Tuesday, 21 December 2021

MATSAYIN YESU KIRISTI: ƊAN UBANGIJI KO KUWA 'DAN AIKEN SA NE?

 MATSAYIN YESU KIRISTI: ƊAN UBANGIJI KO KUWA 'DAN AIKEN SA NE?

  

SADIQ TUKUR GWARZO

    


A duk Ranar 25 ga watan disamba na kowacce shekara, mabiya addinin Yesu Kiristi suna bikin tunawa da ranar Haihuwar Annabi Isa A.S

  Haka kuma, Mabiya addinan Islama da na kiristanci, dukkansu sun amince da wanzuwar Yesu Almasihu, kuma suna darajanta shi.

  Sai dai, yadda mabiyan kowanne daga addinan biyu suka ɗauka game dashi na da bambamci.

   A addinin musulunci, ya zo cewa Yesu Kiristi Mutum ne mai daraja, wanda Ubangiji Allah abin yiwa bauta ya aiko domin yayi wa'azi da kaɗaita shi.

  Haka kuma mahaifiyarsa, an yabeta a matsayin mace mai gaskiya. A duba Alkur'ani (3:45) da (19:17)

   Sai dai a kiristance, ba haka abin yake ba.

   Domin kuwa da yawan mabiya addinin suna ɗaukar Yesu Almasihu a matsayin Ubangiji, yayin da wasu ke ɗaukarsa a matsayin ɗa-ga Ubangiji.

   Don haka, wannan saɓani, zai warwaru ne kurum idan mukayi duba izuwa littattafai masu tsarki na waɗannan addinai guda biyu.

  Da fari dai, acikin Suratu Maryam cikin littafin Alqur'ani mai girma, maganar Ubangiji ta faɗi labarin yadda aka haifi Yesu kiristi ba tare da Uba ba, har mutane ke tuhumar mahaifiyarsa da cewa "yake 'yar uwar Haruna, hakika kinzo mana da bakon abu, gashi kuwa mahaifinki ba fasik'i bane, mahaifiyarki kuma ba mai bin mazaje bace".

   Sai kuwa Maryamu tayi musu nuni da Jaririn tana nufin su nemi ba'asi daga gareshi. Har suke cewa gareta "tayaya zamuyi magana fa wanda ya ke cikin zanin goyo?"

  Ai kuwa Sai Yesu Almasihu da ke zanin goyo ya amsa da cewar "Ni bawan Ubangiji (Mai suna Allah) ne, ya bani littafi ya kuma sanyani Annabi".

   "Ya sanya albarka a gareni a duk inda na kasance, yayi mini wasicci da Sallah da Zakkah matukar ina raye".

  "Kuma aminci ya tabbata a gareni a ranar haihuwata, da ranar mutuwata, da ranar da za'a tashe ni rayayye".

  Sai Ubangiji yace "wannan fa shine Isa Dan Maryamu.."(karanta har karshen Aya)

 Maryamu: 26-34


A littafin Babil mai tsarki, nan ma ana iya cewa yazo a wurare daban-daban cewar Yesu Almasihu ba shine Ubangiji ba.

   Sahabban Yesu kiristi irinsu Matthew, Mark, da Luke waɗanda suka ruwaito zantukan sa har suka haɗa zantukan izuwa littafin Babil, sun tafi akan cewa Yesu kiristi bai taɓa kiran kansa da suna Ubangiji ba. A duba Matthew 10:18, da Matthew 19:17.

   Abinda wasun su suka yadda shine: shi ɗan Ubangiji ne, saboda haihuwarsa da akayi babu uba da kuma karamomin da ya nuna a zamanin rayuwarsa.

   Haka kuma, ɗaukarsa a matsayin ɗan Ubangiji na nufin kasancewarsa Mutumin kirki nagartacce, don haka ba shi kaɗai ba, duk wani nagartaccen bawa su kan kira shi 'ɗan Ubangiji'. A duba Matthew 23:1-9 don a tabbatar.

   Shikuwa Paul, wanda shima Maruwaicin Babil ne, ya aminta da cewar Yesu Kiristi ba Ubangiji bane.

  A cewar sa, Yesu kiristi ne wanda Ubangiji ya soma halitta, don haka yayi amfani da shi wajen halittar sauran halittu kamar yadda yazo a Colossians 1:15 da 1 corinthians 8:6.

     Saboda haka, kasancewar Paul, John da sauran manyan maruwaitan littafin Babil mai tsarki, sun tafi akan cewar Yesu Almasihu shine halittar Ubangiji na farko kuma mafi daraja, har ma Paul ɗin ya ruwaito a Babil cewa yaji Yesu na faɗin "The Father is greater than I". Watau "Uban, ya fificeni" sai waɗanda suka biyo bayansu sukayi shishshigin ɗora masa laƙabin shi ɗan ubangiji ne, wasu kuma suka ce shi Ubangiji ne kachokan.

  Ga kaɗan daga ayoyin Babil da suke nuna Yesu Kiristi ba Ubangiji bane, bawan Ubangiji ne kamar yadda muka kawo Yesu ɗin ya faɗa da bakinsa daga Alkur'ani:-

   "Men Of Israel, listen to this:Jesus of Nazareth was a Man accredited by God to you by miracles.." Acts 2:22

 "God Has raised this Jesus"

 Acts 2:32

 "God Raised up his Servant"

 Acts 3:26

  "The Lord of Abraham, Isaac, and Jacob, the Lord of our fathers, has your holy servant Jesus"

 Acts 3:13

  A wani kaulin ma, shi da kansa Yesu Almasihu ya faɗi cewa bai san ranar da za'a tashi alkiyama ba, don haka shi fa bawan Ubangiji ne (Matthew 24:36).

 A Wani wajen kuma an ruwaito Yesu Kiristi yana neman taimakon 'Eloi', ko 'Eloh' wajen tabbatuwar ayyukansa, kamar yadda akace ya faɗa yayin da Yahudawa zasu halaka shi cewa "ELOI, ELOI, LAMA SABACHTANI  (Markus 15:34. ) 

Ma'ana,  "Ubangijina,  Ubangijina, don me ka yasassheni?"

  Don haka, idan har Yesu ya kasance ubangiji, me zaisa ya rinka neman taimakon wani kuma, sannan me zaisa ya rinka faɗawa mutane da kansa cewar shi bawa ne ga ubangijinsa ELOHIM?

  Koda yake, wannan ƙin gaskiyar karamin aiki ne ga manyan malamai mabiyansa idan muka kalli Babil, Song of Songs (5:16), inda kai tsaye akayi busharar zuwan wani Annabi mai suna 'מַחֲמַדִּים' cikin harshen yahudawa (wanda aka fassara haruffan da m-ħ-m-d-y-m, ake kuma furtasu da meħmadim ko

maħammaddīm don girmamwa bisa karin 'im'), amma kai tsaye sai sukace sam kalmar ba Annabi Muhammad take nufi ba, wai tana nufin wani wanda kowa keso ne ko kuma wani mafi cancanta..


MENENE SUNAN SA?

Marigayi Sheikh Ahmad Deedat ya yi dogon nazari akan sunan Ubangiji kamar yadda yazo a cikin littafin Babil mai tsarki har ya wallafa littafi a game da haka wanda ya sanyawa suna 'MENENE SUNAN SA?, ga kaɗan daga abinda shehin Malamin ya ke cewa:-

Akwai wasu Mutane 'yan ɗarikar Jehovah daga cikin ɗarikun kiristoci masu zagayawa gida-gida ga 'yan uwansu kiristoci suna tambaya menene sunan sa? (Suna nufin menene sunan Ubangiji)

 Sai kaji kirista yace "Ubangiji"

  Sai suce "Ubangiji ai ba suna bane, abin bauta ne".

  Sai su kara tambaya, "to menene sunan sa?"

  Sai kaji kirista yace "Sunan sa Uba (Baba God)"

  Sai suce masa "shin Ubanka Ubangiji ne?"

  Nan take kirista zaice "A'a".

  Sai su sake tambayarsa, "to menene sunan sa?"

  Idan yayi shiru babu amsa, sai suce  "Jehovah shine sunan sa".

  Waɗannan kalmomi guda huɗu da ake kira Tetragammation, sun hana kowa yabisu dalla-dalla don zakulo asalin ma'anarsu.

   Amma idan ka tambayesu, menene 'Je-ho-va-h', sai suce maka 'Y-H-W-H', watau kalmomi huɗu da suka zo a littafin Babil mai tsarki na yaren Ibraniyanci.

  Kasancewar tsohon rubutun Ibraniyanci da Larabci babu wasulla, waɗancan kalmomi na YHWH (ko JHWH saboda matsalar J da ake sauyata da Y a larabci, kamar misalin Jacob da Yakub, Jesus da Yesus, Joseph da Yusuf, W kuwa har yau a wasu yarukan da lafazin V suke ambatonta) kaɗai sunzo da maimaicin akalla sau 6,823 acikin Babil.

 Saboda haka, mabiya ɗarikar jehovah sun gamsu cewar Kalmar JHVH (YHWH) sunan Ubangiji ne daya kira kansa da kansa a littafi mai tsarki sama da sau dubu shidda, to amma kalmar ELOHIM (YHWH ELOHIM) ce ke tare da waɗancan haruffa a mafi yawan lokuta.

   Idan muka kalli kalmar 'ELOHIM', zamuga kalmomi ne biyu a haɗe, watau ELOH da kuma IM.

  Da Fari, ita IM, ɗango ne na girmamawa ga ELOH a yaren Annabi Ibrahim A.S. misali, idan za'ace Ibrahim yana da girma, sai a kara masa IM, ya zamo 'Ibrahimim', kamar yadda idan aka lura har yanzu yaren yahudanci da wasu yaruka na bin wannan tsari.

   Saboda haka 'ELOH' shine sunan, wanda shima zamu gane ainihinsa idan muka kalli yadda Larabci ke kiran duk abinda Ibraniyanci ya kira da 'EL' da lafazin 'AL'.

  Don haka, kalmar 'Eloh' ta yaren Ibraniyanci na nufin 'Aloh' kenan a larabci.

  Kalmar da idan mukaci gaba da mai-mai-ta-ta a zukatanmu zamuga ta sauya daga Eloh, Eloh, Zuwa Aloh Aloh.. Zuwa Allah Allah..

 Wannan ke nuni da cewa kalmomin 'YHWH ELOHIM' da suka zo a Babil na Ibraniyanci ba komai suke nufi ba sai 'YA HUWA ALLAH' a larabci, kusan Aya kenan ta farko a Suratul Ahad, da Ubangiji yace "Qul Huwallah..." (watau kace shine Allah)

   To waɗannan kalmomin fa, sune sukazo a Babil sama da sau dubu shidda.. Abinda Allah ke faɗawa Manzonsa Annabi Isah A.S shine "ka sanar musu da cewa Ubangijinka Shine Allah.." Kuma abinda Yesu Kiristi yayi ta sanarwar kenan, amma har zuwa yanzu Ubangiji baisa 'yan uwanmu kiristoci sun gane cewar Allah ne sunan ubangiji abin bauta da gaskiya ba.

   Marigayi Sheik Ahmad Deedat Rahimahullah yana Cewa dangane da wannan batu "Idan da Malaman kiristoci zasu sanar da Mabiyansu wannan abu, tabbas da lokaci yayi wanda musulmai da kiristoci zasu haɗu wajen bautawa Ubangiji makaɗaici".

   Daɗi akan haka, shine kalmar nan ta ELLELUYA, wadda babu kiristan dabai santa ba.

  Har ma sukan ambace ta aduk sanda suka so godewa Ubangiji, kamar yadda Musulmai ke faɗin Allahu Akbar don tsarkake Ubangiji.

   Ya kuwa ishemu misali idan muka kalli kalmar Ibraniyanci ta ELLELU-YA muka musanya ta da zubin larabci izuwa ALLELU-YA.. (muka sauya EL da AL)

  Sai mu kalli waɗannan kalmomi:-

  ALLELU YA

  YA ALLELU 

  ALLAHU YA 

  YA ALLAHU

  Ku tambayi kanku, don girman Allah akwai banbanci ko babu?

  Sheikh Deedat, Zakir Naikh da sauran malumman musulunci duk sun tabbtar da cewa Ya Allahu shine asalin Kalmar Elleluya.

  Don haka, aduk sanda kaji malaman kiristoci na faɗin "Praise the Lord!" sukuma suna amsawa da "ElleluYa!!!" kasani cewa "Ya Allahu" kurum suke ambata a sauye.

  Allah da aka ambata a Linjila, shine aka sake ambata a Alqur'ani mai tsarki, amma k'alilan daga mutane ke fuskantar haka.

  Hakika, Tsarki ya tabbata ga Ubangiji mai tsarki da Buwaya. Allah kayi daɗin tsiranka ga Shugabanmu Annabi Muhammad (s.a.w) da sauran Annabawan Allah masu tsarki. Amin.

Tuesday, 14 December 2021

KWAZAZZABON YAR KWANDO

 LABARI NA GASKIYA DANGANE DA KWAZAZZABON 'YAR KWANDO



Labari na gaskiya dangane da Kwazazzabon 'Yar Kwando da kuma saukar Shehu Mujaddadi a K'asar Dugabau.

Daga Sadiq Tukur Gwarzo

Hakika Labarin da ake fada dangane da kwazazzabon 'yar kwando gaskiya ne. Ita 'yar kwandon ai aljana ce, watakila tana cikin jinsin fararen aljannu don kuwa bamu samu labarin wani data taɓa cutarwa ba.

Amma dai mutanen Dugabau dake ƙasar Kabo ta jihar Kano sun bada shaidar cewa ana yawan haɗuwa da Aljanna 'yarkwando a daf da wannan kwazazzabon.

Akwai wanda yace min takan fito da sigar tsohuwa ko Budurwa, har ma zata iya neman wani taimako daga gareka, ko ka ganta tana wani uzuri nata, amma dai ba zata yarda kaga fuskar ta ba.

Ance ta taɓa fitowa wani mutum a siffar tsohuwa, sai tace masa ya taimaka ya tsallakar da ita ta haye ruwa, amma sai mutumin yaƙi. Juyawar da zaiyi sai hangota yayi kanta a cikin ruwa, ƙafufuwanta suna kaɗawa a sama, a haka ta tsallake ruwan.

Wani mutum kuma mai noman rani a daf da wannan kwazazzabo ya shaida min cewa suna yawan ganin abubuwan mamaki dangane da aljanna Ƴar kwando. Har yace min ba'a yi musu satar amfanin gona, domin kuwa ita aljanar ke musu gadi, sannan kuma yace gidan ta yana kusa da wani ƙaton rimi da aka sare acan kan tudu idan an haye ruwa, ragowar surkukin kuma na ɗauke ne da gidajen 'ya'yanta.

Shi dai wannan kwazazzabo da ake kira 'kwazazzabon 'yarkwando' a kusa da garin Dugabau din yake, waje ne mai girman gaske dake hayin ƙorama, yana da tarihi kuma, domin kuwa anan ne akace magoya bayan Shehu Usmanu Bn Fodio (Allah yajikan sa da rahama) suka taɓa sauka a sa'ar da ake buga yaƙin Jihadi a k'asar hausa (wajajen 1804).

Marubuci Ibrahim Bala Gwarzo ya ruwaito a littafinsa 'Mazan kwarai' cewa a wannan wuri mai suna kwazazzabon Yarkwando Shehu Usmanu ya sauka ya huta ya kuma ƙara ƙarfin rundunar sa. Daga nan ya afkawa masarautar Karaye da yaƙi, sannan ya afkawa birnin kano.

