TARIHIN KAFUWAR DAULAR ZAZZAU
Kashi na shidda
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
Sauran sarakunan da akace sunyi sarautar zazzau da shekarun mulkinsu sune kamar haka:- (koda yake akwai saɓanin shekaru daga masu ruwaitowa)
23. Ibrahim 1539-1560
24. Karama 1566-1576
25. Kofa 1576-1578
26. Bako I 1578-1581
27. Aliyu I 1581-1587
28. Ismailu 1587-1568
29. Musa 1598-1599
30. Gabi 1598-1601
31. Hamza 1601-1602
32. Abdaku 1602-1610
33. Burewa 1610-1613
34. Aliyu II 1613-1640
35. Makama Rabo 1640-1641
36. Ibrahim Basuka 1641-1654
37. Bako II 1654-1657
38. Sukwana 1657-1658
39. Aliyu III 1658-1665
40. Ibrahim Dan Aliyu 1665-1668
41. Mamman Abu 1668-1686
42. Sune 1686-1686
43. Bako dan Musa 1696-1701
44. Isiyaku dan Gabi 1701-1703
45. Burema Ashakuka 1703-1704
46. Bako dan Sukwana 1704-1715
47. Muhammadu dan Gunguma 1715-1726
48. Uban Bawa 1726-1733
49. Muhammadu Gabi 1733-1734
50. Abu muhanad Gani 1735
51. Gabir dan Ashakuka 1734-1737
52. Makama Abu 1737-1737
53. Bawo 1737-1757
54. Yunusa 1759-1767
55. Yakubu 1765-1764
56. Aliyu IV 1767-1773
57. Cikkoku 1773-1779
58.Muhammad Maigamo1779-1782
59. Jatau (isiyaku) 1782-1802
60. Makau 1802-1804
Sarakunan zazzau na Fulani Bayan Jihadin Shehu Usmanu ɗan fodio:-
1. Sarkin zazzau Malam Musa 1804-1821
2. Sarkin zazzau Malam Yamusa 1821-1834
3. Sarkin zazzau Malam Abdulkarimu 1834-1846
4. Sarkin zazzau Malam Hammada ( kwana hamsin da uku yayi)
5. Sarkin zazzau Malam Mahamman Sani 1846-1853
6. Sarkin zazzau malam sidi
( shima wata ya yi yana mulki).
7. Sarkin zazzau Malam Abdulsalam 1853-1863
8. Sarkin zazzau Malam Abdullahi 1863-1873
9. Sarkin zazzau Malam Abubakar 1873-1876
10. Sarkin zazzau Malam sambo 1881-1890
11. Sarkin zazzau Malam Yero 1890-1897
12. Sarkin zazzau Malam Kwasau 1897-1903
13. Sarkin zazzau Malam Alu dan Sidi 1903-1920
14. Sarkin zazzau Malam Dalhatu 1920-1924
15. Sarkin zazzau Malam Ibrahim 1924-1936
16. Sarkin zazzau Malam Jafa'ru 1937-1959
17. Sarkin zazzau Alhaji Muhammadu Aminu 1959-1975
18. Sarkin zazzau Alhaji shehu idris 1975 zuwa yanzu.
FADAR ZAZZAU
Ana kiran gidan sarkin zazzau da suna 'gidan Bakwa', kuma yana nan a unguwar da ake kira kofar fada dake tsakanin Madarkachi da Fadamar Bono.
Anan ne kusan duk sarakunan da suka hau karagar mulkin daular suke zama.
Ance tun zamanin Sarki Bakwa Turunku aka gina shi, a wajajen 5036 miladiyya kenan, don haka ma ake kiran gidan da sunan sa.
Wasu suka ce wani maharbi ne ya bada shawarar ayi gidan anan bisa dalilai na tsaro.
Da fari, yace wajen kan tudu ne, zai baiwa jagoran gari damar kallon duk abubuwan dake faruwa a Kufena, Turunku, Hange da sauran unguwannin cikin ganuwa.
Sannan wajen yafi kusa da tsakiyar gari inda da zarar an buga kugen taruwar jama'a, mutane zasu runtomu da gaggawa.
Wannan fada an gina ta da turɓaya ne, kuma an kasa ta gida huɗu. Akwai Fada inda sarki ke zama da fadawa ayi fadanci. Akwai sashen da sarki ke kwanciya. Akwai cikin gida sashen da iyalan sarki suke. Sai kuma tsohuwar gida inda barorin sarki suke.
Amma a karni na goma sha takwas, ance sanannan maginin nan mai suna Muhammadu Durungu, Babban Gwani ya sake sabunta gidan tare da gina masa sabbin ɗakuna na kasaita.
