LABARIN ZUWAN KWARARRAFAWA BIRNIN KATSINA
A ƙarni na goma sha shidda, zamanin mulkin Sarkin Katsina Jan Hazo, ance kwararrafawa sun kawo yaƙi birnin katsina.
Sarkin su ya sauka a yammacin gari a Babbar Ruga, yayin da wazirin sa ya sauka a gabashin gari.
Sarkin kwararrafawa ya kama mashin sa ya girgiza sannan ya jefa shi cikin gari, aikuwa sai mashin ya faɗa can tsohuwar Kasuwa kusa da kududdufin Tafkin Daule, inda wuta ta kama nan take.
Daga nan sai sarakunan Katsina suka taru a wurin Sarkin Katsina Jan Hazo, sukayi shawarar su fita daga garin in yaso wanda zai samu tsira ya tsira.
Bayan nan sai suka aikawa Mallam Ɗan Masani shawarar da suka yanke, shikuwa sai ya gayawa matarsa ta yi shiri su fita daga gari.
Ita kuma sai tace 'ni da bani fita ko da dare, don haka ba zan fita da rana ba'.
Sai yayi mata faɗa, sannan ya aikawa Sarkin Katsina da cewa kada su fita daga gari har sai sun ga abinda Allah zai yi dasu, ya shiga roƙon Allah ya ɗauke musu wannan bala'i.
Da dare sai Sarkin Kwararrafawa ya tashi don ya duba dokinsa, sai kuwa doki ya shure shi a wajen cibiyarsa, ya faɗi yana shure-shure, kafin a jima ya mutu. Aka baiwa wazirin sa labarin abinda ya auku, sai ya hau dokin sa domin yaje ya gano, sai kuwa dokin ya kayar dashi, wuyan sa ya karye ya mutu.
Haka kuma acikin daren nan manyan-manyan sarakunan su duk sai da suka mace. Yaƙin su ya ƙare, suka tashi.
Sarkin Katsina Jan Hazo yazo gun Mallam Ɗan Masani yayi durƙushe yana godiya, yayi masa alƙawarin kowa yazo gidan sa don kamun ƙafa ya tsira, koda kuwa kisan kai yayi.
A ƙarni na goma sha shidda, zamanin mulkin Sarkin Katsina Jan Hazo, ance kwararrafawa sun kawo yaƙi birnin katsina.
Sarkin su ya sauka a yammacin gari a Babbar Ruga, yayin da wazirin sa ya sauka a gabashin gari.
Sarkin kwararrafawa ya kama mashin sa ya girgiza sannan ya jefa shi cikin gari, aikuwa sai mashin ya faɗa can tsohuwar Kasuwa kusa da kududdufin Tafkin Daule, inda wuta ta kama nan take.
Daga nan sai sarakunan Katsina suka taru a wurin Sarkin Katsina Jan Hazo, sukayi shawarar su fita daga garin in yaso wanda zai samu tsira ya tsira.
Bayan nan sai suka aikawa Mallam Ɗan Masani shawarar da suka yanke, shikuwa sai ya gayawa matarsa ta yi shiri su fita daga gari.
Ita kuma sai tace 'ni da bani fita ko da dare, don haka ba zan fita da rana ba'.
Sai yayi mata faɗa, sannan ya aikawa Sarkin Katsina da cewa kada su fita daga gari har sai sun ga abinda Allah zai yi dasu, ya shiga roƙon Allah ya ɗauke musu wannan bala'i.
Da dare sai Sarkin Kwararrafawa ya tashi don ya duba dokinsa, sai kuwa doki ya shure shi a wajen cibiyarsa, ya faɗi yana shure-shure, kafin a jima ya mutu. Aka baiwa wazirin sa labarin abinda ya auku, sai ya hau dokin sa domin yaje ya gano, sai kuwa dokin ya kayar dashi, wuyan sa ya karye ya mutu.
Haka kuma acikin daren nan manyan-manyan sarakunan su duk sai da suka mace. Yaƙin su ya ƙare, suka tashi.
Sarkin Katsina Jan Hazo yazo gun Mallam Ɗan Masani yayi durƙushe yana godiya, yayi masa alƙawarin kowa yazo gidan sa don kamun ƙafa ya tsira, koda kuwa kisan kai yayi.
No comments:
Post a Comment