Tarihi ya tabbatar mana da cewa Shehu Usmanu Danfodio bai sauka a wannan yanki na Dugabau ba, amma magoya bayan sa Malamai da suka jagoranci yaƙi da Sarkin Kano na zamanin watau Alwali, anan suka yi hijira tare da haɗa gagarumar rumduna.  Zuwa yanzu dai akwai tsohon masallacin jumu'a da magoya bayan shehun suka buɗe wanda akace wani mutum mai suna Isyaka ne ya gina shi acikin garin na Dugabau. Sama da shekaru ɗari da tamanin da faruwar wannan lamari, wannan masallaci ne babba a yankin, saboda an gina shi ya ginu, an kuma ƙawata shi da ado dai-dai da wayewar maginan ƙasa na wancan zamani.

Na tambayi wani Tsoho akan ko zamu samu wata shaida takamaimiya wadda aja taskance kamar misalin Littafi Alkur'ani maigirma, takobi ko wani abu wanda ya fito daga magoya bayan shehu Usmanu mujaddadi a halin saukar su a wannan yanki ?.. Sai dai hakan bai samu ba, watakila saboda jimawar zamani ko kuma gushewar Dattijan da suka kiyaye ainihin abinda ya faru a wancan zamanin gwargwadon yadda suka samu labari, amma dai ya tabbatar min da ingancin wannan labari, ya kuma k'aramin da cewa akwai wata Katuwar kuka mai suna 'JARMA' (wadda a yanzu ta fadi da kanta) wadda ke daura da kwazazzabon 'yarkwando, itama ada can jarumai da sarakunan kasar Katsina na sauka a wurinta kafin su riski birnin Kano don kai harin yaƙi ko aiwatar da wata buƙata tasu.

Shikuwa kwazazzabon 'yarkwando, nan ne filin yaƙin da aka gwabza gagarumin faɗan nan da ake ambata da suna 'YAƘIN ƊAUKAR GIRMA', wanda gagarumar runduna ta taso daga kano da nufin murƙushe tsirarun mayaƙan da suka yi hijira zuwa wurin masu biyayya ga Shehu Usmanu Danfodio, amma cikin ikon Allah sai ƙaramar rundunar ta samu galaba gagarima akan waccan gagarumar runduna.

  Labari ya samu gare mu cewar wajen tun a baya dandali ne, watakila ƙoramar dake gudana adaf da kwazazzabon ke jan ra'ayin matafiya masu shigewa daga ƙasar katsina, sokoto da sauran wurare su yada zango a wajen. Tunda wani tsoho ya ƙara min da cewa ada, wajen maɗeba ce, watau ya taɓa zamowa dandali wanda masu sana'ar Su suka kakkafa rumfuna suke kuma tururuwar zuwa domin kamun kifi.

Zuwa yanzu dai, Bamu san alaƙar wannan aljana da rundunar Fulani masu jihadi ba, ko wadancan matafiya masu yada zango a wajen ba, ma'ana, tun a wancan zamanin an san da ita ko kuwa daga baya ne labarinta ya fito?, sannan idan akwai ta wanne taimako ko akasarin haka ta basu..? To amma dai ko a yanzu mun kara sanin ɗaya daga manyan hanyoyin da matafiya ke bi daga kano zuwa katsina ko Sokoto a zamanin da ya shuɗe. Don haka muna yiwa Allah godiya domin kuwa hakika ko a yanzu mun ƙara Sani..

# SadiqTukur Gwarzo

Saturday, 11 December 2021

TUNAWA DA YAKIN SANTOLO

 TUNAWA DA YAKIN SANTOLO

(YAKI DON TABBATAR DA MUSULUNCI A KASAR HAUSA)

9/12/2017

DAGA SADIQ TUKUR GWARZO

       08060869978

Hakika, idan har Tarihin kasar hausa ba zai cika ba har sai an kalli tarihin kano, to haka ma tarihin kano da zuwan musulunci ƙasar kano bazai taɓa kammaluwa ba har sai an sanya wani yanki daga yaƙin Santolo.

   Santolo tsohuwar daular hausawa ce, tsohuwar masarauta ce wadda salsalar ta take tukewa da salsalar asalin hausawa.

   A cikin zantuka masu yawa na maruwaitan tarihin kano, an gamsu cewar wani mai suna 'Dala' shine wanda ya soma zama akan dutsen da ayau ake kira da suna 'Dala', a wajajen shekarar 700 miladiyya, tun a wancan lokacin kuma wasu na ganin akwai mutane dake rayuwa a kan wani dutse mai suna 'santolo', wanda shi ma da alama, sunan ya samo asali ne daga mutumin da ya soma rayuwa a saman dutsen.

   Zuwa yanzu, babu takamaimen tarihin asalin kafuwar Santolo, sannan kuma yana da wuya a iya lissafa tsawon zamanin da mutane suka soma rayuwa akan dutsen santolo, to amma tarihi ya auna cewar mazauna Santolo da na Dala dake kano suna da alaƙa da juna. Alaƙar kuwa na iya zamowa ta jinsi, ko ta addini ko kuma ta duka gaba ɗaya, tunda har ma an samu cewa acan baya alakar kasuwanci na shiga tsakanin mazauna waɗannan duwatsu biyu. Wasu kuma na ganin Santolo tayi shaharar da har daga Borno ake zuwa yin fatauci a koma, to amma daga baya sai Allah ya fifita yankin Dala sama da ita Santolon.

    Babban abin tunawa dangane da Santolo shine 'Yakin Santolo' wanda aka gwabza tsakanin Sarkin Kano Ali Yaji ɗan Tsamiya da kuma shugaban Santolo mai laƙabin 'Magajin Santolo' wanda ya karɓi bakuncin takwaransa 'Magajin Dala' bayan sarkin Kano ma goma sha ɗaya Ali Yaji ɗan Tsamiya ya karya tsumburbura da ke saman dutsen Dala, sannan ya kori Magajin Dala da mutanen sa.

    Tarihi ya nuna cewa asalin garin Kano ya faro ne daga dutsen dala, inda ake bautar gunkin wata aljanna mai suna 'tsumburbura' dake saman dutsen, amma daga baya maɗatai ta kafu, har Bagauda yazo ya soma sarautar ɗaukacin yankunan maɗatai da na yankin Dala, waɗanda suka haɗe da sunan kano.

   Haka kuma, tsawon zamani a kano babu addinin musulunci, daga masu bautar tsunburbura karkashin ikon magajin dala (wanda yayi gadon Barbushe) sai kuma maguzawa waɗanda basa bautar komai irin su Bagauda da salsalarsa da ke sarautar kano. 

  A haka kano ta taho har aka zo kan mulkin Sarki Ali yaji ɗan Tsamiya a wuraren shekara ta 1349-1385 miladiyya, wanda ya karɓi bakuncin kabilar fulani Wangarawa daga Kasar Mali, waɗanda suka kawo musulunci zuwa garin kamar yadda Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya faɗa a littafinsa da yayi magana akan tarihin kano da tarihin zuwan wangarawa birnin.

   To, bayan sarki Ali Yaji ya karɓi addinin musulunci, sai kuma ya jagoranci karya gunkin tsunburbura tare da umartar masu bauta masa su dawo musulunci, amma sai wasun su suka ce sam-sam ba zasu bar addinin kaka-da-kakan-nin su ba suyi addinin dungure, don haka sai suka gudu izuwa Santolo domin cigaba da bautar da suka saba.

Ga abinda yazo a littafin Kano Chronicle game da wannan yaƙi:-

Sarki ya umurci dukkan garururuwan Kanawa su yi salla, sai suka yi. Ya gina masallaci mai-kusurwa hudu a karkashin itaciyar da muka ambata a baya, suna salla a cikinsa wakati biyar, suna komawa gidajansu. shi ko, Sarkin Gazarzawa ya kan zo da jama'arsa, suna yin najasa suna shafe dukan masallaci da ita. Saboda wannan aka sa Dan-buje ya rika gewaya masallaci da dukan makamai iri iri tun daga lisha har hudowar alfijr, yana kururuwa.   

  Kai duk da haka suka yaudare shi da mutanensa, wadansu suka bi maganar arna, shi da sauran jama'a suka ki. Ba su daina najasa cikin masallaci ba, har Sheshe da Famore suka ce, "Babu maganin wadannan kafirai sai rokon Allah." Sauran suka ce, "Hakanan ne." Sa'an nan suka taru cikin masallaci daran Talata, tun daga magariba har hudowar rana suna addu'a a kan kafiran. Sa'an nan suka fito suka koma gidajansu suna masu rauni.

 A cikin wannan rana Allah ya karbi rokonsu,

ya makantad da idanun babbansu, da kuma dukan wanda yake yin wannan aiki ya makance, duk da matansu. Daga nan sai sauran kafirai sukaji tsoro. 

Sa'an nan Yaji ya tuɓe babbansu daga sarautarsa, ya ce masa, "Kai ne Sarkin Makafi."

An ce a cikin zamanin Yaji ne Sarkin Dabi da Sarkin Daf da Sarkin Gano suka zo da dawaki cikin wannan gari, amma wannan zance ba shi da karfi.


Bayan haka sai Sarkin Kano Yaji ya ce da Wangarawa,"Ina so ku taimake ni da addu'a domin in rinjayi Santolo, idan na rinjaye ta

dukan garuruwa za su bi ni, domin ita ce ƙusar Kasashen Kudu. Suka ce, "To, ma taimake ka da addu'a amma ba za mu yi addu'ar ba sai a

bakin ramin ganuwarta. Sa'an nan Sarki ya fita tare da Wangarawa zuwa Santolo, mayakan da ke tare da shi mutum ɗari da goma sha

ɗaya, hamsin na fuskar Wangarawa, sittin na fuskar Sarki. 

Na farko daga cikin jarumawansa: Jarmai Gobara-daga-sama, da Jakada Kwalo, da Ragamar-giwa, da Makama Butaci, da Madawaki Kuamna, da Barde Shege, da Sarkin Zaura Gamaji, da Dan-buram Gantaroro, da Ɗan-makoyo Dagazau, da Galadima Tuntu, da Sarkin Sirdi Maguri, da Gauji, da Garuji da Tankarau, da Kargage, da Karfashi, da Kutunku, da Toro da Kamfashe, da Gwauron-giwa shine

Galadima, da Zaki, da Bambauri, da wadansu na Cikwan sittin.

Yayin da Suka kai Santolo, sarKI ya zauna a Duji (Sunan mutum ne.) Da duhun dare ya tashi ya tafi tare da Wangarawa zuwa Santolo, suna kewaye ta suna yi mata addua har hudowar alfijir, sa'an nan suka komo sansani. Sa ad da rana ta hudo suka taso zuwa gare ta da niyyar yaki Mutanen Santolo suka fita suka tare su a sarari, suka soma yaƙi tun daga hudowar rana har faduwa ta ba wanda ya rinjayi wani.

Kanawa suka koma Duji, mutanen Santolo suka koma gida. Sarkin Kano kuwa ya yi bakin ciki. Famore ya ce, "kada ka yi bakin ciki, ma rinjaye Su in Allah ya so." Sarkin Kano ya yi farin ciki saboda wannan magana. Daga nan Ƙosa bawan Sarkl, yace "Ya Ubangijina, ni na san asirinta. Akwai waɗansu mutum takwas

cikinta, in ba a kashe su ba ba wanda zai iya shiga ramin ganuwarta".

Famore ya ce, Ka san sunan mutanen nan?"  Ƙosa Ya ce, "I na san sunan su". Sai Famore yace, "Kaka sunayansu?" sai ya ce, "Sunan babbansu Hambari, da kuma Goshin-Ɓauna da Ka-fi-wuta, da Gugan-karfe, da Gandar-giwa, da Hamburkin-toka da Zangada-kere, da Gumbar wake" Goje yace, "Idan na ga Hambare na kashe shi in Allah ya so".

Sa'ad da alfijir ya hudo Sarkin Kano ya fita tare da rundunarsa, zuwa dutsen Santolo da mashi a hannunsa, yana mai daurariyyar fuska, GoJe yana gaban sa, Zaite yana damar sa, Famore yana hagun sa, Sheshe yana bayansa, sauran Wangarawa da Kanawa suna binsa.

Sa'ad da suka iso Santolo dukan kafirai suka fito. Da Goje ya ga Hambare sai ya zage dantsan sa ya zabura zuwa gareshi, dukan kafirai Suka zaburo wa Goje, sai ya yi musu tsawa suka watse. Sa ad da ya kai wurin Hambare ya soke shi da mashi, Hambare kuma ya ribce wuyansa ya fizgo shi daga kan doki, sai Goje ya fid da ƴar wuka ya soke shi da ita a ciki, ya mutu. Daga nan ya hau dokinsa

ya shiga cikin ganuwar Santolo, Kanawa suka bi shi suka ci birnin dukansa. Sarki ya yi umurni a yanka dukan wanda aka samu a cikinta, Sai mata da kananan yara. Goje kuma ya shiga cikin gunkinsu tare da Kosa da Gurgu, suka sami kuge da ƙaho biyu da barandami da mari.

Goje ya dauki kugen da kahon nan biyu, Kosa ya dauki barandamı da mari, Gurgu ya dauki mari.

 Yaji ya zauna a cikinta kwana bakwal, ya rushe ta sarai, ta zama babu gini ko itace. Bayan wannan ya komo garinsa, ya ce da Goje, "Fadi dukan abin da kake so, na ba ka. Goje yace "ba ni son kome sai ka naɗa mini sarautar Madawakin Kano".

Sarkin Kano ya ce. "Kai ne Madawakin Kano. Ya tube Madawaki Gasatoro, ya fita ya gina gida a gawo; saboda haka aka Kira shi da suna Madawakin Gawo, domin a rarrabe tsakaninsu.

   Dutsen Santolo gagarumi ne, faffaɗa da doro, tsayinsa ya tafi kamar hawan bene daga baya, daga gabansa kuwa goshi yayi mai faɗi da santsi, tsakiyarsa yana da faɗi harma akwai koguna da akace dabbobin daji misalin su kyarkeci, dila da macizai na rayuwa a ciki.

  Ko da yake, bamu ji sunan gunki da aljanar da aka ce akwai a saman dutsen santolo ba, amma har yanzu mutanen dake zagaye da wurin sun kiyaye cewar kakanninsu sun basu labarin cewar a zamanin da, ana taruwa ahau kan wannan dutse don neman wata biyan bukata. 

   Sannan kuma akwai wata rijiya zuzzurfa dake saman dutsen mai suna 'Rijiyar Giɗaɗo', wadda akan hana mutane zuwa kusa da ita saboda kuɓuta daga k'wank'waman dake wurin masu halaka mutane.

   Zuwa yanzu garin santolo ya kasu biyu, akwai sabon garin santolo wanda kanawa (kabilar hausawa) ke ciki, sai kuma santolon fulani, amma dukkan su suna karkashin ikon dagaci mai suna Santolo Da'u. 

    Haka kuma dutsen yana nan a tsakiyar kauyukan sabon garin santolo, santolon fulani, Madawa, Koɗe, kyarmawa, da Tsakuwa waɗanda dukkanin su suke cikin gundumar Dawakin Kudu ta Jihar Kano.





Sunday, 5 December 2021

Tunawa da Yaƙin Basasar Kano

 TARIHI: TUNAWA DA YAK'IN BASASAR KANO


DAGA SADIQ TUKUR GWARZO


4/Dec/2016


"Galadima Yusufu mutane ke so ba Alu ba. A garin Garko yake kuma acan ya mutu. Kafin rasuwar sa, kowa yayi amannar cewa shine zai zamo Sarki, amma sai ciwo ya kamashi har ya mutu a Garko.

