TARIHIN KAFUWAR DAULAR ZAZZAU
Kashi na Uku
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
KAFUWAR DAULAR ZAZZAU
Da yawan masana na kallon yawan karuwar mazauna waɗannan tsoffin wurare dake kasar zazzau da kuma karancin tsaro a garesu yasa sukayi shawarar ajiye kiyayyar juna gami da yin ganuwa wadda zata haɗe kusan ɗaukacin garuruwan tare da samar da shugaba guda ɗaya. Wannan kuwa shine asalin samuwar daular zazzau.
Marubucin tarihi Abdullahi Smith ya faɗi cewar Zaria ta soma ne sa'ar da gidaje suka soma wanzuwa a waɗancan yankuna. Ya zamana kowanne gida yana cikin ikon maigidan, to sai kuma unguwanni ko kauyuka suka haɗu karkashin ikon mai unguwa.
Daga baya kuwa sai waɗannan unguwannin suka yanke shawarar samar da babban gari a cikin ganuwa ɗaya tare da zamowa karkashin ikon mutum ɗaya mai suna Sarki.
Ana tsammanin shugabanin kauyen Kufena ne suka soma assasa wannan shawara, sune kuma suka jagoranci ginin ganuwar wadda ta zagaye yankinsu na Kufena, da kauyukan Dala, Kona, Madarkachi, Tukur- Tukur, da sauransu.
Tsawon ganuwar ance yakai kimanin mil dubu 24 daga yammaci zuwa gabashi.
Ance da Fari an sanyawa garin suna 'Garin ɗan zau' ne, watau sunan maharbin daya kafa Kufena, daga baya ne ake cewa Zazzau.
Sai dai wasu na ganin Zazzau ɗin sunan wata takobin sihiri ce dake garin wadda ake ɗauka ayi rantsuwa ko asha alwashi da ita tun a lokacin maguzanci.
Baya da haka, littafin tarihin kano ya nuna garin zaria ya wanzu a wani wuri kusa da birnin zazzau na yanzu a zamanin sarki Kanajeji wanda ya kawowa garin yaki har kuma aka halaka sarkinsu a wani wuri mai suna Gadaz.
Duk wannan, tana iya yiwuwa anyi kafin kafuwar wannan ganuwar ne.
Wani bature mai suna Dr. Baikie ya wuce ta zaria a shekarar 1862, zamanin mulkin sarkin Zaria Abdullahi, shine ya ruwaito cewar zaria nada gagarumar ganuwa, wadda kaurinta zaiyi kimanin mil goma, sannan akwai kofofi takwas a zagaye da ita. Sai kuma wata kofa da ya gani an ciketa mai suna Kofar kuyambana.
Shima Paul Staundinger, wani bature ne daya ziyarci zaria a shekarar 1880, kuma ya faɗa cewar a kowacce kofar gari dake zari akwai murfi na katako da ake rufe shi da masakali, sannan akwai dogari dake zama yana amsar kuɗin farin wuri ga dukkan manoman dake shigo da hatsi cikin birnin daga kauyuka, amma shi Paul ɗin da tawagarsa basu bada komai ba.
KOFOFIN ZARIA DA TARIHIN SU
Kofofi shidda ne akace tsoffi da aka soma fitarwa tun zamanin da aka ginawa garin ganuwa.
Kofofin kuwa sune:-
1. Kofar Gayan.
Ance an sanya mata suna ne daga tafkin Gayan wanda ke kudancin kofar saboda muhimmancin sa ga rayuwar mazauna birnin zazzau.
2. Kofar Kuyambana
Ance zamanin Sarauniya Amina aka ɓusa wannan kofa, lokacin da taje yaki garin kuyambana ta karɓe ikonsa, ta ɗora wani baranta ya zama hakimi a garin. Sai aka ɓusa kofar tayadda mutanen zaria dana kuyambana zasu rinka saduwa da juna cikin sauki.
3. Kofar Tukur-Tukur
Da fari an sanyawa kofar suna ne daga dutsen Tukur-Tukur, kuma da haka aka santa tsawon lokaci.
