Friday, 8 March 2019

IKON ALLAH: HALITTAR ZANZARO

IKON ALLAH: HALITTUN GIDA DA NA DAJI
1. ZANZARO, ISHARA GA MAI LURA
  Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai.
A wannan makon cikin ikon Allah zamu buɗe wannan fili ne da nazarin hikimomin da Allah Ta'ala ya ajiye wa zanzaro.
  Babban abin mamaki ga zanzaro shine, kullum za ka ganshi su biyu tare da matarsa.
   Lokacin da matar ta kusa yin ƙwai, shi mijin ya sani, don haka za ka gan shi yana ta zirga-zirga.
Da farkon farawa sai ya sami wani wuri cikin ɗaki ya ɗebo ɗanyar ƙasa a ko'ina ne ya same ta, domin gina gida.
    To a cikin bakinsa akwai wani ruwa mai danƙo da yake shafawa ƙasar a lokacin da yake ginin.
   Za ka ga ya yi ginin nasa hawa-hawa har ya ƙare dai-dai yawan ƙwayayen da mai ɗakinsa za ta yi. Kuma daga cikin ɗakunan yana yin wata farar shimfiɗa mai taushi.
Daga yin wannan, sai ya sanar da matarsa. Ita kuma babu wata wata sai aga ta shiga zuba ƙwai.
Da zarar ta ƙare, sai ya je ya samo tsutsotsi masu rai ya zuba cikin ɗakunan.
 Wani babban abin mamakin ma shine, a bayan sa akwai wani abu mai tsini kwatankwacin allurar likita ɗan tsirit da shi.  Wanda acikin sa akwai wani ruwa daidai da ruwan allurar da likitoci ke yiwa marar lafiya yayin da za a gudanar masa da aikin tiyata, wadda take ɗauke masa raɗaɗi gami da sanya shi bacci.
Sai zanzaron yabi duk tsutsotsin nan yayi musu waɗannan allurori, sannan sai ya cusa su ɗakunan da matarsa ta zuba ƙwayayen ta.
Daga nan sai ya ɗebo sabuwar ƙasa ya liƙe ƙofar ɗakin ya yi tafiyar sa tare da matarsa.
Bayan wasu kwanaki kaɗan sai ƙwayayen nan su ƙyanƙyashe kansu, sannan su cinye naman tsutsotsin nan domin da ma ba su mutu ba balle su ruɓe su zamar musu cuta.
Ba da jimawa ba sai kaga jira-jiran zanzaro sun girma a wannan ɗaki mai matsatsi, sannan su yunƙura da ƙarfi wadda zata sa ɗakin ya fashe tare da ficewa daga cikin sa.
Wani abin ta'ajibin a nan shine, su waɗannan ƴaƴan zanzaro idan lokacin yin ƙwansu ya zo haka suma zasu yi duk kuwa da cewar ba su tarar da iyayen su ba balle ace a wajen su suka koya.
Sannan, yadda namijin zanzaro ke yiwa matarsa hidima shima abin koyi ne matuƙa ga dukkan ɗan Adam.
Don haka lalle akwai hikimomi a tattare da wannan halitta ta ubangiji wadda idan mutum ya natsu ya gane, zai ƙara jin tsoron Allah gami da kiyaye haddodin sa, domin shi mai iko ne a kan komai.
An ciro ne daga Littafin HIKAYOYIN KAIFAFA ZUKATA NA 2 Wanda Mallam Aminu Kano ya rubuta.
Insha Allah, a wani makon zamu taɓa wata halittar ta da ban. 

No comments:

Post a Comment