   Daga nan sai sarakunan bayin Sarki da 'ya'yansu sukace yanzu menene abinyi? Sai wasu sukace abu d'aya ya kamata muyi, mutum d'aya ne kurum zai iya jagorantar mu zuwa Kano. Shine Mallam Babba, Alu kenan. Daga nan suka aika masa, sannan suka ɗora shi a gadon Mulkin Yusufu.

   Bayan sunyi haka, da dare suka binne Yusufu da hasken fitilu. Suka kawo Alu suka zaunar dashi akan karagar mulki. Suka yi masa nad'i. Sai kuma suka ce da sauran fadawa kowa yazo yayi mubaya'a. Kaji yadda Alu ya zamo Sarki. Kuma shine dalilin da yasa da yaji turawa na tafe ya tafi sokoto domin ziyartar hubbalen Shehu ta yadda Sarkin Musulmi zai amince da zamowar sa Sarki tare da goya masa baya.

   Jama'ar gari, mafarauta da maharba ne suka yi bore ga Sarki Alu a lokacin da yakin Basasa ya ɓarke.

   Basasa anan na nufin yaƙin da akayi don ɗora Alu akan karagar mulki. Anyi shine a Ramli shekarar 'Ba-Sa-Sha'. 'Sha' a ilimin Hisabi na nufin 1000, 'Sa' na nufin 300, 'a' na nufin 1, yayin da 'ba' ke nufin 2. Idan ka hada lissafi zai baka shekara ta 1303 kenan bayan Hijira. (Dai-dai da 1894 miladiyya).

   Ana kiran Alu da suna 'Mallam Babba' (Ma'ana babban malami), domin a wurin mu duk wani dan Sarki Mallam ne koda bai koyi karatu ba. Amma da zarar Sarki ya bashi wata sarauta sai a daina cewa Mallam, a koma kiran sa da wannan sarauta.

    Alu ya shiga Kano ranar wata Laraba. A wannan lokacin mutane da yawa sun bar Kano izuwa Kamri wajen Tukur, domin shi akafi so.

   An kashe Tukur ne a Gurum (Kamri da Gurum wasu kauyuka ne dake kusa da juna a kasar katsina). Naji labarin cewa anji masa raunika sannan aka kawo shi gaban Sarki Alu. Ance Sarki Alu yayi fushi sosai har yake cewa don me zasu yiwa ɗan uwansa na jini haka? Sarki Alu yace "kuyi maza ku kawo masa ruwa yasha". Amma sai Sarki Tukur yace "kada a kawo min ruwa, azumi nake yi, bazan sha ruwa ba". A haka kuwa Allah ya amshi ransa. Allahu Akbar!!!

   A garin Gurum aka binne Sarki Tukur, shi yasa ake Kiran sa da 'Maje-Gurum' kamar yadda ake kiran Galadima Yusufu 'Maje-Garko', ake kiran Sarki Abbas kuma 'Maje Nasarawa'".

   Marigayi Alhaji Mahmud Koki tafinta ne na turawa, ya kasance yana cikin birnin kano a lokacin da yaƙin Basasa ya tashi, shine kuma ya bamu wannan labari na sama. An rubuta labarin a cikin tarihin sa wanda aka wallafa a shekarar 1977.

    ASALIN YAKIN BASASA

Sarkin Kano Abdullahi Maje-karofi shine ɗa na biyu ga Sarkin Kano Ibrahim Dabo, ya rasu a wajajen shekara ta 1882 miladiyya a wani gari mai suna Karofi a ƙasar katsina akan hanyar sa ta zuwa Ƙauran-Namoda. Sai Ƙaninsa Muhammad Bello (shima dan Marigayi Ibrahim Dabo ne) ya hau karagar mulki. 

   Ance Sarki Muhammad Bello ya rinka kokarin karɓe muƙamai daga hannun 'ya'yan 'yanuwansa yana dasa 'ya'yansa na cikin sa. Sannan ya ƙara yawan jakadu masu tattara Haraji, abinda yayi sanadiyyar jefa talakawa cikin matsi kenan, tare da janyo masa bakin jini a gurinsu. Ance tun a lokacin ya fara sharewa dansa Muhammad Tukur hanyar zama Sarki bayan ya rasu. Ya rinka aikawa da Kyaututtuka izuwa Sokoto domin neman goyon bayan Sarkin Musulmi.

   Shi kuwa Sarkin Kano Muhammad Tukur, sarkin musulmi Abdurrahman (Ɗanyen kasko) ne ya naɗa shi bayan mutuwar mahaifin Tukur din, watau Sarkin Kano Muhammad Bello. Wasu sunce bai kai shekaru arba'in ba aka naɗa shi mulki, Wasu kuma sunce bashi da karsashin Riƙe mulki.

   A wannan lokacin, sai dan uwansa Galadima Yusuf, wanda yake ɗa ga marigayi Sarkin Kano Abdullahi Maje-karofi tare da jama'ar sa suka gudu izuwa garin Takai wadda ke kudu maso gabashin Kano. 

   Mutuwar Galadima Yusuf a garin Garko a jan hanyar su ta zuwa Kano tare da ƙwace sarauta itace sanadin ɗora Sarkin kano Alu a mazaunin sa. Sannan a hankali suka rinka cinye garuruwan gabashin kano da yaki suna ƙarfafa rundunar su. A haka har sai da rundunar su tayi karfi, suka shigo kano a ranar wata Laraba, 19 ga watan agusta na shekarar 1894 miladiyya, ana buga tambura na sarauta bayan ya samu nasara akan Sarki Tukur, wanda ya gudu ya bar Kano don gudun zubar jinin mutanen kano idan har za a buga yaƙi alhali yana cikin birnin kano.

  Sarki Alu ya cigaba da sarautar kano har lokacin da turawa suka karɓe iko da ita tare da danƙa sarauta ga ɗanuwansa Sarki Abbas.

  Dafatan Allah ya jikansu duka amin, kuma da fatan zamu amfanu da darussan wannan labari.

Tuesday, 2 November 2021

MAL MUHAMMADU AL KATSINAWI

MUSAN MALAMAN MU: Masani Malam Muhammadu bn. Muhammadu al-Katsinawi

A farkon ƙarni na 18, an yi wani malami a Katsina mai
Suna Malam Muhammadu bn Muhammad al-Katsinawi
wanda ya shahara a wajen shekarar 1732. 
  Wannan masani ya karantar, ya kuma yi wallafa ta littattafai da yawa cikin Larabci. A cikin littattafan nasa akwai wani mai suna ' Bahajat al-Afaq' wanda ya ƙunshi bayani kan ilmin taurari, da na sufanci da na lissafi. 
Dr. Hassan Ibrahim Gwarzo yayi nazarin wannan littafi, ya bayyana abin da sashin ilmin  ya ƙunsa, watau ana yin amfani da ilmin lissafi ne wajen danganta baƙaken Larabci da lissafi. Kowane baki na larabci an ba shi darajarsa a alkaluman lissafi (hisabi) kamar yadda yake a hoto:
Muhimmancin irin wannan lissafin shi ne ana iya shirya
wata kalma guda daya, ko biyu, ko fiye, sannan a zo a bi
darajar kowane babi na cikin kalmar ko kalmonin, a tara
yawan darajojin, sai a sami jimla mai adadin wata shekara
da aka yi wani abu a cikinta. 
Wannan shi ne ake kira RAMZI. Masu rubuta waƙoki sun fi sarrafa ramzi. Musamman wakoƙin su Mujaddadi Shehu Usman dan Fodiyo, da na Muhammadu Bello, da na Abdullahi Fodiyo, da na Isan Kware, sukan ƙare da wadansu baitoci masu kalmomin ramzi, watau kalmomin nuna shekarar da aka wallafa waƙokin.
 Irin wannan lissafi yana taimakawa wajen fitar da shekarar wallafar wadannan waƙoƙi. 
Misali, a cikin wakar nan ta Shehu Usmanu mai suna Tabban Hakikan wadda lsan Kware ya yi wa tahamisi, akwai baiti na 47 wanda yake cewa:
Nan waƙag ga tac cika ai fa ramzi,
JAMMU RUSHDIN ku lura tabban hakikan

Wadannan kalmomi na JAMMU RUSHDIN sun kunshi
haruffan fitar da hijirar da aka wallafa wakar, (3+40+200+1000+4), jimilla 1247hijiriyya (1832 miladiyya)
Sadiq Tukur Gwarzo ya ciro daga littafin HAUSA A RUBUCE: Tarihin rubuce-rubuce cikin Hausa na marigayi Farfesa Ibrahim Yaro Yahaya.





 

Saturday, 23 October 2021

MAGANIN BIRI KAREN MAGUZAWA: LABARIN WANI MUTUM DA MATAR SA

 MAGANIN BIRI KAREN MAGUZAWA

Wani mutum ne ya ƙwazzabi matarsa, a kullum sai ya Sami hanyar da yabi ya Ci mata mutunci, yana zagin iyayenta anini-anini. Daga yace 'duk inda aka fito na tabbata kin haɗa jini da makaɗa', sai ya ce 'wane ɗan gidan ku yayi mini Kama da wani kuturu da na sani.'.

 Haka dai, yana mata Matuƙar cin mutunci.  Idan dare ya yi ta ce ya raka ta bandaki sai ya ce 'ai da ma na san ke jikar Yambashirwa ce (wato masu zawayi a kasuwa)'.


Tana nan cikin wannan hali kullum idan ya yi mata sai dai ta haɗe kai da guiwawu ta yi ta kuka, in ta kare ta share hawayenta amma ba ta taɓa gwada rama zaginsa ba. 

Rannan sai ga wani kawunta ya zo ya sanarmata cewa anyi  haihuwa a gidansu. Bayan sun gaisa ya sha ruwa, sai ya ce mata, "Amma naga duk kin rame kamar da ke ake miya".

 Yarinya da ta samu kafa Sai ta kwashe

duk labarin ƙuƙumin da take ciki ta labarta wa kawunta. Da ya ji haka sai yace, "Ya yi da gwannai. Ai duk wanda ya ci tuwo da mu miya ya sha. Idan rashin kunya yake taƙama muna marhabin da shi."

Sai ya shawarta mata cewa ta sami lokaci su tafi wurin bikin nan tare da shi.

Ta kuma gaya masa cewa a gidan kawun nata za su sauka.

Hakan ta haddasu.

 Ranar biki sai ga yarinya tare da mijinta a gidan kawun nan nata. Aka kawo wa mijin fura da zuma kamar ta harbe shi don zaki, ya sha.

Da ƙare sha sai ya ce, "Allah sarkin baiwa, watau ko gidan ƙaho kamar kawun nan naki ana shan fura da zuma. Ko kuwa an yi ne don in zata ya daina ɗanbashirwanci?"

  Ita dai ta kanne, bata ce masa komai ba.

Can an jima aka shiga kawo masa nama soyayye mai maiƙo.

 Shi kuwa sai ɗorawa yake yana cewa, "Oh, ashe ragon gidan mayu ma yana da mai. Mu dai Allah ya mai da mu gida lafiya kada a yi balangu da kurwar mutum." 

Haka dai aka yi ta kawo masa gara iri-iri shi kuma yana ci yana yankan ƙauna kamar

yadda ya saba.

Da dare ya yi lokacin bacci ya zo sai kawun yarinyar ya kira shi ya ce masa,

"Saboda yawan jama'a mun rasa ɗakin da za mu ba ka kai da matarka. Sai dai

za mu yi maka shimfiɗa a can dakin yara tun da yau ne kawai gobe za ku tafi gida".

Bako ya ce, "Ai ba kome."

Aka je aka yi masa shimfida, sannan aka kira yaran da suke dakin aka ce musu in dare ya yi duk abin da suka ji bakon nan ya yi kada su ce kome.

 Bayan kowa ya kwanta sai wani ƙanin yarinyar nan ya tayar da mutumin nan kamar

yadda aka shirya masa, ya ce, "Na manta in gaya maka cewa idan dare ya tsala

kada ka kuskura ka fita waje ko da sunan tofaar da yau. Dalili kuwa shi ne saboda a ƙauyen nan namu akwai wasu fatalwoyi da suka kai mana ƙul. Duk wadanda suka gwada fitar dare daga wanda za a tarar an kwakule wa idanu, sai wanda za a tarar ba hannaye da ƙafafuwa duk an cire, mu dai Allah ya tsare kawai".

Bako ya Ce, "Amin. Ai ka ga gara da na sani yanzu in na kwanta abina sai da asuba ko?"


Abisa wannan shiri sai kawun matar nan ya je ya dauko damin karan dawa biyu da ya shirya wata dabara da su. Wannan sai ya daura masa farin zane ɗayan kuwa ya daura masa baƙin zane, ya yi musu wasu yan dabaru suka ƙara tsawo.

 Idan ka gan su sai ka zata wasu aljanu ne a tsaye. Ya kawo ya jingine a jikin bango daidai kofar dakin da bakon nån yake, ya koma ya kwanta abinsa.

CIKin toye-toyen nan da aka yi wa bako da rana ashe an barbaɗa wani maganin sa gudawa an hada da yaji. Can mutumin nan na Cikin barci sai magani ya fara aiki. Cikinsa ya murd'a ƙwarrai. 

Mutumi ya tashi zaune yana wani nannauyan numfashi. Can kuma sai ciki ya lafa. Har barci ya soma kama shi sai kuwa cikinsa ya kuma murɗawa.

 Ya zabura.

 A wannan karon fa ciki ya ce bai san rangwame ba.


Tun yana zaune nar ya mike tsaye gumi na karyo masa sai runtse ido yake kamar wanda ake caka wa allura.

Da azaba ta yi masa yawa sai ya yi tunanin fita waje ƙila ma fatalwa ba ta zo ba.

 Yana bud'e kofa sai ya yi kaciɓis da abubuwan nan da kawun yarinya ya

kafa. Nan da nan ya jawo kyauren daki kub ya mayar ya rufe yana cewa, "Wai!!! yau na yi arziki da an kwakule idanuna." 

Ciki ya ƙara murɗa wa mutumi tun yana tsaye har ya kai tsugune. 

Da ya ga kamar idan bai yi zawon nan ba zai

mutu sai ya ce wa yaran nan, "Kuna ji?",

 ya ga ba su motsa ba. Ya sake cewa,

"Kuna ji?!!"

 ya ga ba su motsa ba. Sai kawai ya kwale ya tsuguna cikin dakin nan ya tsulala zawonsa har kashi uku, ya koma ya kwanta abinsa yana cewa "Kai ai gara haka."


Washegari sai babban cikin yaran ya tashi ya ce, "Hm'mm'" ya rike hanci,  "ga tsinannun yara. Yanzu ku rasa inda za ku baje mana zawayi sai cikin ɗaki? Ku tashi marasa kunya"

 Ya doddoke su suka yi waje. 

Da mai gida ya ji ana kaiya kaiya sai ya ce wa babban cikin yaran, "Menene ne"?

Sai yaron ya ce, ""Kashi suka yi mana a daki, wajen ba ya shakuwa."

Maigida ya zo ya duba ya ce, ""Kai wadannan akwai 'yan banza, yanzu ba ku tashi ba ni kunya ba sai da surukai suka zo mana. To duk wanda ya yi zawon nan ya kuka da kansa, don sai na barbaɗa magani cikinsa ya kumbura ya fashe."


