TARIHIN KAFUWAR DAULAR ZAZZAU
Kashi na Biyar
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
Akwai daga tarihin zazzau labarin wannan takobin mai suna Zazzau, wadda wasu ke kallon daga sunan ta aka sanyawa daular suna. Akwai masu kallon cewa asalin takobin ta sarki Gunguma ce wadda ya yaki abokan gaba da ita, don haka aka ajiyeta a masarautar bayan rasuwarsa ta yadda kowanne sarki yazo sai yasha alwashi da ita.
Haka kuma babu takamaimen lokacin da sarkin Gunguma ya soma sarautar zazzau da kuma adadin shekarun da yayi dashi da sarakunan nan goma sha shidda da suka gabace. Watakila hakan ta faru kasancewar zazzau bata da tsohon ajiyayyen rubutaccen tarihi misalin irin na masarautar kano. To amma duk da haka, an hakikance rayuwar sarakunan ta wanzu ne sama da karni na goma sha ɗaya, zuwa kasa da karni na goma sha biyar.
Haka kuma Leo Africanus ya ruwaito cewar a wajajen shekara ta 5012 miladiyya daular Songhai ta kasar Mali da Sarki Muhammadu Askiya na ɗaya ke jagoranta ta kwace ikon daular zaria. Watakila a lokacin sarki Muhammadu Abu (sarki na goma sha takwas) ne ke sarauta, ko kuma tana iya yiwuwa Muhammadu Abu ya hau sarauta ne da sahalewar torankawan Mali waɗanda suka kawo musulunci Zazzau tunda a jerin sunayen sarakunan nasa ne yafara da Muhammadu.
Daga nan sai wani abu da akaji akan sarkin zaria na 22 Bakwa Turunku.
Ance shine mahaifin Sarauniya Amina, da 'yar uwarta Khadija mai lakabin zaria wanda ya taso da cibiyar daular zazzau daga wani wuri zuwa wani.
Khadija ce akace ta kafa wani ɗan kauye mai suna zaria, wanda yanzu ya bunkasa har cibiyar daular zazzau ke ciki.
Ita kuwa Amina anfi cewa ita sarauniya ce wadda sunan ta ya shahara a kasar hausa duk kuwa da kasancewar babu sunanta a jerin sarakunan Zazzau da aka bayar.
Wasu na ganin abubuwa biyu ne suka sanya haka.
Na farko akace bata zauna a zazzau tayi mulki ba a sanda ta zamo shugaba, sai kawai ta fita cinye garuruwa da faɗaɗa girman daularta.
Abu na biyu kuwa shine wanda ake kallon Amina a matsayin sarauniya, kuma shugabar mayaka wadda ba itace lamba ɗaya mai faɗa aji a zazzau ba.
An samu cewar a zazzau ana kiran 'yar sarki da suna Sarauniya, mahaifiyar sarki kuma da suna Iya. Ance waɗannan mataye biyu nada faɗa aji da matukar tasiri a masarautar zazzau
Don haka wasu ke hasashen Amina a sarauniya kurum take, watau ɗiya ga sarki Bakwa Turunku, kuma ɗanuwanta shine wanda ya zama sarki bayan rasuwar Mahaifinsu, ita kuwa sai taci gaba da zamowarta sarauniya, wadda ta fita kasashe yaki na tsawon shekaru har kuma ta mutu acan ba tare da tayi aure ba.
Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ya karyata waɗanda ke cewar ba'a taɓa yin wata mace mai suna Amina a zaria ba a littafinsa 'Infaqul Maisur' inda yace a zamaninta ta cinye garuruwan dake makwabtaka da zaria musamman na Nufawa dana Kwararrafawa. Kuma suna biyanta Jizya. Harma sarkin Nufe ya taɓa aika mata da bayi Arba'in da kuma goro dubu goma. Yace kumu Amina tayi sharafi tsawon shekaru 34.
Amma abu mai gaskata wanzuwar Amina shine wani kufai da ake samu a garuruwan da taci ko ta sauka wanda ake kira da suna 'ganuwar Amina'. Wanda kuma har yanzu akwai ɓurɓushinsa a garuruwa da yawa cikin kasar hausa dana makwabta.
Kari akan kasashen da akace Amina taci galabar yaki akai baya da kasashen Nufawa dana Kwararrafawa, akwai kasar Gwari, kasar kano, kasar katsina, da kasashen yankin Nasarawa.
