ZUWAN TURAWA ZARIA
Kashi na biyu
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
Sarkin Zazzau Kwasau ya gamsar da zuciyarsa cewa ko kaɗan ba zaiyi biyayya ga turawa ba, tunda kasar sace ba tasu ba. Kuma ba addini ɗaya gare suba. Don haka ya soma tunanin mafita.
Akan haka ya aike wa Sarkin Kano Aliyu Babba wasikar neman tallafi, yana mai shaida masa cewar kiristoci sun yawaita a Zazzau, har kuma sun yi kaka gida gareta tare da maisheta mallakinsu, don haka yana neman mafita.
Ana haka sai rikicin kisan Kyaftin Moloney ya bijiro.
Shi Kyaftin Moloney, shine Rasdan na Kyaffi. Ita kuwa Kyaffi tana karkashin daular Zazzau ne a lokacin. Kuma Sunan shugabanta wanda yake a matsayin wakilin sarkin Zazzau a Kyaffi shine Magaji Dan Yamusa.
Akace rannan Kyaftin Moloney ya tara mutane yana musu jawabi, yana karanto turanci garesu, wani bakin mutum kuma yana tafintan abin da duk ya faɗa.
Magaji Dan Yamusa da tarin wasu jama'a duk suna wurin.
Kwatsam sai rashin fahimta ya dabaibaye tafintan kyaftin Moloney sakamakon tsauraran kalmomin turancin da Moloney ke karantawa, shikuma tafinta sai ya rinka yiwa turancin fassarar kalma da kalma..
Akan haka ya faɗawa mutane cewar turawa keda iko dasu, da komai nasu. Har matayensu ma mallakin turawa ne.
Ance kafin a ankara sai ganin kan Kyaftin Moloney akayi yana mirginawa a kasa, Magaji Dan Yamusa ya saro shi.
Daga nan faɗa ya ɓarke tsakanin mutanen Magaji da dakarun Moloney.
Daga karshe dai, Magaji Dan Yamusa ya gudu da tawagarsa zuwa kano. Sarkin Kano Alu Babba yaji daɗin abinda Bakonsa yayi, ya karrama shi tare da bashi mafaka.
Duk da cewar akwai saɓanin inda wannan rikici ya auku, shin a Keffi ne ko a Zaria, amma dai turawa sun ɗora alhakin faruwar hakan akan Daular Zazzau, tunda acikin ikon ta abin ya faru.
Sannan kuma sun damu matuka bisa abinda Sarkin Kano yayi, wannan yasa suka sake ɗaura aniya da kaimin tafiya kano da yaki duk da cewa daman fakonta sukeyi.
Ganin haka sai Sarki Kwasau ya soma shirin guduwa, saboda ya tabbatar abinda zai faru ba mai daɗi bane.
Ya sake aikewa da wasika ga Sarki Alu Babba na kano yana sanar masa da cewar lallai ba-suga ta zama ba, haɗari gagarumi na zuwa garesu.
Sukuwa turawa sai suka ji tsoron idan Sarkin Zazzau ya gudu da mutanensa, to fa zaije ya haɗu ne da Sarkin Kano su kara karfi, don haka sai suka baza dakarunsu akan hanyoyin Zaria zuwa kano, zaria zuwa Katsina da Zaria zuwa Bauchi, da niyar hana sarkin gudu ko kuma a kame shi idan ya gudo.
Rannan sai kurum Rasdan na zaria watau kyaftin Abadie, ya aikewa Sarki Kwasau gayyata domin tattaunawa.
Sarki Kwasau ya fusata da haka, yace don me kamar kyaftin Abadie kirista da yake a kasarsa zai kira shi yazo, don haka ba zai jeba.
Daga nan sai turawa suka samu yadda suke so, suka turo dakaru masu ɗumbin yawa cikin zaria, suka yiwa fadar Sarki kwasau kawanya, sannan suka shiga suka kama shi tare tafiya dashi Wushishi. Acan suka tsare shi har Allah yayi masa rasuwa.
Kuma an samu cewar Sarki Kwasau yayi rubututtuka dangane da yadda aka kamashi da halin daya tsinci kansa. Aciki akwai wata takarda mai suna 'Nuzhatul Asiyr' inda ya rubuta cewar turawa sun kama shine bisa kin yi musu biyayya, a yammacin wata ranar jumua cikin kwanaki goman karshe na watan Jumada Ula. (dai-dai da 19-satumba-1902).
Sannan kuma ya bayyana farin cikinsa bisa yadda suka kamadhi ba tare daya bi umsrninsuba ya zauna akarkadhinsu, hsr ma ya kamanta kansa da mutanen Ashabul Kahfi a wata waka ea aka samu ya rubuta.
Daga karshe, sai turawa suka naɗa Galadima Salmanu sarkin Zazzau a farkon shekarar 1903.