Ya tafi yana zage-zage mutanen gida duk suka fito. Ya dauko wata jaka ya fitar da wani ƙunshin magani daga cikinta. Ya ce, "Yanzu ina barbada wannan magani cikin ko wane ne ya kumbura tim har ya fashe. Me ake da dan da zai kai ka ga kunya?"

Yara wannan ya ce, "Ni dai ba ni ba ne". Wancan ya ce, "Ni dai ban farka ba."


Maigida ya ce, "Ai ko wane ne sai uwashi ta yi kuka." 

Ya damƙo magani zai barbada sai baƙon nan ya rike hannunsa ya ce, "Tsaya kawu kada mu yi ɓarna, in dai don ni ne wallahi na yafe. Ka bar su matsuwa ce ta sa su yin haka."

Mai gida ya ce, "Ai ba don kai ba, idan na kyale gobe ma haka za ta faru. Bari ka gani ko wane kafiri ne yau uwarsa ta rasa shi." Yayi wuf zai sa magani sai bako ya sake rike hannunsa ya ce, "Tsaya. Gaskiya 'yar Allah da wannan d'an ƙaramin na fari ni na yi shi, amma han san wanda ya yi waɗancan biyun ba,"

Mai gida ya ce, "To in kai ka yi shi ai mun san lalura ce. Saboda haka bari a zuba kan wanda ba kai ka yi ba." 

Mai gida ya je zai zuba magani akan kashi, sai baƙo ya riƙe shi, ya ce,

"Dakata, kai wannan ma ina tsammani nine na yi shi, amma fa na manta ko ni ne ko ba ni ne ba."


Mai gida ya ce, "To tun da ba ka tabbata ba bari a sa kaɗan yadda ko wane ne zai wahala kam amma ba zai mutu ba". 

Mai gida ya yi kamar zai zuba sai bako ya tare shi ya ce, "Tsaya. Don Allah a ɗauka a kan shi ma nine na yi, Amma ka ga wancan, mai yawan can, ba ni na yi shi ba."

Mai gida ya ce, "To, shi ke nan. Tun da ka nuna iya waɗanda ka yi ai ba kome. Shi kuma mai wancan ya mutu sai wani." 

Ya matsa kusa da tarin zawon nan mai yawa ya dumbuzo magani zai sa sai baƙo ya cafke hannunsa ya ce,

"kai tsaya dai in faɗi gaskiya, ko kuwa? Tun da dai nan gidanmu ne ba na wasu ba, ba wani abin ɓoyo. Wannan ma ni na yi shi kada a tsaya ana wahala."

Sai yaran nan duk suka fashe da dariya mai gida ya dubi surukin nan nashi ya ce, "Kai wane irin mutum ne da za ka rasa wurin da za ka, ka yi zawo sai gidan surukanka. Ka gan ka dai ba ka gaji kunya ba. Tun da kuma ka yi mana zawo a nan, ai ba inda ba za ka iya yin zawo ba har a masallaci. To wa ma ya sani ko gado ka yi ba mu sani ba muka dauki 'yarmu muka ba ka. Ni ai tun ranar da ka

zo nan na dubi idanunka na gan su kamar idanun wanda ya sha nonon maita na Ce auren nan a yi dai amma sai ka kai mu ga kunya. Yanzu bari i Kira makwabta su gani su shaide mu, ke kuma.."

Ya ce da matar, "ki tafi gidan AIkali ki yi ƙara.. Kai Sarki ma ya kamata ya ji wannan maganar don a aika har mutanen garinku su zo."

Da mutumin nan ya ji haka sai ya faɗi kwance yana dibar kasa yana afi yana cewa, "Na tuba na bi Allah na bi ka kawu don Allah ka yi min sutura kada mutanen garinmu su ji." Kawun yarinya ya ce nan fa ɗaya, lallai sai jama'a sun sani. 

Da mijin matar nan ya ga ba Sarki sai Allah sai ya je gabanta ya rike ƙafafunta yana cewa ya tuba ita ma ta yi masa gafara kada mutane su sani. 

Can dai da ita da duk sauran matan bikin nan suka shiga ba mai gida hakuri. Kai da ƙyar dai suka ciwo kansa. Ya ce wa mutumin nan, "To tashi ka tafi garinku kada ka ƙara yin zawo, ka ji ko? Yanzu na yafe ka."

Mutumin nan ya tashi ya dawo gida shi kadai. Bayan 'yan kwanaki matarsa ta dawo ta same shi.

Daga ranar nan ko awakin gidan su yarinyar nan ya gani kunyarsu yake ji balle mutane. Ita kuma daga lokacin nan ta sami lafiya.

LABARIN FALKE DA BAƘO: ZAMAN DUNIYA IYAWA NE

 FARKE DA BAƘO


Wani falke ne yake cin kasuwar wani gari mai nisan tafiyar kwana goma sha biyar daga garinsu. Shi wannan falken sana'arsa ita ce sayar da auduga. To duk sa'ar da ya zo wannan garin sai ya sauka a gidan wani mutum sababbensa.

Saboda irin sakayyar da falken nan ke yi wa mai masaukinsa, idan kasuwa ta watse, sai ya zama ba shi ba ma har jakunansa ba su rasa abin taunawa.

Wata rana sai falken nan ya zo, suna hira da mai masaukinsa a zaure, Sai ga wani mutum ya zo daga shi sai lagensa, ya ce yana neman masauki. 

  Falke da mai masaukinsa suka riƙa yiwa mutumin nan kallon uku kwabo. Kai daga Karshe falken nan ya ce shi bai amince a baiwa wannan masauki ba don ba su san Ko wane

iri ne shi ba.

   Da mutumi ya ji haka sai ya ce, "Don kun gan ni CIKin wannan kama shi ya sa za ku wulakanta ni? To ai ni ma mai gidan kaina ne yanzu ma shanu na kai kurmi na sayar. Tafiya ce ta mayar da ni haka".

Sai ya ɗaga hammatarsa ya jawo wani burgami ya ce, "Ni ma ga tawa dukiyar, mai irin wannnan kuwa me zai tsaye tsiwace-tsiwacen dukiyar wani."

Ya zazzage jakarsa suka ga kudi irin wanda ba su taɓa gani ba. Nan da nan hankalin falke ya tashi, sai zare ido yake yana lasar baki. Mai gida kuwa sai ya ce da mutumin nan, "don Allah ka yafe mu. Ka san halin duniyar tamu mutumin yau abin tsoro ne."

Falke kuma sai ya ce "Shi kenan a yi masa masauki tare da ni, ka ga na huta da kwana ni daya".

Da bakon nan ya ga masaukinsa sai ya ce to zai isa kasuwa domin kuwa gobe ranar kasuwa. 

Ya kama hanya ya tafi. Yana isa kasuwa sai ya sami

wani lungu ya cire kudinsa daga cikin burgami ya cuccusa su cikin bantensa ya sayi dakuwa ya cusa cikin burgamin kamar ba a cire kome daga cikinsa ba.

Baƙo ya kama hanya ya koma masauki

Da dare ya yi aka zauna ana hira sai farken nan ya yi shimfida ƙasa da inda jakar mutumin nan take rataye.

Ana cikin hira sai ya yi hamma, ya yi mika da wayo ya mike hannunsa ya taɓo jakar nan ya ji  har yanzu kudin na nan. Da an ɗan jima duk sai ya yi haka.

 Can sai ruwan sama ya ɓarke kamar da bakin kwarya, sai bakon nan ya lunsashe idanunsa ya shiga minsharin ƙarya kamar ya yi bacci.

 Da farken nan ya ji gari ya yi tsit sai ya zabura ya figi burgamin nan taf da dakuwa ya auna da gudu daga shi sai gajeren wando ga shi ana ruwa.

 Da baƙo ya ga haka sai ya tashi sannu ya tafi ya tayar da mai gidan ya ce masa "Ka ji abin da mutumin nan ya yi mini".

Gari na wayewa sai mai gidan ya dauki bakon nan suka tafi suka shaida wa sarkin garin abin da ya faru. Sarki ya sa aka kama jakunan falke da kayan audugarsa aka sayar aka ba bakon nan aka ce ya ci da hakuri Allah ya saka masa.

Bako kuwa sai ya raba kudin nan biyu ya ba mai masukinsa rabi, rabi kuwa ya tara almajirai da nakasassu ya yi ta sadaka.

   Ya bar garin ana ta yi masa addu 'ar Allah ya kiyaye gaba. 









Sunday, 10 October 2021

TARIHIN ALH SAFIYANU MADUGU, HAMSHAƘIN ƊAN KASUWA


 TARIHIN ALH SAFIYANU MADUGU, HAMSHAƘIN ƊAN KASUWA

Shine Alhaji Safiyanu Madugu, ɗan Ali  (wanda akafi sani da suna MADUGU MAIRAWANI) ɗan Abdullahi, ɗan Muhammadu, bafillatani a jinsi, haifaffen birnin kano, ƙwararren ɗan kasuwa, mai kyauta da kyautatawa, mai yawan ƙasƙantar da kai wanda baya son a yabeshi. Shine ya kafa kamfanin 'A.S Madugu & sons Ltd wanda ya shahara a fagen dillacin kayayyakin masarufi, sannan daga baya ya kafa kamfanin 'Dala foods' wanda yake samar da kayayyakin abinci misalin ganyen shayin CITY TEA, KUNUN TSAMIYA, da FURA.

 An haifi Marigayi Alhaji Safiyanu Madugu a garin Kano, a gidan masaƙa wanda yake cikin  unguwar ceɗiyar ƙuda a cikin birnin kano, a shekarar 1938. Sunan mahaifin sa Alhaji Ali Madugu amma yafi shahara da suna 'Madugu Mai Rawani', mahaifiyar sa kuwa sunan ta Hajiya Hadiza Yusuf, ita haifaffiyar unguwar Daurawar koki ce cikin birnin kano.


KARATUN SA

Karatun addini marigayi Alhaji Safiyanu Madugu ya soma runguma tun da ƙuruciyar sa kasancewar ya taso a gidan girma da mutumci, gidan fatauci da riƙo da addini.

Haka kuma ya yi karatun boko, amma ba a makarantar Primary ko Elementary ba, sai dai an samu cewa da girmansa cikin shekarar 1960 da ɗoriya, ya shiga wata makarantar dare mai suna IGBO UNION dake Sabon Gari ta kano , wacce ta zama makarantar 'Mai kwatashi' a halin yanzu. Da daddare suke zuwa shi da abokanansa domin karatun yaki da Jahilci.

ƘURUCIYAR SA

Mahaifinsa Alh Ali Madugu ne ya soma sanya shi cikin harkokin ciniki tun bayan soma ɗagawar sa, domin ya zama ya soma buɗe ido a lamurorin kasuwanci. Alhaji Safiyanu Madugu ya soma kasuwanci tun yana ƙarami, yana mai hawa keke daga kasuwar kurmi zuwa kasuwar sabon gari don saro kayayayakin siyarwa. A haka ya girma har kuma ya bunƙasa a kasuwanci.

Haƙiƙa Allah Ta'ala ya albarkaci Alhaji Safiyanu Madugu da abubuwa guda biyu, na ɗaya shine kyakkyawar mu'amala  a cikin harkar kasuwaci sa na biyu kuwa shine haƙuri.

RASUWAR SA

 Allah ya karɓi ran Alhaji Safiyanu Madugu a ranar litinin, 3 ga watan fabrairu na shekarar 2003 (3/2/2003) a halin jinya a asbitin Mallam Aminu dake birnin Kano.  Ya rasu da misalin ƙarfe 1:00 na rana.

Alhaji Safiyanu Madugu ya rasu ya bar mata huɗu da ‘ya’ya talatin da tara (39), maza sha tara (19) mata ashirin (20).

NB: Wannan tsakure ne daga littafin Tarihin Alh Safiyanu Madugu mai ɗauke da tarihin rayuwar sa da kuma salon kasuwancin sa.

Da fatan Allah ya rahamshe shi amin

Monday, 27 September 2021

ASALIN KAFUWAR GAYA

 ASALIN GAYA


(Tsakure)



SADIQ TUKUR GWARZO



Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya kawo a littafinsa 'Tarihin Kano kafin Jihadi' cewa asalin garuruwan Kano, Gaya da Rano ya samu ne daga wasu mutane uku waɗanda suka yiwo balaguro tare da ahalin su daga ƙasar Habasha tare da ƴanuwansu Maguzawa. 

Sunayen waɗannan mutane kuma jagororin tawagar sune Ranau, Gayya da Dala, kuma sun yiwo wannan balaguron ne tun kafin haihuwar Annabi Isa A.S. (shekaru sama da dubu biyu da suka gabata kenan).

  A cewar marubucin, Ranau ne ya soma zama a garin Rano, kuma daga gareshi aka samar da sunan Rano, Dala ne ya soma zama akan dutsen Dala na kano, kuma daga gareshi aka samar da sunan dutsen Dala, haka kuma Gayya ne ya soma zama a inda garin Gaya yake a yanzu kuma daga gareshi aka samar da sunan Garin Gaya.

Masana irin su marigayi Alh Maitama Sule Ɗanmasanin kano da wasun sa duk sun haɗu akan cewa tabbas asalin (Hausawa) mutanen Gaya daga Habasha suke, kuma shi kansa wani shahararren mutum wanda aka ce daga sunan sa aka samo sunan garin Kano mai suna 'Kano maƙeri', daga garin Gaya yake. Har ma sun ƙara da cewa Bagauda wanda tarihi ya kiyaye a matsayin sarkin Kano na farko shima ɗan garin Gaya ne.

Amma a wasu zantukan na tarihi musamman waɗanda suka fito daga garin Gaya, an samo wani abu mabanbanci da wannan game da asalin kafuwar Gaya.

  Tarihin ya tafi akan cewa zamani mai tsawo da ya gabata, inda garin Gaya yake a yanzu jeji ne mai cike da albarkatun namun daji.

  Akan haka wani mafarauci da ake kira da suna Bagauda tare da ɗanuwan sa mai suna Gayya, suka ruski wajen tare da zama a inda garin Gaya yake a yanzu. Bagauda ya kafa rumfar sa a wani waje da har zuwa yanzu ake kira da suna 'unguwar Bagauda'. Ya zama nan ne makwancin sa, a kullum ya kan shiga daji yayi farautar namun daji sannan ya dawo rumfar sa ya sarrafa.

   Sannu a hankali sai mutane musamman ƴanuwan sa mafarauta suka fara riskar wajen tare da kafa rumfunan su na kwana. Kwanci tashi albarka na ƙaruwa, mutane na ƙara kwarorowa, daga mafarauta zuwa manoma, zuwa maƙera, zuwa matafiya masu shigewa zuwa Borno, da dai sauran masu sana'o'i daban-daban. Wannan kuma shine asalin yadda aka kafa garin Gaya.

  Game da yadda aka samo wannan suna na Gaya, an samu zantuka guda biyu.

  Na farko an faɗa cewa jim kaɗan da soma kafuwar garin Gaya a wancan lokaci, sai Bagauda ya ɗaura niyya tare da barin garin. Daga nan yayi yamma yana tafiya cikin dazuka gaminda farautar namun daji a hanya. Akan haka ya je ya sari wani gari da ake kira ƴar Gaya, sannan kuma da ya ƙara tashi, bai sauka ba  sai a inda garin kano ya ke a yanzu. A wancan lokacin ne ya sari kano.

  Littafin tarihin kafuwar kano kuwa 'kano chronicle' ya sanya cewar Bagauda shine sarkin kano na farko, kuma ya soma mulki ne a shekara ta 999 A.D.