Kashi na Biyar
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
Akwai daga tarihin zazzau labarin wannan takobin mai suna Zazzau, wadda wasu ke kallon daga sunan ta aka sanyawa daular suna. Akwai masu kallon cewa asalin takobin ta sarki Gunguma ce wadda ya yaki abokan gaba da ita, don haka aka ajiyeta a masarautar bayan rasuwarsa ta yadda kowanne sarki yazo sai yasha alwashi da ita.
Haka kuma babu takamaimen lokacin da sarkin Gunguma ya soma sarautar zazzau da kuma adadin shekarun da yayi dashi da sarakunan nan goma sha shidda da suka gabace. Watakila hakan ta faru kasancewar zazzau bata da tsohon ajiyayyen rubutaccen tarihi misalin irin na masarautar kano. To amma duk da haka, an hakikance rayuwar sarakunan ta wanzu ne sama da karni na goma sha ɗaya, zuwa kasa da karni na goma sha biyar.
Haka kuma Leo Africanus ya ruwaito cewar a wajajen shekara ta 5012 miladiyya daular Songhai ta kasar Mali da Sarki Muhammadu Askiya na ɗaya ke jagoranta ta kwace ikon daular zaria. Watakila a lokacin sarki Muhammadu Abu (sarki na goma sha takwas) ne ke sarauta, ko kuma tana iya yiwuwa Muhammadu Abu ya hau sarauta ne da sahalewar torankawan Mali waɗanda suka kawo musulunci Zazzau tunda a jerin sunayen sarakunan nasa ne yafara da Muhammadu.
Daga nan sai wani abu da akaji akan sarkin zaria na 22 Bakwa Turunku.
Ance shine mahaifin Sarauniya Amina, da 'yar uwarta Khadija mai lakabin zaria wanda ya taso da cibiyar daular zazzau daga wani wuri zuwa wani.
Khadija ce akace ta kafa wani ɗan kauye mai suna zaria, wanda yanzu ya bunkasa har cibiyar daular zazzau ke ciki.
Ita kuwa Amina anfi cewa ita sarauniya ce wadda sunan ta ya shahara a kasar hausa duk kuwa da kasancewar babu sunanta a jerin sarakunan Zazzau da aka bayar.
Wasu na ganin abubuwa biyu ne suka sanya haka.
Na farko akace bata zauna a zazzau tayi mulki ba a sanda ta zamo shugaba, sai kawai ta fita cinye garuruwa da faɗaɗa girman daularta.
Abu na biyu kuwa shine wanda ake kallon Amina a matsayin sarauniya, kuma shugabar mayaka wadda ba itace lamba ɗaya mai faɗa aji a zazzau ba.
An samu cewar a zazzau ana kiran 'yar sarki da suna Sarauniya, mahaifiyar sarki kuma da suna Iya. Ance waɗannan mataye biyu nada faɗa aji da matukar tasiri a masarautar zazzau
Don haka wasu ke hasashen Amina a sarauniya kurum take, watau ɗiya ga sarki Bakwa Turunku, kuma ɗanuwanta shine wanda ya zama sarki bayan rasuwar Mahaifinsu, ita kuwa sai taci gaba da zamowarta sarauniya, wadda ta fita kasashe yaki na tsawon shekaru har kuma ta mutu acan ba tare da tayi aure ba.
Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ya karyata waɗanda ke cewar ba'a taɓa yin wata mace mai suna Amina a zaria ba a littafinsa 'Infaqul Maisur' inda yace a zamaninta ta cinye garuruwan dake makwabtaka da zaria musamman na Nufawa dana Kwararrafawa. Kuma suna biyanta Jizya. Harma sarkin Nufe ya taɓa aika mata da bayi Arba'in da kuma goro dubu goma. Yace kumu Amina tayi sharafi tsawon shekaru 34.
Amma abu mai gaskata wanzuwar Amina shine wani kufai da ake samu a garuruwan da taci ko ta sauka wanda ake kira da suna 'ganuwar Amina'. Wanda kuma har yanzu akwai ɓurɓushinsa a garuruwa da yawa cikin kasar hausa dana makwabta.
Kari akan kasashen da akace Amina taci galabar yaki akai baya da kasashen Nufawa dana Kwararrafawa, akwai kasar Gwari, kasar kano, kasar katsina, da kasashen yankin Nasarawa.
No comments:
Post a Comment