Kashi na biyu
Daga Sadiq Tukur Gwarzo
Sarkin Zazzau Kwasau ya gamsar da zuciyarsa cewa ko kaɗan ba zaiyi biyayya ga turawa ba, tunda kasar sace ba tasu ba. Kuma ba addini ɗaya gare suba. Don haka ya soma tunanin mafita.
Akan haka ya aike wa Sarkin Kano Aliyu Babba wasikar neman tallafi, yana mai shaida masa cewar kiristoci sun yawaita a Zazzau, har kuma sun yi kaka gida gareta tare da maisheta mallakinsu, don haka yana neman mafita.
Ana haka sai rikicin kisan Kyaftin Moloney ya bijiro.
Shi Kyaftin Moloney, shine Rasdan na Kyaffi. Ita kuwa Kyaffi tana karkashin daular Zazzau ne a lokacin. Kuma Sunan shugabanta wanda yake a matsayin wakilin sarkin Zazzau a Kyaffi shine Magaji Dan Yamusa.
Akace rannan Kyaftin Moloney ya tara mutane yana musu jawabi, yana karanto turanci garesu, wani bakin mutum kuma yana tafintan abin da duk ya faɗa.
Magaji Dan Yamusa da tarin wasu jama'a duk suna wurin.
Kwatsam sai rashin fahimta ya dabaibaye tafintan kyaftin Moloney sakamakon tsauraran kalmomin turancin da Moloney ke karantawa, shikuma tafinta sai ya rinka yiwa turancin fassarar kalma da kalma..
Akan haka ya faɗawa mutane cewar turawa keda iko dasu, da komai nasu. Har matayensu ma mallakin turawa ne.
Ance kafin a ankara sai ganin kan Kyaftin Moloney akayi yana mirginawa a kasa, Magaji Dan Yamusa ya saro shi.
Daga nan faɗa ya ɓarke tsakanin mutanen Magaji da dakarun Moloney.
Daga karshe dai, Magaji Dan Yamusa ya gudu da tawagarsa zuwa kano. Sarkin Kano Alu Babba yaji daɗin abinda Bakonsa yayi, ya karrama shi tare da bashi mafaka.
Duk da cewar akwai saɓanin inda wannan rikici ya auku, shin a Keffi ne ko a Zaria, amma dai turawa sun ɗora alhakin faruwar hakan akan Daular Zazzau, tunda acikin ikon ta abin ya faru.
Sannan kuma sun damu matuka bisa abinda Sarkin Kano yayi, wannan yasa suka sake ɗaura aniya da kaimin tafiya kano da yaki duk da cewa daman fakonta sukeyi.
Ganin haka sai Sarki Kwasau ya soma shirin guduwa, saboda ya tabbatar abinda zai faru ba mai daɗi bane.
Ya sake aikewa da wasika ga Sarki Alu Babba na kano yana sanar masa da cewar lallai ba-suga ta zama ba, haɗari gagarumi na zuwa garesu.
Sukuwa turawa sai suka ji tsoron idan Sarkin Zazzau ya gudu da mutanensa, to fa zaije ya haɗu ne da Sarkin Kano su kara karfi, don haka sai suka baza dakarunsu akan hanyoyin Zaria zuwa kano, zaria zuwa Katsina da Zaria zuwa Bauchi, da niyar hana sarkin gudu ko kuma a kame shi idan ya gudo.
Rannan sai kurum Rasdan na zaria watau kyaftin Abadie, ya aikewa Sarki Kwasau gayyata domin tattaunawa.
Sarki Kwasau ya fusata da haka, yace don me kamar kyaftin Abadie kirista da yake a kasarsa zai kira shi yazo, don haka ba zai jeba.
Daga nan sai turawa suka samu yadda suke so, suka turo dakaru masu ɗumbin yawa cikin zaria, suka yiwa fadar Sarki kwasau kawanya, sannan suka shiga suka kama shi tare tafiya dashi Wushishi. Acan suka tsare shi har Allah yayi masa rasuwa.
Kuma an samu cewar Sarki Kwasau yayi rubututtuka dangane da yadda aka kamashi da halin daya tsinci kansa. Aciki akwai wata takarda mai suna 'Nuzhatul Asiyr' inda ya rubuta cewar turawa sun kama shine bisa kin yi musu biyayya, a yammacin wata ranar jumua cikin kwanaki goman karshe na watan Jumada Ula. (dai-dai da 19-satumba-1902).
Sannan kuma ya bayyana farin cikinsa bisa yadda suka kamadhi ba tare daya bi umsrninsuba ya zauna akarkadhinsu, hsr ma ya kamanta kansa da mutanen Ashabul Kahfi a wata waka ea aka samu ya rubuta.
Daga karshe, sai turawa suka naɗa Galadima Salmanu sarkin Zazzau a farkon shekarar 1903.
No comments:
Post a Comment