  Wanda Bagauda ya bari a Gaya shine ɗan uwansa Gayya wanda suka riski wajen tare, don haka shine ya zamo jagoran mutanen da suka cigaba da zama a wurin, kuma daga sunan sa 'Gaya' ta samo asali.

Zance na biyu kuwa ya tafi akan cewa sunan Gaya ya samo asali ne daga wani jagora da aka taɓa yi a farko-farkon garin (ko Gayya ko kuma sarki na farko mai suna Sarki Kwalo). 

Ance wannan jagora yana da kyauta da haba-haba da mutane. Ya kasance duk baƙon da ya isa gareshi sai ya samu wani abu na alheri yayi masa. 

Akan haka ya kasance idan wasu suka ziyarce shi alhali ya gama rabar da abubuwan da yake dasu ga masu ziyartar sa,  maimakon ya barsu haka nan ba tare da ya basu komai ba sai yace " sai hakuri, babu abinci, babu nono, sai dai gaya".

Sai ya ɗauko gayan ya bayar.

Don haka sai mutane ke kiran sa da suna 'mai gaya'. Kuma daga gare shi sunan Gaya ta samo asali...

Sunday, 26 September 2021

FALSAFAR MUTUWA

 MUTUWA


SADIQ TUKUR GWARZO


Ubangiji Ta'ala ya faɗa a littafin sa Alqur'ani mai girma cewa 

 كُلُّ نَفْسٍ ذَائِقَةُ الْمَوْتِ  

3:185

Ma'ana, dukkan rai sai ta ɗanɗana mutuwa.

   Tabbas, mutuwa aba ce wajiba ga dukkan wani rai da aka busa mata numfashi.

  Masana falsafa sun haɗu akan cewa mutuwa na nufin tafiyar ruhi zuwa barzahu; watau zuwa rayuwa bayan mutuwa. 

  Shikuwa mutum yana ɗauke ne da ruhi da kuma gangar jiki. Ruhi kuma shine kamar 'software' mai rayar da gangar jiki 'hardware' a ilimin na'ura mai ƙwaƙwalwa.

  Don haka mutuwa na nufin raba ruhi da gangar jiki. Kuma da zarar rabuwar ta kasance, sai ruhi ya soma tafiya zuwa sama.

Wannan kuwa wata tafiya ce da Allah ya ƙadartawa ruhi, wadda ta zarar an ɗauke shi daga nan duniya sai a tafi dashi zuwa wata duniyar wadda aka tanadarwa masu irin aiyukan da ya aikata alhali yana cikin gangar jiki a wannan duniyar tamu, walau ayyuka na alheri ko na akasin haka. 

Haka zai cigaba da rayuwa har kuma lokacin da Ubangiji zai hukunta sake tayar da rayayyu domin yin hisabi.

  Haka nan, wani lokacin Allah yana yiwa wasu daga bayin sa nuni da ƙaratowar ajalin su, ta yadda za a ga sun sabunta alaƙantuwar su ga Ubangiji maɗaukakin Sarki, tare da riƙo da wasu ayyuka masu kusantar da bayi ga Allah.

  Hakika mun ga irin haka ga rayuwar magabata musamman masana ilimin falsafanci irin su Imam Muhammad Ibn Sina, wanda duk da kasancewar sa likita kuma marubucin Qanun fiɗ ɗibb, amma yayi biris da yiwa kansa magani.. a lokacin mutuwa kawai yake hange, kuma ita yake marari..

  A wani ƙadamin kuma mutuwa ta kan zowa wasu bagatatan ba tare da aune ko ankararwa ba. An ga irin hakanga mutane da dama, waɗanda suka mutu alhalinsuna cikin wani sha'ani, kuma suna masu cike da burikan rayuwa.

  Hakika, ga wanda duk yasan ilimin mutuwa ya isheshi tsarkake buwayar Allah maɗaujakin sarki. 

A ƙarshe, yana da kyau mubsani, babu wata tabbatacciyar alama ga mutuwa. Ita tana iya zuwa da dalili, tana kuma iya zuwa babu gaira babu dalili.

  Domin shiryawa mutuwa, yana da kyau mutum ya kasance a kullum ayyukan sa na alheri sufi na akasin su yawa, domin haƙiƙa ayyukan mu na da tasiri ga halin da zamu tsincinkawunan mu bayan mutuwa.

  Dafatan Allah ya jiƙan mu amin

Thursday, 26 August 2021

ASALIN HARSHE

 RANAR HAUSA TA 2021: Asalin Harshe

SADIQ TUKUR GWARZO

  Harshe na nufin adabin yare da ake amfani dashi wajen sadarwa tsakanin al'umma, wanda ya ƙunshi fitar da sautin kalmomi a bayyane ko a rubuce.

  Farfesa Greg Downey, da sauran masana irin sa na fannin ilimin tarihin wanzuwar ɗan adam a duniya da yadda ya kasance yana rayuwa tun fil-azal, 'Anthropology', sun gamsu da cewa har yanzu ba a san takamaimen dalilin soma maganar ɗan adam ba musamman dube da ƴan uwansa na kusa a ƙwayoyin halittu irin su birrai da gwaggwonin sa waɗanda suke ɗauke da kusan duk abinda ɗan adam yake dashi na halitta, amma su basa iya magana. 

   Don haka bincike ya yanke cewar wasu ɓangarori da aka gani a ƙwaƙwalwar ɗan adam waɗanda duk da cewa akwai shigen su a ƙwaƙwalwar gwaggon biri, amma sun fi haɓaka a na ɗan adam, ke da alhakin baiwa ɗan adam wayewar furta magana da amfani da harshe, waɗannan ɓangarorin sune 'Brocas area, da 'wernick area'.

SOMA YARE A DUNIYA

Hasashe dai na ilimi ta nuna cewa an soma amfani da harshe kimanin sama da shekaru 150,000 da suka gabata. Haka kuma binciken adadin harsuna da masana suka yi yana nuni da cewa yarukan da ake amfani dasu a duniya sun kai kimanin 6000, sai dai binciken wasun su na nuni da samuwar su a wasu shekaru ƙasa da lokacin da aka ƙiyasta soma yare a duniya.

Zantukan da aka rinƙa samu a jikin kogunan duwatsu ya ƙara zama hujjar cewar harsuna da yawa sun samo asali ne daga tsatso ɗaya, watau harshe ɗaya.

Daga ina Harshe ya samo asali?

  Harshe ya soma ne a wannan duniyar kaɓar yadda aka faɗa tun da farko kimanin shekaru 150,000 da suka gabata yayin da halittun zamanin suka haɓaka wata wayewa ta soma amfani da shi (harshe) wajen sadarwa a tsakanin su. Amma sanin asalin harshen da aka soma amfani da shi a wancan zamanin abu ne da har yanzu masana ke bincike akai, wasu ma na ganin ba abu ne mai yiwuwa da za a iya samu ba.


MENENE ASALIN DUKKAN HARSUNA?

Masana da yawa na cewar asalin dukkan harsuna sun samo ne daga guda ɗaya tilo, sannu a hankali suka rinƙa rarrabuwa. To amma da yake da akwai ra'ayin masana daban daban akan haka, zai fi kyau mu ji wasu daga ciki kamar yadda yazo a littafin 'Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa' wanda Rabiu Zarruk, Abubakar Kafin Hausa da Bello S Alhassan suka wallafa a shekarar 1990:-

1. Ra'in Bow-Wow

Dangane da labarin da ake kira ra'in bow-bow, kalmomin da muke amfani da su a harsunanmu na yau, sun faro daga sauti ne irin na halitta. Wai lokacin da dan Adam ya fara magana, yana ƙókarin misalta sauti ne na dabbobi da tsuntsaye da sauran halittu. Saboda haka, in mutum ya ga wani abu yakan yi magana ne, bayan ya riya wani sauti a zuciyarsa. Sautin da yakan riya kuwa, shine kamar kukan wani tsuntsu, ko motsin wata dabba in tana tafiya, ko tana gudu,ko motsin ganye yayin da ake guguwar iska, ko wanin wadannan. Wai haka ne abubuwa suka sami sunayensu a kowane harshe.

2. Ra'in Poob-Pooh

Ra'in pooh-pooh shigen na bow-wow ne. Shi yana cewa, duk kalmomi mafarinsu razana ce ko mamaki. Larurar magana ce take kama dan Adam yayin da wani abu ya razana shi ko ya ba shi mamaki. A lokacin nan, duk abin da ya fito daga bakinsa ya zama sunan wani abu. Saboda haka, a wannan ra'in kalmomin motsin rai, kamar a'aha! assha! haba! kash! tir! wai! wayyo! yawwa! da sauransu, su suka fi kowanne tsufa a harshe.

3. Ra'in Ding-Dong

A wannan ra'in, kwatancen kamannin abubuwa ko motsinsu shi ne asalin kalmomi a harshe. Watau da farko dan Adam ya yi kokarin samun lakabin abubuwa ne dangane da kamanninsu ko motsinsu. Saboda haka a nan, amsa-kama su ne kalmomin farko a harshe.


4. Hasumayar Babila

A wannan labarin cewa aka yi, can asali, duk 'yan Adam harshensu daya ne.

Jikokin Annabi Nuhu sun gaji duniya bayan Ruwan Dufana. Sun yadu ƙabila-ƙabila, amma a sannan harshensu daya ne. Daga baya, wasu 'masu taurin kai a cikinsu suka yi tunanin gina babban gari mai suna Babila. Bayan sun gina garin sai kuma suka ga cewa za su iya gina hasumayar da za ta kai su sama. Da hasumayar ta yi nisa sai ta rushe. Shi ke nan, duk wanda ya faddo daga hasumayar dą wanda ke cikin garin sai bakinsa ya juye. Daga nan- ne mutane suka rarrabu kowa harshensa daban.

5. Ajiyar Allah

Ga abin da wannan labarin ke cewa: Kamar yadda Allah ya halicci zanzaro da ilimin gini, ya ba ƙudan zuma baiwar tattara zuma dága furanni, to hakanan ya ajiye wa dan Adam harshe. Dalilin wannan baiwa, duk inda mutum ya girma Sai ya tashi da harshen wurin. Saboda haka, Allah ya ajiye harsuna ne a wurare daban-daban na duniya. Saboda haka tun can farko idan al'ummá ta zauna a wani wuri shi ke nan, sai ka ji tana kiran abubuwa da sunayen da aka ajiye a wannan wun. (Asalin labarin dai shi ne kamar yadda yazo a littafi mai tsarki Alkurani cewa, tun lokacin da aka halicci Annabi Adamu aka sanarda shi sunayen dukkan abubuwa).

Tammat bi Hamdullahi

(Da fatan Allah ya bamu zama lafiya amin)





Monday, 9 August 2021

BINCIKE A DUTSEN BAƘOSHI

 BINCIKE A DUTSEN BAƘOSHI

Sadiq TUkur Gwarzo

Asalin Garin Dutsen Baƙoshi

Abisa Tarihi, wannan yanki ya jima sosai yana ɗauke da mutane masu rayuwa a wuraren ta yadda zai yi wuya a iya gane lokacin da aka soma zama a yankin.

Mutane sun rayu a wuraren a warwatse, har daga baya wayewa tazo musu na haɗa kai da fuskantar matsalolin zamanin, suka kafa gari.

Ɓur-ɓur Bamaguje ne da yayi zamani da Dala, shima ya zauna a saman wani dutse wanda dake yammacin Tsaunin garin Baƙoshi, ko kuma ace mazaunin Aljanna Mararaka. Ance suna da siffa mai girma wadda har sukan iya girgiɗe bishiyar giginya su saɓo ta a kafaɗa, ko kuma su girgiza su ciro ɗan giginya su yi jifa dashi.

Hasashe ya nuna garin ya soma kafuwa ne a bayan tsaunin garin Dutsen ɗan Baƙoshi shekaru sama da dubu  da suka gabata. Har zuwa yanzu kukoki na nan a kufan garin masu nuna wanzuwar gari a wajen.

Yaƙe-yaƙe ne silar da mutanen garin suka baro tsohon gari tare da dawowa inda garin yake a yau. A zamanin wani mai suna Baƙoshi shine sarki. Sai jama'ar garin suka kafa gari tare da yi masa ganuwa domin samun tsaro daga mahara.

Akwai wani dutse a kofar Fadar garin na yanzu wanda akace Baƙoshi ne ya ɗauko shi a saman kansa ya kawo kofar gidan sa, kuma nan ne wurin zaman sa inda yake ganawa da jama'a har zuwa rasuwar sa.

   Sunan Baƙoshi ya fito a cikin fadawan Barbushe, a littafin Kano chronicle, da cewa tun a lokacin a duk shekara mutane na niƙar gari zuwa gindin dutsen Dala domin yiwa Aljana Tsumburbura bauta.

Don haka muna iya auna shekarun kafuwar sabon garin kenan da zamanin Barbushe na saman tsaunin Dala.

Marina

Akwai tsohuwar marina dake saman dutse a zangon garin, baya da ganuwar garin kenan, har yanzu ana iya ganin raɓukan baba da katsi waɗanda akayi amfani dashi.

Maƙera

Akwai ɓurɓushin maƙera da Dr Mahmud ya hango a saman tsaunin garin Baƙoshi, masanan sun tsinci uwar maƙera a saman tsaunin wamda ke tabbatar da wanzuwar maƙera masu sarrafa ƙarafa a wajen. 

Falalen Mararaka

Falalen Mararaka, Wuri ne mai kyawun gani, yana ɗauke da duwatsu masu ƙayatarwa, kuma anan ne gidan Aljanna Mararaka yake da iyalinta. Har yanzu masu bori da tsubbu suna zuwa domin neman taimako daga gareta. Akwai ramuka da suka yi akan dutsen inda suke tsima magunguna domin bayar dasu ga jama'a, akwai turaruka da akan iya gani waɗanda masu neman biyan buƙata daga Aljanna mararaka suke ajiyewa hadiya zuwa gareta.

Daman tun da jimawa mun samu labarin akwai alaƙa tsakanin aljana Mararaka ta saman dutsen Baƙoshi da kuma Aljanna Tsumburbura ta saman tsaunin Dala, dukkansu ance bauta musu ake yi, to amma salon bautar da ake yi garesu ya sha bam-bam da juna.

  Ita Aljana Mararaka dake dutsen ɗan Baƙoshi har yanzu tana da matukar tasiri a wannan yanki, ana ganin ayyukanta kuma ana neman taimakonta saɓanin Aljanna Tsumburbura ta saman dutsen Dala wadda ko kaɗan ba a jin ɗuriyar ta.

Tsohon Masallacin Dutsen Baƙoshi

A tsohon ginin masallaci dake kofar fadar garin, ginin hausa na tubali da maginam dauri suka gina. Katangar masallacin mai kauri ce, a wani wajen ta haura mita ɗaya, a wani wajen kuma ta gaza mita ɗaya da kaɗan. Ana hasashen tsufan masallacin na ita tasamma shekaru 500, wanda hakan ke nuna jimawar addinin musulunci a garin duk kuwa da cewar bai hana mu'amala da iskokai ba.

SARAUTA

Daga kan Baƙoshi aka soma shugabanci a wannan gari, don haka da ɗansa ya gajeshi sai ake kiransa da 'Ɗan Baƙoshi'  Kuma har zuwa yau, da wannan suna ake kiran dagacin wannan gari mai tsohon tarihi.