Amma sai sunan kofar ya sauya zuwa Kofar Kibau/Kibo a zamanin da Sarkin Ningi Haruna ya kawo farmakin yaki Zaria lokacin mulkin sarkin zaria Sambo. Zazzagawa suka shige cikin ganjwa tare da rufe kofa. Sadaukan Ningi kuwa sai sukayi ruwan kibiyoyiƴga birnin na zaria.
Ta wannan kofa mutanen da suka ɓullo daga zamfara, kebbi, Yauri da Gobir suke shigowa zaria.
4. Kofar Doka
Wasu sunce kofar ta samo asali ne daga bishiyar Doka dake wajajen kofar. Amma wasu sunce an saya mata wannan suna ne daga wani dogari mai tsaron ta mai suna Doka.
5. Kofar Bai.
Ance ainihi, ana kiran tane da suna kofar Bayan gidan sarki. Daga baya ake yankewa ace mata kofar Bai.
Kuma ta cikin tane mutanen yankin Bauchi ke shiga Zaria.
6. Kofar Kona
Ance ana kiranta da suna Kofar kona saboda ta cikinta Malaman Kona suka shigo zaria.
Shi kona wani kauye ne da akace wasu malamai suka kafa. Asalin sunasa ance ya samu ne lokacin da malaman suka zo shigewa suna neman wurin zama, sai shugabansu ya lura da kyawun wurin, don haka yake tambayar sauran malaman cewa 'ko nan zamu zauna?' Sai suka amsa masa da gamsuwar zama a wurin.
Daga baya da akazo ginin ganuwa sai shashin garin ya shigo cikin birni, don haka suka yanke shawarar barin kauyen nasu na Kona tare da komawa cikin zazzau da zama.
Waɗannan sune tsoffin kofofin da akace sun jima a zazzau, amma daga bisani an samu fasa wasu kofofin kamar su Kofar Jatau, Kofar Galadima da kofar Matar-kwasa wadda akafi kira da Sabuwar kofa.
Kashi na Uku
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
KAFUWAR DAULAR ZAZZAU
Da yawan masana na kallon yawan karuwar mazauna waɗannan tsoffin wurare dake kasar zazzau da kuma karancin tsaro a garesu yasa sukayi shawarar ajiye kiyayyar juna gami da yin ganuwa wadda zata haɗe kusan ɗaukacin garuruwan tare da samar da shugaba guda ɗaya. Wannan kuwa shine asalin samuwar daular zazzau.
Marubucin tarihi Abdullahi Smith ya faɗi cewar Zaria ta soma ne sa'ar da gidaje suka soma wanzuwa a waɗancan yankuna. Ya zamana kowanne gida yana cikin ikon maigidan, to sai kuma unguwanni ko kauyuka suka haɗu karkashin ikon mai unguwa.
Daga baya kuwa sai waɗannan unguwannin suka yanke shawarar samar da babban gari a cikin ganuwa ɗaya tare da zamowa karkashin ikon mutum ɗaya mai suna Sarki.
Ana tsammanin shugabanin kauyen Kufena ne suka soma assasa wannan shawara, sune kuma suka jagoranci ginin ganuwar wadda ta zagaye yankinsu na Kufena, da kauyukan Dala, Kona, Madarkachi, Tukur- Tukur, da sauransu.
Tsawon ganuwar ance yakai kimanin mil dubu 24 daga yammaci zuwa gabashi.
Ance da Fari an sanyawa garin suna 'Garin ɗan zau' ne, watau sunan maharbin daya kafa Kufena, daga baya ne ake cewa Zazzau.
Sai dai wasu na ganin Zazzau ɗin sunan wata takobin sihiri ce dake garin wadda ake ɗauka ayi rantsuwa ko asha alwashi da ita tun a lokacin maguzanci.
Baya da haka, littafin tarihin kano ya nuna garin zaria ya wanzu a wani wuri kusa da birnin zazzau na yanzu a zamanin sarki Kanajeji wanda ya kawowa garin yaki har kuma aka halaka sarkinsu a wani wuri mai suna Gadaz.