Haka kuma bayan jihadin fulani, sarki na farko watau Mallam Musa bai shiga gidan ba bisa tsoron kada ya zama mai aikata irin abinda hausawan haɓe ke aikatawa kafin jihadi, don haka yayi mulkin zazzau daga gidansa dake unguwar kwarbai.
Wanda ya biyo bayansa Mallam yamusa shima bai dhiga gidan Bakwa ba bisa wancan tsoro, sai yayi mulki a gidansa dake Unguwar kaura.
Daga nan sai Mal Abdulkarim da yazo, shi kuma ya shiga gidan Bakwa yayi sarauta, kuma a lokacinsa akace magini Muhammadu Durungu yayiwa fadar gyara na musamman.
Amma bayan mutuwar sarkin sai wanda ya gajeshi mai suna Hammade yaki shiga fadar, yayi kwanaki yana mulki ya rasu, sarakunan kabilar fulani Bare-bari suka biyo bayansa, suma sai sukayi mulkinsu a Unguwar kaura.
Abdulsalam yayi nasa mulkin a gidansa dake Unguwar Bishar.
Mal Abdullahi yayi mulki a kofar Doka.
Mal Abubakar yayi mulki ba tare daya shiga gidan ba.
Wanda akace ya komowa gidan shine Mal Sambo, kuma tun daga kansa har yanzu sarakunan zazzau na shiga domin yin sarauta.
UNGUWANNIN ZARIA DA TARIHINSU
1. Anguwar Zaria
Nan ne inda birnin zaria yake a yanzu.
Ance asalin sa fili ne babu kowa a wurin. Amma a lokacin da ake gina ganuwar birni zamanin Sarki Bakwa Turunku, sai wata ɗiyar sarki da ake kira Zaria tazo taga wannan wuri, daga nan sai ta nemi mutanen daular Zazzau da akace a lokacin cibiyar su na Turunku su dawo wannan wuri domin bada dama ga magina su kammala ginin fadar Sarki, da ganuwa, da rijiyoyi da kuma gidanta a Unguwar Magajiya.
Don haka ake ganin tun abaya wurin ya zama cibiyar daular na wani lokaci, amma ana kammalawa sai duk suka tashi izuwa sabon waje.
Tun daga nan kuma sai zaria ya zamo tsirarun mutane kaɗai ke rayuwa a wurin har zuwa karni na goma sha takwas da wajen ya haɓaka izuwa birnin zaria.
2. Unguwar Salman Duna
Ance sunan unguwar ya samo ne daga sunan wata mace mai Suna Salma, mata ga sarkin makera Duna da suka shahara a wajen.
Wasu sunce wani maharbi mai suna Bono ne ya soma sarar wajen. Shikuma ya kasance miji ne ga zariya ɗiyar sarki Bakwa Turunku.
Akace wata rana ya fita farauta sai ya riski wurin da ayau ake kira Fadamar Bono, sai ya jima yana farauta har sama da lokacin daya saba idan ya fita gida. Wannan yasa hankalin matarsa ya tashi ta biyo bayansa.
( Sai akace anan ne har taga yankin Zaria kuma ta kayatu da zama a wurin saboda ni'iamar ruwa da yake dashi, inda daga baya ta roki mahaifinta ya komo da jama'arsa wurin kafin a gama aikin gina gari. Ance jajircewar ta bisa haka yasa ake kiran wajen da sunanta)
Amma wasu sunce wannan yanki na Salmanduna sanananne tun da jimawa, domin kuwa sarkin zazzau na farko Gunguma ne ya fara sanyawa aka gyara wurin da nufin fara yin noma a yankin. Daga baya mutane suka soma zama har ya zama unguwa.
Sannan akwai wani yanki mai suna Babban dodo a jikin unguwar Salmanduna, inda akace a baya matattara ce ta bautar iskokai.
Har ma an samu ana yiwa wata iska kirari domin shaida ga bautar da akayi a wurin. Ga kirarin kamar haka:-
Duna na kar kashin kasa
Arne Na gidan Nabijari.
Ko uwanka na Tsoronka
Bakaka mushagala
Mai kallabi da hanjin yaro
Talaka baya iya ajiyeki
Ko ya ijeki me zai baki
Sai dai ya baki bargon doki.
Ba dai ya baki jini ba.
Wani mutum a wurin mai suna Mal Mahmud Aliyu, ya faɗa cewar tun a karni na goma shabiyar wajen ya haɓaka da jama'a sosai saboda waccan bauta da akeyi, kuma sai a karni na goma sha tara ragiwar mutane a wurin tayi kasa.