Wednesday, 4 August 2021

ADABIN WASAN KWAIKWAYO

 WASAN KWAIKWAYO

Wannan na daga cikin rabe-raben adabi, gundarin sa kamar  ya samo ne daga kalmomin 'drama' ko 'play' na turanci, ma'anar su bai wuce 'aikata shiryayyen wasa' ba musamman a dandali  domin nishaɗantarwa da ilimantar da masu kallo.

Ana gabatar da wasan kwaikwayo a dandali, talbijin, radiyo ko duk wani taron jama'a. Babban abu dai a game da shi shine ya zamo an yi ne ga wasu mutane waɗanda suke kallon sa kai tsaye ko kuma suke sauraro.

Masani Brion Crown  ya fassara wasan kwaikwayo da cewa "Wasan kwaikwayo hanya ce ta gabatar da abubuwan da suka shafi rayuwa a cikin nishaɗi da ban dariya tare da motsa sassan jiki da kuma rakiyar sauti".

Soma taskance wasan kwaikwayo a duniya ya samo ne tun a zamanin Masani Aristotle na ƙasar Girka (c. 335 BCE), kuma tun daga wancan zamani an gamsu da cewa kowacce ƙabila tana da yanayi da siga na gabatar da wasan kwaikwayo ga al'ummar ta.

A wani yanayin, ana iya cewa wasan kwaikwayo ya dogara ne kachokan bisa kalmomin da ake musanyawa a cikinsa, waɗanda mafi akasari ake shirya su cijin hikima domin zaburar da masu kallo/sauraro bisa halayya, ayyuka, ko shirye-shirye na masu gabatar da wannan wasan kwaikwayo. 

   

ADABIN ZUBE

 RUBUTUN ZUBE

  Rubutun zube wani jigo ne ma adabi wanda ya tattara mabanbantan abubuwa kama daga rubutattun labarai, hikayoyi, da sauran su.

  Mallam Yakubu Musa Muhammad ya rubuta a littafin sa 'Adabin Hausa' cewa "Zube; ya haɗar da tatsuniya, hikaya, maganganun azanci, azancin magana da sarrafa harshe.."

  Akan raba Adabin zube izuwa rubutattun Tatsuniya, Labarun Gargajiya, Barkwanci da Tarihi, ko kuma a rarraba shi gida uku izuwa Almara, Ƙissa da Hikaya.

*Azancin Magana na nufin wata magana da akeyi mai ma'ana saɓanin gundarin maganar, misalin karin magana (i.e, Kowanne Allazi..) , zambo (i.e, mai bakin zalɓe..), ba'a (i.e hassada bata hana samu), habaici (i.e, yaro bari murna karen ka ya kama zaki) da sauransu.

* Sarrafa harshe ya tattara zantukan azanci da hikima waɗanda ake amfani dasu wajen siffantawa, ƙawatawa, bayyanawa da sauran su.

* Ƙissa: maanar ta shine wani jinsin labari na gaskiya wanda babu sofanen ƙarya a cikinsa musamman wanda ya shafi addini. Missali, maimakon ace labarin Annabawa sai a kira shinda Ƴissoshin Annabawa.

*Almara: maanar sa shine, jinsin labari wanda yake shiryayye domin janyo hankulan mutane, a wasa musu ƙwaƙwalwa ta hanyar samar musu da wata gagarumar matsala a cikin labarin wadda take buƙatar nazari da tunani wajen warwareta.

*Hikaya: Maanar ta shine jinsin labari na gaskiya amma wanda aka yi masa ƙari da wasu abubuwa don ƙawatashi ko zuzutashi. A wani fannin kuma akan samu labarai na hikima da ake kira hikayoyi waɗanda suka ƙunshi dabbobi da tsuntsaye waɗanda ake bayar dasu domin koyawa alumma darasi.

Tatsuniya: Labarai ne ƙirƙirarru da ake bayarwa musamman ga yara domin koyar dasu halaye kyawawa da tunkuɗe su daga munanan halaye.

 

ILIMIN SANIN RUBUTACCIYAR WAKA

 ILIMIN SANIN RUBUTACCIYAR WAƘA

  Ita dai rubutacciyar waƙar hausa ta samu tasiri ne daga waƙoƙin larabci, domin kuwa ba a san ta ba sai da musulunci da ilimin larabci suka shigo ƙasar nan, watau musamman lokacin jihadin Shehu Usmanu.

   Tun daga nan har zuwa yau, idan aka bincika marubuta waƙoƙin hausa za a tarar ba zasu rasa wani tasiri na harshen larabci ko addinin musulunci ba.

   Wani abin ban sha'awa kuma shine, harshen Hausa harshe ne mai iya karɓar kowanne irin salo da harshen larabci yazo dashi, ya zauna daram kamar dama anan aka halicce shi.

   Bugu da ƙari, ma'aunin waƙar hausa rubutacciya da amsa amon ta duka irin na waƙoƙin larabawa ne, sai fa daga bisani ne mawaƙan hausa suka saɓa da irin waƙoƙin larabci, har ma aka samu sabbin jigogi waɗanda suka shafi lamuran yau da kullum.

    Abubuwan da ake sa rai aga sun tabbata kafin a hukunta cewa rubutacciyar waƙar hausa tayi yadda ake sonta guda 9 ne, amma na ƙarhen bai zama tilas ba. 

Ga abubuwan kamar haka:-

1. Buɗewa da rufewa da yabon Ubangiji da Salatin Annabi (S.A.W).

 Misali: Na fara da sunan Zuljalali maƙagin duniya,

   Ina salati ga Khairul Anami hasken idaniya.

2. Ma'auni; ta yadda za a iya yanyanke ta kuma baitocinta su zamo kai-da-kai.

  Misali: 

*Dawil:

 Mutum haka ma in yaga bashi da ko zare,

Ya kan roƙi Allah safe da daddare.

*Madid:

Ko ina, duk an sani kai ka mulki,

Duk ƙasar nan babu mai arziƙin ka.

*Da sauran su; kamar su Basiɗ, Watir, Kamil, Hazaj, Rajaz, Ramal, Mumsarih, Hafit, Muƙtabib, Mutaƙarrab, Muɗarid.

3. Waƙa ta kasance tana amsa amo, tana kuma da ƙafiya.

4. A shirya baitocin waƙa dai-dai da ɗangogin waƙa guda bakwai.

   Misali: Gwauruwa itace mai baiti ɗango ɗaya.

Ƴar tagwai mai ɗango biyu,

Ƴar uku mai uku,

Ƴar huɗu mai guda huɗu,

Ƴar biyar mai biyar,

Tahamsi mai shidda,

Sai Tarbi'i mai guda bakwai.

5. Ambaton jigon waƙa tun daga farkon ta.

  Misali: "Nayi shiri tsaf zan ja hankali,

                Akan mata masu yawon dandali".

6. Warwarar jigon waƙa

Watau a kawo ɗangogi waɗanda suka tafi dai-dai da jigon da ake waƙar akan sa.

7. Ambaton sunan mawaƙi da tarihin yin waƙar a ƙarshen ta.

8. Salon mawaƙin ya kasance yana da ƙarfi, watau yana yin bayani mai gamsarwa.

9. Gwanin ta da iya sarrafa harshe.

Sadiq Tukur Gwarzo ya ciro wannan bayanin daga littafin 'WAƘA A BAKIN MAI ITA' wanda kamfanim ɗab'i na NNPC ya wallafa a shekarar 1979.

MA'ANAR ADABIN HAUSA DA RABE-RABEN SA

 ADABI

  Sheshin Malami uban Malamai, Farfesa Abdulkadir Ɗangambo, ya kawo a littafin sa mai suna 'Rabe-Raben Adabin Hausa da muhimmancin sa ga rayuwar Hausawa' cewa kalmar Adabi ta samo ne daga kalmar 'al-adab' ta larabci. Ma'anar ta a larabce shine 'ɗa'a, fasaha, ko ƙwarewa'.

   To amma a hausance, ma'anar kalmar kamar yadda Farfesa Ɗangambon ya rubuta a wancan littafin shine "ya ƙunshi yadda al'adunsu (Hausawa), ɗabiunsu, harshen su, halayyar su, abincinsu, tufafin su, maƙwabtan su, huɗɗoɗinsu, da ra'ayoyin su da sauran abubuwa na dabarun zaman duniya don cigaba da rayuwa, kai har ma da abinda ya shafi mutuwa".

   Dalili kenan da akan kira Adabi da 'madubin rayuwar dan adam', domin ana hasashen da zarar ka kalli adabin al'umma, to zaka fuskanci yadda take.

  Don haka, adabi ya tattara bayani ne game da al'adu, rayuwa da fasaha ta al'umma.

  Wannan ne silar da ake nazarin rubututtuka, wakoki da sauran hikimomin ɗai-ɗaikun al'umma a manyan makarantu, ana yin hakan ne domin ƙwaƙulo ilimai na adabi dake jibge a cikin su.

   RABE-RABEN ADABI

1. Adabin Gargajiya

Shine adabin da Hausawan dauri ke da shi tun kafin zuwan turawan mulkin mallaka, wanda kuma nason sa ya biyo gar zuwa yanzu. Ga yadda ya rabu:-

A. Rubutun zube; wannan ya ƙunshi rubutu na Tatsuniyoyi, labarai, Almara, wasa ƙwaƙwalwa, ƙissoshi, wakoki da kaɗe-kaɗe da sauran su waɗanda aka taskance tun kafin zuwan turawa, misalin ayyukan Abdullahi Suka, Wali Ɗan Marna da Wali Ɗan Masani da sauransu.

B. Makaɗa

Sun rabu kaso da dama, misali:-

I. Makaɗan Fada: Misakin Ɗankwauro

II. Makaɗan jama'a: Misalin Dr Mamman Shata

III. Makaɗan Maza: Misalin Ɗan anace mai waƙar ƴan dambe

IV. Makaɗan ban dariya: Misalin Ƴan kama 

C. Kayayyakin kiɗan Hausawa sun haɗar da kayayyakin dokawa misalin ganga, kalangu, jauje, dundufa, da kayayyakin  gogawa misalin goge, kukuma, da kuma kayayyakin busawa misalin siriƙi, da algaita.

2. Adabin Zamani

Shine adabin da ya zowa Hausawa sabili da shigowar sabuwar  wayewa sanadiyyar mamayar turawan mulkin mallaka musamman wanda ya soma a farkon ƙarni na goma sha tara.

Ga yadda adabin ya rabu:

A. Rubutattun waƙoƙi

Misalin Rubutattun waƙoƙin Aliyu Na Mangi, Sa'adu Zungur, Khalid Imam, Murtala Uba 

B. Rubutun zube: misalin labarin littattafai irin su Magana Jari na Abubakar Imam, In da so da ƙauna na Ado Ahmad Gidan Dabino, Idan so cuta ne na Farfesa Yusuf M Adamu, Sihirtacce na Bala Anas Babinlata, Mace Mutum na Rahama A Majid 

B. WASAN KWAIKWAYO

Misalin littattafan wasan kwaikwayo irin su Zamanin nan Namu, Mallam Zalimu

Friday, 9 July 2021

HIV PREVENTION: UTILISATION OF ORAL HIV PRE EXPOSURE PROPHYLAXIS

 HIV PREVENTION: UTILISATION OF ORAL HIV PRE EXPOSURE PROPHYLAXIS



Oral pre-exposure prophylaxis, or PrEP, is a way for an HIV-negative person who is at risk of HIV infection to reduce their risk of getting HIV by taking antiretroviral drugs. 


How do you identify a suitable candidate for Oral PrEP use?


In accordance with the WHO Implementation Tool for Pre-exposure Prophylaxis of HIV Infection, suitable candidates for PrEP use must:

A: Meet Eligibility Criteria

B: Have no side effect with any of the HIV Treatment Drugs

7 ELIGIBILITY CRITERIA

1. Test HIV negative

2. Have no known exposure to HIV in the past 72 hrs.

3. No sign and symptoms of Acute HIV infection

4. Have no allergies or Contra-indication to PrEP medicines

5. Have creatinine clearance of >60ml/min

6. Be willing to use PrEP as prescribed and test for HIV periodically

7. Be at substantial risk of HIV infection

  PEOPLE WHO ARE CONTRAINDICATED TO USE HIV PRE EXPOSURE PROPHYLAXIS

1. People who test positive for HIV

2. People who have exposure to HIV in the past 72hrs (should be on Post-exposure prophylaxis possibly)

3. People who have signs and symptoms of HIV

4. People who have allergy to PrEP drugs

5. People who have creatine clearance of lessthan 60ml/min

 REGIMENT OF  ORAL HIV PRE-EXPOSURE PROPHYLAXIS DRUGS

1. TDF: Tenofovir Disoproxil Fumirate

a. Single agent, can be taken orally.

b. Daily usage is 300mg per adult

c. TDF alone is safe and effective in men who have sexual intercouse with women, or women who have sexual intercourse with women.

2. TDF (Tenofocir) in combination with FTC (Emtricitabine)

a. Is safe and effective for preventing HIV in both heterosexual men amd women, and also in men who have sex with men and in transgender women.

b. The regimen contains 300mg of TDF and 200mg of FTC for adult

c. They can be contained and consumed in a single tablet called 'fixed dose combinator'.

d. Its the most commonly used PrEP in all countries

3. Tenofovir (TDF 300mg) combined eith Lamivudine (3TC 300mg)

a. TDF/FTC are considered equivalent for antiretroviral treatment.

b. There's only one study of it, but in used in some countries.

     PrEP DOSING

WHO recommends 2 optiins for the dosing frequency of PrEP

A. DAILY DOSING (TAKING THE MEDICATION DAILY FOR A PRESCRIBED PERIOD OF TIME)

This is for Heterosexual men and women, and also for men who have anal intercourse with women. And it should be taken as;-

* A client should take either of the drugs for 7 days before exposing self to HIV. This ensures muximum protection.

* Daily dosage should be sustained through out the exposure period

* Those wanting to stop PrEP should continue taking the drugs for 28 days after the last HIV exposure.

2. EVENT DRIVEN (DRUG TO BE TAKEN TIMELY PRIOR TO AN EVENT YIELDING TO EXPOSURE TO HIV)

This is only for Men who have sex with Men, and :-

a. They should take a first dose of 2 PrEP pills called 'the loading dose' between 2 amd 24 hours prior to exposure/intercourse.

b. They should take the second dose of single pill after 24htɗrs of the exposure

c. Third dose is a single dose, and to be taken after 24hrs of the secomd dose.


SUGGESTED CLINICAL PROCEDURE SCHEDULE

Initial visit: Investigatiin amd interventions

1. Determine eligiblity for PrEP use

2. Test for Hepatitis B surface antigen

3. Test for Hepatitis C Antibody

4. Testing for STIs eg RPR test

5. Test for pregnancy (PrEP is safe during pregnancy and motherhood)

6. Review vaccination history

7. Coumsel the client on; prevention need, sexual and reproductive right, fertility interventiim, Gender base violence, substance use and mental health.

COUNSELLING ON PREP EFFECTIVENESS: 

During the counselling session on HIV PrEP, the 7 key counselling messages should be clearly communicated with the client, which are;-

1. EFFICACY

PrEP is highly effective for preventing HIV.


According to CDC, PrEP reduces the risk of getting HIV from sex by about 99% when taken as prescribed., and can be taken at daytime or night, with food or on empty stomach, also using alcohol or rexreational drugs doesnt ɓake PrEP less effective.

2. ADHERENCE

Adhere strcitly to dosing regiment for complete prevention

3. TIME TO PROTECTION

A. For Men and Women who have sex with women, it takes 7 days of taking PrEP pills before building complete HIV protection giant in the body.