Duk wannan, tana iya yiwuwa anyi kafin kafuwar wannan ganuwar ne.
Wani bature mai suna Dr. Baikie ya wuce ta zaria a shekarar 1862, zamanin mulkin sarkin Zaria Abdullahi, shine ya ruwaito cewar zaria nada gagarumar ganuwa, wadda kaurinta zaiyi kimanin mil goma, sannan akwai kofofi takwas a zagaye da ita. Sai kuma wata kofa da ya gani an ciketa mai suna Kofar kuyambana.
Shima Paul Staundinger, wani bature ne daya ziyarci zaria a shekarar 1880, kuma ya faɗa cewar a kowacce kofar gari dake zari akwai murfi na katako da ake rufe shi da masakali, sannan akwai dogari dake zama yana amsar kuɗin farin wuri ga dukkan manoman dake shigo da hatsi cikin birnin daga kauyuka, amma shi Paul ɗin da tawagarsa basu bada komai ba.
KOFOFIN ZARIA DA TARIHIN SU
Kofofi shidda ne akace tsoffi da aka soma fitarwa tun zamanin da aka ginawa garin ganuwa.
Kofofin kuwa sune:-
1. Kofar Gayan.
Ance an sanya mata suna ne daga tafkin Gayan wanda ke kudancin kofar saboda muhimmancin sa ga rayuwar mazauna birnin zazzau.
2. Kofar Kuyambana
Ance zamanin Sarauniya Amina aka ɓusa wannan kofa, lokacin da taje yaki garin kuyambana ta karɓe ikonsa, ta ɗora wani baranta ya zama hakimi a garin. Sai aka ɓusa kofar tayadda mutanen zaria dana kuyambana zasu rinka saduwa da juna cikin sauki.
3. Kofar Tukur-Tukur
Da fari an sanyawa kofar suna ne daga dutsen Tukur-Tukur, kuma da haka aka santa tsawon lokaci.
Amma sai sunan kofar ya sauya zuwa Kofar Kibau/Kibo a zamanin da Sarkin Ningi Haruna ya kawo farmakin yaki Zaria lokacin mulkin sarkin zaria Sambo. Zazzagawa suka shige cikin ganjwa tare da rufe kofa. Sadaukan Ningi kuwa sai sukayi ruwan kibiyoyiƴga birnin na zaria.
Ta wannan kofa mutanen da suka ɓullo daga zamfara, kebbi, Yauri da Gobir suke shigowa zaria.
4. Kofar Doka
Wasu sunce kofar ta samo asali ne daga bishiyar Doka dake wajajen kofar. Amma wasu sunce an saya mata wannan suna ne daga wani dogari mai tsaron ta mai suna Doka.
5. Kofar Bai.
Ance ainihi, ana kiran tane da suna kofar Bayan gidan sarki. Daga baya ake yankewa ace mata kofar Bai.
Kuma ta cikin tane mutanen yankin Bauchi ke shiga Zaria.
6. Kofar Kona
Ance ana kiranta da suna Kofar kona saboda ta cikinta Malaman Kona suka shigo zaria.
Shi kona wani kauye ne da akace wasu malamai suka kafa. Asalin sunasa ance ya samu ne lokacin da malaman suka zo shigewa suna neman wurin zama, sai shugabansu ya lura da kyawun wurin, don haka yake tambayar sauran malaman cewa 'ko nan zamu zauna?' Sai suka amsa masa da gamsuwar zama a wurin.
Daga baya da akazo ginin ganuwa sai shashin garin ya shigo cikin birni, don haka suka yanke shawarar barin kauyen nasu na Kona tare da komawa cikin zazzau da zama.
Waɗannan sune tsoffin kofofin da akace sun jima a zazzau, amma daga bisani an samu fasa wasu kofofin kamar su Kofar Jatau, Kofar Galadima da kofar Matar-kwasa wadda akafi kira da Sabuwar kofa.
No comments:
Post a Comment