWARZO
Kafin muji labarin asalin Nufe da tarihin ta, zamu fara jin labarin Shehu Abdurrahman al Sherifi ne, shahararren masani kuma mayaƙi ɗan ƙasar Nufe.
Alƙalin Nufe Ummaru ɗan Muhammadu  Allah ya rahamsheshi ya bamu labarin da mahaifin sa ya sanar dashi game da Shaihu Abdurrahman ɗan Muhammadu Sharifi bawan Allah.
  Yace " Mahaifinsa Muhammadu Sharifi balarabe ne, zamanin da faɗa ya auku tsakanin larabawa da turkawa a wajajen ƙarni na goma sha takwas, sai Muhammadu Sharifi ya gudu tare da ƙetare kogi mai zartsi ya shiga ƙasar Nufe, ya zauna a cikinta lokaci mai tsawo.
   Sa'an nan sai ya zauna a ƙasar Abaji ya daɗe.
Akwai wani malami a ƙasar Abaji yana da ƴa Mace kyakkyawa, sai ya ba da ta sadaka ga Muhammadu Sharifi domin neman ladan Allah.
  Bayan Muhammadu Sharifi ya tara da amaryarsa, sai ta samu ciki, daga nan kuma sai ya bar wannan gari zuwa wani wuri daban, ya zauna lokaci mai tsawo acan har matar sa ta haihu yaro ya girma. Aka sanya masa suna Abdurrahman.
 Rannan sai kakan sa yake tambayar sa "kai ina uban ka ne?"
Sai yaro yace "ai ni ban taɓa ganin ubana ba, amma In Allah yaso, kana ganin sa gobe da hantsi".
 Sai kakan yace " idan ubanka yazo ka ganshi zaka gane shi?". Yaro yace "in yazo, na san shi in Allah yaso". Kakan yace ''su wanene dangin ubanka, Bahaushe ne ko Banufe?" Yaro yace ''Haƙiƙa ubana Balarabe ne, sharifi, kakansa kuwa Alassan ne ɗan Ali ɗan Abi Dalibi, Allah ya girmama fuska tasa"
Ai kuwa abinda yaro ya faɗa ne ya auku, sa'ad da yaro ya ga ubansa sai yace " Marhaba da ubana! Barka da komowa daga ziyara! Ka sani ƙasarmu ba irin ƙasar ku bace: ƙasar ku ta larabawa ce"
 Sai kuwa mahaifinsa yayi mamakin abinda yaji daga gare shi. Yace masa " wa ya sanad dakai ni ba mutumin nan ƙasar bane?"
 Yaro yace masa " Wanda ya halicce ni ya sa ni acikin tsatsonka ya goye ni, shine ya sanad da ni maganar nan da na faɗa maka"
  Sa'an nan ubansa yace" wa ya sanad dakai karatu?" Sai yaro yace "Wanda ya halicce ni ya shiryad dani madaidaiciyar turba, shi ne ya sanad dani"
Daga nan sai Uban ya zauna tare dasu tsawon watanni uku, sannan yace wa ɗan nasa " Ina son in koma wurin da na fito, watau ƙasar larabawa".
Ɗansa Abdurrahman yace " In Allah ya yarda ba mu ƙara gamuwa bayan wannan rana har zuwa ranar ƙiyama"
 Ubanshi ya bar shi a wurin uwa tasa ya tafi. Ɗan uwanta shine wanda ya kai shi makaranta a cikin Ebugi.
  Da ya tafi makaranta sai yaƙi yin karatu, idan malamin sa yace masa "Yi karatu", sai shima yace "Kai ma kayi karatu".
A zamanin da yaro ya nufi nunawa malamin sa yana da karatu, sai yace masa "Ina son ka tara malamai a gidanka"
Ai kuwa malami ya tara malamai kamar yadda yaro ya buƙata. Dukkan su suna ɗauke da takardun Alƙur'ani maigirma. Sannan yaro ya soma karatu tiryan-tiryan da ka.
  Daga wannan rana malaman garin duk suka gane yaron yana da karatu, kuma suka san cewa shi waliyyi ne daga waliyyan Allah maɗaukakin sarki.
Akwai wani zane mai yawa a kunduƙuƙinsa na hagu, Nufawa na kiran zanen da suna 'Benuwa'. Akwai kuma wani a kundukukin sa na dama, ana ce masa 'Banguba' da Nufanci. Sai kuma wani tukku a tsakiyar kansa da Nufawa ke kiransa da suna 'Kuturma'.
  Malam Abdurrahman yayi addua cewa 'Na roƙi Allah ya shafe dukkan zanuka da yake fuskokin mutane ranar alƙiyama, ban da zanen fuskata, domin itace alama ta a ranar alƙiyama'.
A zamanin da ya nufi mulkin duniya, ya kan hau jaki ya tafi ya dakace turbar kafirai waɗanda suke dawowa daga kasuwa yayi musu fashi. Idan kafirai sun biyo shi, suka iske shi a turba, idan yayi musu tsawa sai wuta ta riƙa fita daga cikin bakinsa tana binsu tana kora su suna guje mata.
A zamanin da shekarun sa suka yi yawa har ya balaga, sai yayi nufin tafiya ƙasar Hausa bayan ya kai hari ƙasar Bida dake cikin ƙasar Nufe.
A duk inda ya samu kafirai a hanya sai ya yaƙe su, har ma ance yayi yaƙi da garuruwa bakwai bakwai na kafirai, sannan ya zarce ya tafi Sakkwato domin ziyarar Shaihu Usmanu, hasken zamani, fitilar addini, kambin yamma, babban waliyyi.
  Ko da isar sa Sakkwato sai yace wa Shehu Usmanu "Ni nazo karatu ne gareka ya Shaihun mu, malamin addini".
   Sai Shehu Usmanu yace masa "Tafi wurin Abdullahi kayi karatu a wurin sa".
  Daga nan sai ya cira ya tafi Gwandu, ya sauka wurin shehu Abdullahi wanda ya girmama shi tare da saukar dashi a masauki mai kyau.
Bayan wannan, sai Shehu Abdurrahman yace da Shehu Abdullahi "Ni ina so in yi karatu ne a wurin limamin mu, shehu Usmanu mai sabunta addini. Amma yace ba shi da sukuni, ya maishe ni gareka".
  Sai Shehu Abdullahi yace masa "Ko kasan Balaga da Ma'ani da Badi'i?"
  Abdurrahman yace "duka waɗannan fannonin na sansu.
Sai Abdullahi Gwandu yace masa "Ko kasan Tasifi da Tauhidi da Tafsirin Alƙur'ani?"
Abdurrahman yace "duka na san waɗannan turbobin da ka faɗa"
  Sai ya sake tambayar sa da cewa "Shin kasan Aya mai shafe Aya, da wadda aka shafe, da ma'anonin su da kuma wuri wanda yake da fassarori da yawa?"
Nan ma sai Abdurrahmanu yace "duk na sansu, har ma na san Tafsirin Alif Lamin, da Yasin, da Nun, da Sad, da Ƙaf da sauran su duka"
Daga nan sai Shehu Abdullahi Gwandu yayi shiru ya ƙyale shi.

No comments:

Post a Comment