B. For Men who have sex with Men, first dose is 2 pills, followed by second single pill after 24 hours of the exposure, and also another single dose after 24hrs of taking the second dose.

  REDUCING STIGMA FOR HIV PrEP

Educate the community to help them umderstand the diffrence between HIV treatment and PrEP. Also, guide the community members to understand that PrEP should be viewed as a responsible choice to protect health

Sunday, 30 May 2021

LABARIN MAI ASIGIRI ƊAN SAMAME

 LABARIN MAI ASIGIRI ƊAN SAMAME

  Cikin zamanin sarkin Katsina Muhamman Bello, anyi wani mutum wanda ya dami Katsinawa da fitina, yana kama musu ɗiya yana kai su ƙasar Arewa yana sayarwa. Sa'an nan sai sarkin  Katsina ya tara manyan malamai duka na katsina, ya basu dukiya mai yawa, yace su taimake shi don a kama wannan mutumi; idan an kama shi, sai a kaishi kasuwa a sare masa  kai.

  Nan take malamai suka duƙufa ƙoƙari, aikuwa dai ba'a yi kwana goma ba, sai Mai-asigiri ya zo ya kama wata budurwa a ƙofar sami da daddare. Tayi hargowa, daga nan masu tsaron garke suka ji ana ihu, kowa ya ɗauko kwari da baka da kunkeli, suka zo gudummawa.

 Ko da ya ji su sai ya yi ta kirari, yana cewa "A gayawa yaro ga Mai-asigiri!" Ko da fulani suka ji Mai-asigiri ne, sai suka ce ashe yau daga zamuyi a wurin nan. Sai suka yi ta hargowa,   suka fito daga gidajensu, suka zo bakin ƙofa amma tana rufe, shi kuwa sai kirari yake yi daga waje. 

Mutane suka koma gida, Gulbi Bikwaine ya fito fadanci daga gidan Durɓi, sai  yayi kichiɓus da wannan hargowa, Mai-asigiri yana ta kirari. 

   Daga nan sai Gulbi ya ɗauko alkilla yai ɗamara da ita, ya ɗauko garkuwa da takobi ya fito ya zo bisa ganuwa, ya aza garkuwarsa, ya hau daga nan, sai ya darza waje. Ya nufi inda Mai-asigiri yake, koda isar sa sai shima yayi kirari yace "A gayawa yaro ga Gulbi"

  Sai mai asigiri yace yau ƙarya ta ƙare tunda ga baraden katsina sun fito su da kansu, sai ya zabura da gudu don ya tsira sai kuwa Gulbi ya bi shi ya banke, ya kamashi ya ɗaure shi da asalwayi, ya shiga gari dashi sannan ya baiwa waɗannan mutane dake wajen yace musu "kada ku sanarwa da kowa nine na kama shi, kuyi shiru, kuce kune kuka kamashi". Sai suka tafi dashi wurin Durɓi.

  Durɓi ya tafi dashi ga sarki acikin dare tsaka anan Nasarawa. Sarki ya tambayi Durɓi wanda ya kama shi, sai Durɓi yace Ƴan garke ne. Sarki yace da safe a kawo su yana son ganin su. Durɓi ya tafi gida, sa'annan Mai asigiri yace "ni babu wanda ya kamo ni sai Gulbi Bikwaine".

   Da gari ya waye, Sarki ya kawo kenkendi goma da dawaki goma da zambar dubu ya baiwa Gulbi kyauta, ya yanki ƙasa cikin kaita ya bashi. Sa'annan sarki ya tara manyan sarakunan katsina ya ce "Yau ga azzalumin nan an kawo shi, ina dabara?"

  Suka che "A sare kansa a kasuwa", Sarki yace "to sai gobe in Allah ya yarda".

  Da dare ya yi, sarki yasa ƴan batakulki suka zo da  Mai-asigiri, sarki yace "Kai, Kaɗo, na yi shawara da sarakuna, sun ce a kashe ka. To ni ba zan kashe ka ba, zan sallame ka, amma kada ka ƙara kama kowa a ƙasar Katsina, kuma duk labarin da ka ji na arewa ka faɗa mani nan da nan in sani." 

Sarki ya kawo kyauta mai-yawa ya ba shi ya che yaransa su raka shi har ƙofar Guga, a buɗe masa ya fita.

Amma ya che, "Kar ku gaya wa mutane." Da gari ya waye, fagachi ya chika, Sarki ya che, "Mai-asigiri ya gudu, an bi shi, ya tsere."

Kwanchi tashi kwanchi tashi ran nan Sarki ya tafi Modoji shan iska tare da iyalinsa, Danbaskore ya ji labari, ya nemi sa'a ya che za shi yaki wajên Sokoto. Mallamai suka ba shi sa'a don ya zo ya mamayi Sarkin Katsina ya yanka shi.

Mai-asigiri ya ji labari, sai da ya bari yaƙi yayi yamma, ya dakako ya nufo Katsina, dare kuwa ya yi-masa a kan hanya.

Da ya zo ƙofar Guga ya che a buɗe kofa. Mai-tsaron kofa ya ƙi, sai ya che shi manzon Sokoto ne, ya nufi ƙofar Samri, ya tambayi sarkin ƙofa, ya che, "Durɓi na nan ?" Ya che, "I." Ya che, "A faɗa masa ga manzo daga Sokoto." Durbi ya taso ya zo gare shi ya che, "Wanene kai, mutumin Sokoto ?" Mai-asigiri ya che, "Ni manzo ne." Durɓi yace "Ina takardarka a kai ma sarki, kana ka shigo?". Sai ya che, "Durɓi, matso nan in yi maka raɗa". Ya che, "NI ne Mai-asigiri, labari na samo mai-girma, ka faɗa ma sarki jibi warhaka karkarar adda'irar Katsina ta chika da yaƙi; ga su nan tafe jibi: sarakuna biyu, Gobir da Tasawa."

 Durɓi ya che, "Ashe ba magana ku buɗe kofa." Aka je aka amso mabuɗi wurin Ajiya aka buɗe, ya shigo, aka ba shi abinchi da goro. Durɓi ya che, "Sarki yana Modoji, bari in gama ka da mutun, shi kai ka." Suka tafi Modoji, suka buga Kofa, sarkin ƙofa ya che, "Wanene ?" Mai-asigiri  ya che, "Manzo daga Sokoto, ku fada ma sarki." Suka che, "A'a, sai ka bada takardarka, a kai wa sarki yanzu, kana ka shigo." Sai Ya che, "Kai, ku gayawa sarki maza maza akwai saƙo gareshi." Aka je aka fada ma sarki, ya fito chikin tsakad dare ya che a kira yaransa, kowa ya ɗauko takobi da mashi da ɗamara da sulke da garkuwa, kana a buɗe kofa manzo ya shigo. 

Sarki kuwa yai ɗamara, da shi da mutanensa a ƙofar birnin Modoji.

Sa'an nan sarki ya che ya shigo. Mai-asigiri ya shiga, ya che ma sarki, "Ni ne." Sarki ya che, "To, ina labarin Haɓe ? Ya che ma sarki, "Gobe warhaka nan tojiyar ta sha wuta, don haka na zaburo in shaida maka." Sarki ya che, "Na gode maka kwarai. Ta ina za su hudo ? Ya che, "Wajen yamma za su hudo." Sa'an nan sarki ya sallame shi.

 Da asuba ta yi sai sarki ya hau, da shi da mutanensa, ya tafo gida ya shiga, sa'an nan ya fito.

Ya che, "Ina manyan sarakunan Katsina ? Su zo, su shiga shirayi. Suka zo, sukai gaisuwa. Ya che masu, "Gobe warhaka muna da baƙi, sarkin Gobir da Ɗanbaskore suna tafe, sai mu yi ƙoƙari mu yi dabara." Durɓi ya che, ya sarki, abin da ya fi sai ka sa a tafi bakin sagagin nan a ƙulle gezozin nan duka, domin da Sun zo Sai su kasa wuchewa: kafin su kwanche gezojin mun chi su da yawa, mun yi masu ɓarna ƙwarrai.

Sarki ya che, "Dai-dai ne." Kuma Ƙaura ya che, "Dai-dai ne".

Aka je aka ɗaure geza sarai, sa'an nan Durɓi ya hau ya tafi bakin mashaya,  ya jera ƴan baka, kuma da azahar sai Sarki ya sa akai shela a kasuwa, aka gaya wa mutane su shirya sosai ga tawaye nan tafe. Kafin Danbaskore ya zo Katsinawa sun shirya, shikuwa sai murna ya ke yi ya wo dukake.

Gari na wayewa rana ta hudo kaɗan, sai aka jiwo hargowa arewa da gari. Durɓi ya che a faɗa wa Sarki tawaye Sunzo. Aka buga tambari da kuge, shi Danbaskore ba shi da labari an ƙulle gezoji sarai. Da ya zo kamin a kwanche geza, Sarkin Katsina ya zo, shi da mutanen sa. Akai ta daukekeniya

da mutane har wajen rana tsaka, sa'an nan aka fasa tawaga, dokin yaƙi ya fasu, akai ta kama mutane da dawakai, aka kama doki kamar hamsa, mutane kuma kamar talata.

Durɓi da ya ga Danbaskore, cha ya ke wani ƙaramin zarumi ne, ya bi shi ya che sai ya kashe shi; ya tarar dashi ya soke shi da mashi; shi kuwa ya sa garkuwa ya amshe, ya che ma Durɓi, "Kai, yaro kula da giwa!." Durɓi ya che, "Ai, giwa ta san mashi." Shi kuwa bai san Sarki ba ne. 

Sai da suka kai ga tasa mahara, dokin Ɗanbaskore ya tsallake tasa-mahara, dokin Durɓi kuwa ya kasa tsallakewa, sai ya tsaya. Danbaskore ya che, "Ni ke saye

da kaina, kai kuwa sai an ba ka." Durɓi ya che, "I, wanda a ke siyarwa ya kore ka da ƙyar ka tsere."

  Ɗanbaskore  Ya koma gida shi ɗaya, sai makaɗinsa don ba a kama makaɗi wurin yaki. Da ya isa gida ya che, "Sai na rama, sai mun gamu da Katsinawa. Ni bakin

bunsuru ne mai-wari, kowa ya chi ni, ya yi amai." 

 Yayi shekara guda bai nufo Katsina ba, sai dai sammu a ke kawowa, in an bisne sai Mai-asigiri ya zo ya faɗa wa Sarki, a je a tone. Duk inda ya nufa Mai-asigiri sai ya zo Katsina ya fadi. 

  Wata rana kuma Danbaskore ya kira wadansu mazaje, sukai lada tukuna, ya che, "In kun kawo Sarkin Katsina, na ba ku abin da zai ishe ku." Ya kawo zannuwa da kalluba ya ba su, ya sa akai masu kitso Kamar mata. Aka dubi wani mutumin Kano, aka gama kai da shi, aka che ya kawo ma Sarkin Katsina ya saya. Aka tsafe wukake, aka ba su, waɗanda in sun soki mutum nan take zasu kashe shi, aka kawo wani sammu kuma wanda za su sa a gidan Sarki.

   Ba-Kanon nan ya tafo da su. Sai wani mutum ya gayawa Mai-asigiri, ya che, "Ba ka bin mutumin nan gashi can zasu katsina tallan bayi na sammu?" Sai yace masa "I",

Sai ya yanko dare ya riga su, ya che ma Sarki, " Ana kawo tallan bayi daga arewa, to, maza ne akai masu siffar mata". Sarki yace "Har su zo, muna saurare". Ko da isowarsu sai aka kama su aka kai su gangi (shine wani rami kusa da ƙofar Guga) aka kashe su. Shi kuwa Ba-kano, akayi biyan bashi dashi.

To haka Mai-asigiri yai wa sarkin Katsina Muhammadu Bello alƙawali, har ya mutu bai warware ba.

  Sadiq Tukur Gwarzo


Friday, 5 March 2021

YALWAN DANZIYAL

 GARIN YALWAN ƊAN ZIYAL


Sadiq Tukur Gwarzo


Daga tsoffin matsugunan da suka yi shura a ƙasar Hausa musamman cikin ƙasar Kano, ananiya cewa garin 'Yalwan Ɗanziyal' na daga gaba-gaba.

Akwai ababen tunawa da dama game da wannan gari.

Marigayi Maje Ahmad Gwangwazo ya ruwaito a littafinsa 'Tarihin kano kafin Jihadi,: wangarawa sunzo kano' cewa sai da Wangarawa (waɗanda suka taso daga Mali tare da isar da addinin musulunci a kano a zamanin sarkin kano Yaji) suka sauka a garin Yalwan Ɗanziyal na lan wani lokaci kafin daga bisani su ƙarasa garin kano.

Kafuwar Garin Yalwan Ɗanziyal 

Kafuwar wannan gari mai tsohon tarihi ya samo ne tun lokacin da masu sarautar kano (na gidan Bagauda) suka karya gunkin Tsumburbura, abin bautar da Barbushe da sauran magoya bayansa da suka gabace shi suka kasance suna yiwa bauta a saman dutsen Dala.

Littafin Tarihin kano (Kano chronicle) ya kawo mana labarin yadda abin ya faru da cewa:-.

" Sarki na Tara, Tsamiya ɗan Shekarau (1307-1343)

Sa'ar da yaci sarauta ya tara kafirai yace dasu "soyayya ana gadonta, ƙiyayya ana gadonta, babu wani abu tsakani na daku sai baka da mashi da takobi, da garkuwa ba yaudara, domin babu mayaudari sai matsoraci"

Domin ya haɗa abubuwa biyar:- sadaukantaka, kwarjini, zabura akan abokan gaba, tsananin fushi da ƙarfi.

A daren alhamis suka taru a gaban gunkinsu birni da ƙauye, jama'a masu yawa , masu ƙuru- da gunduwa da tsintsima dubu arbamiyya, sarakunan baka arbamiyya da tsiraru, basu gushe ba suna kewaye gunkin tun daga magariba har hudowar alfijir.

Yayin da alfijir ta hudo sarki ya fito daga ɗakin sa ya nufi wurin gunkin. 

A gabansa akwai mutum saba'in, kowanne cikin su yana riƙe da garkuwar fatar giwa.  Yayin da yakai wurin sai kafirai suka hanashi shiga ɗakin da gunkin yake. Aka ɗaura yaƙi.

Wani mai suna Bajere aka  ruwaito ya riƙe mashi bisa umarnin sarki yana kashe abokan gaba har sai da ya sadu da ginin ya shiga cikinsa, ya samu wani mutum ya jingina da bayansa da itaciyar gunkin, akwai jar maciya a hannunsa, (Bajere) ya soke shi. 

 Mutumin ya zabura yayi kururuwa , hayaƙi ya fita daga bakinsa ya gama gari duka. Ya fito yana gudu zuwa kofar Ruwa, sarki ya bishi ya kutsa a cikin ruwa.  Sarki ya zauna tare da rundunar sa suna ta neman sa cikin ruwa. Daga nan ya fita zuwa Dankwai, suka barshi, dalili kenan da kowanne taron yaƙin da yasha ruwan Ɗankwai ba ya samun nasara cikin yaƙin sa.

   Sa'an nan sarki ya komo ƙarƙashin itaciyar ya rushe ginin, ya tattara dukan abin dake karkashin itaciyar  na Cibiri. Dukkan kafirai suka gudu, sai Makare ɗan Samagi da Dunguzu ɗan Dorini kaɗai.."

   Don haka, ire-iren waɗannan mutane ne suka kafa wannan tsohon gari mai suna 'Yalwan Ɗanziyal'.

   Matsugunin Garin Yalwan Ɗanziyal

Asalin garin ya kafu ne a gabas da inda na yanzu yake cikin karamar hukumar Rimin gado ta jihar kano, wanda ana iya cewa can ne ainihin garin Yalwa, daga bisani akace annobar wata aljanna mai suna 'Kun taru' wadda ke halaka mutane ta sanya suka koma sabon gari na farko, wanda yanzu yake  yamma da inda garin yanzu yake.

Acan kuma cin ruwa ya sanya mutanen sake yin hijira zuwa inda suke a yanzu. Sai dai babu takamaimen shekarun da waɗannan hijirori suka wakana. Amma dai akwai alamomin zama da ake iya gani har yanzu.

Bisa ainihi, Yalwa ne sunan garin, sabili da albarkar da Allah ya ba shi na noma da kasuwanci ga duk wanda ya ziyarce shi. 

  Wani mai suna Ɗanziyal ya zamo shahararren jagoran garin ne tsawon zamani bayan kafuwar sa, har kuma ya zama ana danganta sunan garin da sunan sa.

A mafi shaharar zance, Ɗanziyal mutum ne masanin ɗibbu, watau mai bayar da maganin waraka daga cututtuka wanda ya riski garin Yalwa da zama a zamanin da wata ɗiyar Sarkin kano ke fama da lalurar rashin lafiya, anyi magani amma abun ya faskara.

  Cikin sa'a sai aka kawo ta wajen Ɗanziyal dake zaune a garin YALWA, wanda ya yi mata magani har kuma ta samu sauƙi. Sarkin kano na zamanin (ba a faɗi sunan sa ba) ya nemi Ɗanziyal ya faɗi ladan sa na wannan aiki, amma sai Ɗanziyal yace duk abinda aka bashi ya wadatar.

  Wannan ne ya sanya sarki ya baiwa Ɗanziyal sarautar garuwa uku manya na wannan yankin. Na ɗaya shine garin Yalwa da shi Ɗanziyal yake zaune, sai Madobi da kuma wani gari mai suna Cunkoso.

  Akwai zance mai nuni da yawaitar ƴaƴan sarkin kano a wannan garin na Yalwan Ɗanziyal musamman a zamanin mulkin fulani a kano, watakila garin yana daga cikin garuruwan da ake tura ƴaƴan sarki koyon ilimi da jarumta. Don haka ake yiwa garin kirari da 'Yalwa ta Ɗanziyal, garin ka taka mallam' (akan ambaci ɗan sarki da Mallam). Wannan ya sa baƙi ke taka-tsan-tsan a garin don gudun kada su yi wani abu ga wani daga ƴaƴan sarki cikin rashin sani.

 Sannan kuma ana ganin zuriyar marigayi Sarkin Kano Muhammadu Tukur can suka koma da zama bayan kammala yakin Basasar kano...

Wednesday, 24 February 2021

Hikayar Sagardatta, Ɗa ga wani Ɗankasuwa

 Hikayar Sagardatta, Ɗa ga wani Ɗankasuwa 


Daga littafin Khalila wa Dhimna, wanda Vishnu Sharma ya rubuta shekaru sama da dubu biyu da suka gabata (300 BC) domin koyar da mabiyan sa sirrikan zaman duniya.


Sadiq Tukur Gwarzo


Sadaukarwa gareku don neman albarkar ku bisa murnar raɗin sunan yaron waje na Muhammad Tukur wanda akayi ayau Laraba 23/2/2021.

Sagardatta shine sunan wani kyakkyawan matashi, ɗa ga wani ɗan kasuwa da aka taɓayi a wani daga garuruwan tsohuwar daular Hindu.

  Wata rana, sai wannan ɗan kasuwa ya samu labarin cewa ɗansa Sagardatta ya siyi wani littafi mai tsada sosai, wanda saɗara ɗaya ce tal a cikin sa watau "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu". 

  Ko da wannan attajiri ya ji haka, sai hasala matuƙa. Ya kira ɗan nasa yana masa faɗa, ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba, yana cewe "Ta yaya zaka yi nasara a harkar kasuwanci, alhali zaka iya ɓannatar da kuɗaɗe masu tarin yawa haka wajen siyen littafi ɗaya tal mai ƙunshe da saɗara ɗaya tal ajikin sa?! Fitar mini daga gida, kada na sake ganin fuskar ka anan!"

  Daga nan Uban ya kori ɗan nasa daga gidan sa.

Wannan matashi ya shiga tsananin baƙin ciki bisa korar sa da mahaifin sa yayi daga gabansa, amma babu yadda ya iya, sai ya ɗauki littafin sa tare da  kama hanya yana tafiya ba tare da yasan inda yake nufa ba. Ya haddace wannan saɗarar dake cikin wancan littafi, don haka yana tafe yana maimaita ta a cikin zuciyar sa.

Akan hanyar sa ya riski wani babban gari, sai ya nemi abashi masauki, mutanen garin suka tambaye shi sunan sa, sai ya amsa musu da waccan saɗara da yake ta faman maimaitawa a zuciyar sa, watau ""Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu". Shikenan, sai aka rinƙa kiran sa da wannan suna.

Wata rana, sai ƴar sarkin garin ta ziyarci wani bikin al'ada na shekara-shekara da akeyi a wannan gari, anan kuma sai ta haɗu da wani kyakkyawan ɗan sarki baƙo wanda shima yazo kallon bikin daga ƙasar su, sai ya kasance ta kamu da sonsa nan take. Sai ta umarci kuyangarta ta bincika hanyar da zasu aika masa da saƙo.

Daga nan Gimbiya ta rubuta ɗan jawabi a takarda, ta baiwa kuyangarta don ta isar a gareshi.

 Sai dai bisa kuskure, wannan kuyanga  ta baiwa matashi Sagardatta wannan wasiƙa a maimakon wancan ɗan sarki, Sagardatta ya karɓaa ya buɗeta, ya soma karantawa kamar haka:-

"Na kamu da sonka tun sa'ar da na soma ganin ka. Ina rokon ka same ni a fadabta. Da zarar ka shiga, za ka samu igiya sarƙafe a ɗaya daga tagogin wajen wadda zata kawo ka kai tsaye zuwa inda nake. Daga Gimbiyar wannan birni”

Ya raya a zuciyar sa da cewa “Tabbas zan amsa gayyatar gimbiya tunda ta buƙaci haɗuwa dani.”

Da zuwan sa ya ga igiya an zirota daga tagar wani ɗaki can a bisan bene, ya kama ta ya soma ɗaɗɗafewa har ya riski ɗakin da gimbiya take. Ɗakin ɗan duhu, kuma gimbiyar tayi tsammanin Yariman nan data gani ne a wajen biki, don haka cikin rawar jiki ta shiga yi masa karɓa cikin girmamawa. Ta gabatar masa da abinci da abinsha kala-kala cikin karramawa.

 Bayan sunci sun sha, sai ta shiga yi masa zantuka tana mai cewa “Nayi matukar kamuwa da sonka. Hakika babu wanda ya kamaci zama miji na sama da kai, ina rokon ka sanar dani menene ra'ayin ka game dani”

Sagardatta yace "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"

Sai tayi mamakin yadda Yarima ɗan sarki zai amsa maganar ta da wannan maganar, da hanzari ta kunna manyan fitulun ɗakin waɗanda suka haskaka shi sosai. Ranta ya ɓaci matuƙa yayin da ta gane ashe ba wanda ta buƙata bane a gabanta, nan take ta fatattake shi tare dayi masa korar kare daga gareta.

  Wannan matashi ya cika da baƙin ciki bisa wannan abu da ya sake samun sa ba bisa laifin sa ba, sai yayi shawarar tafiya wani wajen bauta dake kusa da wajen domin shafe yammaci da daren sa acan, jim kaɗan da isar sa sai bacci ya kwashe shi.

Da lokacin rufe wajen yayi,  masu zuwa bauta duk sun gama tafiya gida, sai wani maigadin dare ya hango matashi na bacci, don haka yazo ya tashe shi yana mai umartar sa da barin wurin, yace masa "Wannan wajen bauta tsoho ne kuma talautacce, idan kai baƙo ne zo muje ka kwana a gida na"

Shikenan, matashi Sagardatta ya bi maigadi zuwa gidan sa dake kusa da wajen, daga nesa ya nuna masa ɗakin da zai shiga ya kwanta kafin safiya. Sai dai cikin kuskure, wannan matashi ya shiga wani ɗakin saɓanin wanda aka nuna masa, wanda aciki ɗiyar wancan maigadi taci ado tana sauraron saurayin ta.

  Mai gadin ya kasance yana da ɗiya wadda take soyayya da wani mutumi, amma ba bisa  son  ran sa ba, har ma ya hana shi kusantar duk inda take. To amma saboda tsabar soyayya, sai wannan ɗiya ta shirya da masoyin nata yin aure a wannan dare yayin da mahaifinta ya tafi gadi a wurin bauta da dare, ta yadda wajibin sa ya amince da matashin a matsayin surukin sa.

Kasancewar akwai duhun dare, da shigar Sagardatti ɗakin, sai ɗiyar maigadi tayi tsammanin masoyin nata ne ya gabato, nan take ta tarbeshi da murna, taje gaban gunkin su  ta ɗauko awarwaron ƙulla aure ta sanya a hannun ta, sannan ta sanya a na Sagardatti. A bisa al'ada, ta ƙulla aure tsakanin su kenan.


Matashi Sagardatti cike da mamaki yace "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"

Ko da taji haka, sai nan take ta gane ashe ta tafka babban kuskure, sannan nadama ta dabai-baye ta tana mai rayawa a zuciyar ta cewa 'dama aduk sanda mutum yake gaggawar aikata wani lamari ba tare dogon nazari ba, tabbas yana iya tafka babban kuskure.'

Nan take ta shiga masa masifa da ci masa mutunci tare da korar sa daga gidan ma baki ɗaya.

Har ila yau dai, Sagardatta ya fito daga wannan gida tare da kama hanya a cikin daren sannu a hankali cike da tsananin ɓacin zuciyar faruwar wannan abu ba tare da ya aikata wani laifi ba, yana cikin tafiya ne ya ga wata tawagar masu ɗaura aure a gefen hanya suna tafiya ana kaɗe-kaɗe da bushe-bushe.

Mutanen suna sanye da kayayyaki na ƙawa, sunyi kwalliya sanye da jawhari da azurfa. Kawai sai ya yanke shawarar shiga cikin su. Yabi bayan ango da tawagar sa, wanda a kusa dashi amaryar sa ce da zai aura ba da jimawa ba, kuma a lokacin suna kan hanyar su ne ta zuwa gidan kawunnan amarya  a inda za ayi ƙwarya-ƙwaryan bikin ɗaurin aure.


Ana cikin haka, Kwatsam sai ga mahaukaciyar giwa ta kutto  tare da tunkaro wannan tawaga, cikin firgici kowa ya dare tare da arcewa, amarya kaɗai tayi tsira yayin da ta gurɗe ta faɗi ƙasa a tsorace tana maƙyarkyata cikin firgici. 


Ko da ganin haka, sai matashi Sagardatti ya zaro wani kullin kusoshi dake rataye dashi, sannan yabi bayan giwa ya buga mata, giwa ta tsorata tare da rugawa da gudu.

Bayan ɗan lokaci tawaga ta dawo, ƴanuwa da abokan arziki suka shiga yiwa amarya jaje da barka da auna arziki, ita kuwa sai ta murtuke fuska, shine ma take cewa "Ayanzu na sauya shawara, domim a lokacin da rayuwata ta shiga cikin haɗari, an rasa wanda zai cece ni sai wannan baƙon, don haka babu wanda zan aura sai shi. Wannan shine abinda na yanke"

 

Wannan mataki na Amarya ya ɓatawa mutane da yawa na cikin wannan tawagar zuciya.  Nan take sai gaddama da cece kuce ta ɓarke a cikin su.. 


Da muhawara tayi tsanani, hayaniya yayi yawa, duk mutanen kewayen wajen suka firfito don ganin abinda ke faruwa. Sai kuma ga Sarkin garin shima ya fito, ashe yaji labarin abinda ya farundon haka ya taso domin yin hukunci. A cikin mutanen dake wannan waje har da gimbiya ɗiyar sarki da kuma budurwa ɗiyar maigadi.


Sarki ya tambayi matashi Sagardatti da cewa "Kana cikin tawagar  biki wannan ibtilai ya auku, sannan kai ne ka kuɓutar da wannan yarinya da ake gab da ɗaura mata aure daga cutarwar giwa, Ina so kayi mana bayanin yadda wannan abu ya faru!"

  Ko da matashin Sagardatti ya yunkura don yin magana, kaɓar kulluɓ, maganar sa dai itace karatun nam da ya haddace, watau  "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu".

 Gimbiya da ɗiyar maigadi duk sunji maganar sa, kuma sun tsargu da ita. Sai suka shiga cikin nadama da damuwa, har sai da Sarki ya lura da hakan.


Koda sarki yaji haka, kuma ya lura da alamar damuwa a fuskokin waɗannan mataye biyu, sai ya ƙara neman cikakken bayani na gaskiya game da wannan lamari. 


Ɗiyar maigadi ta bayar da labarin yadda  ta ɗaurawa kanta aure cikin kuskure da wannan matashi, sannan ta rufe cewa "Ƙaddara ta kenan, kuma bana tuba game da faruwar hakan"

Gimbiya ma ta yiwa sarki bayanin yadda ta shafe lokaci da matashin cikin kuskure, tare da rufewa da faɗin "Ƙaddara ta kenan, bana da-na-sanin faruwar hakan!"

Ko da jin haka, sai wannan budurwa da za a ɗaurawa aure tace "Ya sarkin duniya, abinda ƙaddara ta bani fa, babu mai karɓe mini shi daga gare ni!"

Sarki ya cika da mamakin wannan abu, sannan ya shiga shawarwari da na kusa dashi, daga nan sai ya yanke ɓatsayar sa game da abin, ya sallami mutane.

   Da gari ya waye, ya shirya biki. Ya yiwa matashi Sagardatta kyautar ƙauyuka dubu na ɓasarautar sa baya da zinariya da tarin dukiya. Sannan ya aurar dashi ga ɗiyar sa Gimbiya, tare da naɗa shi a matsayin magajin sarautar sa bayan rasuwar sa.

Ita ma waccan amarya da ɗiyar wancan maigadi, duk sun samu cikar burikan su na auren matashi Sagardatta daga iyayen su bayan an shirya biki gwargwadon ƙarfin n su.


Daga nan matashin yasa aka  gina masa gagarumar fada, sannan bai yi fushi da mahaifan sa ba kasancewar ya gamsu da karatunsa cewa"Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu",  ya gayyato iyayen tare da yanuwan sa zuwa wannannfada dominmsu rayu tare dashi, haka suka wanzu cikin farin ciki.


Darasi: Akwai darussa masu yawa a hikayar gwargwadon fahimtar makaranci, amma dai kaɗan daga ciki sun haɗar da:-

Duk abinda aka ɓatar wajen samun ilimi (hikima) matsawar anyi aiki dashi za a ci riba a gaba, haka kuma a sani cewa sai ansha wuya akan sha daɗi. Sannan, yana da kyau Kayi iya kokarin ka akan lamurorin rayuwa, amma ka barwa ƙaddara dama tayi aikin ta.. domin "Abinda aka ƙaddarta maka kaɗai kake iya samu"