Kashi na shidda
DAGA SADIQ TUKUR GWARZO
Sauran sarakunan da akace sunyi sarautar zazzau da shekarun mulkinsu sune kamar haka:- (koda yake akwai saɓanin shekaru daga masu ruwaitowa)
23. Ibrahim 1539-1560
24. Karama 1566-1576
25. Kofa 1576-1578
26. Bako I 1578-1581
27. Aliyu I 1581-1587
28. Ismailu 1587-1568
29. Musa 1598-1599
30. Gabi 1598-1601
31. Hamza 1601-1602
32. Abdaku 1602-1610
33. Burewa 1610-1613
34. Aliyu II 1613-1640
35. Makama Rabo 1640-1641
36. Ibrahim Basuka 1641-1654
37. Bako II 1654-1657
38. Sukwana 1657-1658
39. Aliyu III 1658-1665
40. Ibrahim Dan Aliyu 1665-1668
41. Mamman Abu 1668-1686
42. Sune 1686-1686
43. Bako dan Musa 1696-1701
44. Isiyaku dan Gabi 1701-1703
45. Burema Ashakuka 1703-1704
46. Bako dan Sukwana 1704-1715
47. Muhammadu dan Gunguma 1715-1726
48. Uban Bawa 1726-1733
49. Muhammadu Gabi 1733-1734
50. Abu muhanad Gani 1735
51. Gabir dan Ashakuka 1734-1737
52. Makama Abu 1737-1737
53. Bawo 1737-1757
54. Yunusa 1759-1767
55. Yakubu 1765-1764
56. Aliyu IV 1767-1773
57. Cikkoku 1773-1779
58.Muhammad Maigamo1779-1782
59. Jatau (isiyaku) 1782-1802
60. Makau 1802-1804
Sarakunan zazzau na Fulani Bayan Jihadin Shehu Usmanu ɗan fodio:-
1. Sarkin zazzau Malam Musa 1804-1821
2. Sarkin zazzau Malam Yamusa 1821-1834
3. Sarkin zazzau Malam Abdulkarimu 1834-1846
4. Sarkin zazzau Malam Hammada ( kwana hamsin da uku yayi)
5. Sarkin zazzau Malam Mahamman Sani 1846-1853
6. Sarkin zazzau malam sidi
( shima wata ya yi yana mulki).
7. Sarkin zazzau Malam Abdulsalam 1853-1863
8. Sarkin zazzau Malam Abdullahi 1863-1873
9. Sarkin zazzau Malam Abubakar 1873-1876
10. Sarkin zazzau Malam sambo 1881-1890
11. Sarkin zazzau Malam Yero 1890-1897
12. Sarkin zazzau Malam Kwasau 1897-1903
13. Sarkin zazzau Malam Alu dan Sidi 1903-1920
14. Sarkin zazzau Malam Dalhatu 1920-1924
15. Sarkin zazzau Malam Ibrahim 1924-1936
16. Sarkin zazzau Malam Jafa'ru 1937-1959
17. Sarkin zazzau Alhaji Muhammadu Aminu 1959-1975
18. Sarkin zazzau Alhaji shehu idris 1975 zuwa yanzu.
FADAR ZAZZAU
Ana kiran gidan sarkin zazzau da suna 'gidan Bakwa', kuma yana nan a unguwar da ake kira kofar fada dake tsakanin Madarkachi da Fadamar Bono.
Anan ne kusan duk sarakunan da suka hau karagar mulkin daular suke zama.
Ance tun zamanin Sarki Bakwa Turunku aka gina shi, a wajajen 5036 miladiyya kenan, don haka ma ake kiran gidan da sunan sa.
Wasu suka ce wani maharbi ne ya bada shawarar ayi gidan anan bisa dalilai na tsaro.
Da fari, yace wajen kan tudu ne, zai baiwa jagoran gari damar kallon duk abubuwan dake faruwa a Kufena, Turunku, Hange da sauran unguwannin cikin ganuwa.
Sannan wajen yafi kusa da tsakiyar gari inda da zarar an buga kugen taruwar jama'a, mutane zasu runtomu da gaggawa.
Wannan fada an gina ta da turɓaya ne, kuma an kasa ta gida huɗu. Akwai Fada inda sarki ke zama da fadawa ayi fadanci. Akwai sashen da sarki ke kwanciya. Akwai cikin gida sashen da iyalan sarki suke. Sai kuma tsohuwar gida inda barorin sarki suke.
Amma a karni na goma sha takwas, ance sanannan maginin nan mai suna Muhammadu Durungu, Babban Gwani ya sake sabunta gidan tare da gina masa sabbin ɗakuna na kasaita.
Haka kuma bayan jihadin fulani, sarki na farko watau Mallam Musa bai shiga gidan ba bisa tsoron kada ya zama mai aikata irin abinda hausawan haɓe ke aikatawa kafin jihadi, don haka yayi mulkin zazzau daga gidansa dake unguwar kwarbai.
Wanda ya biyo bayansa Mallam yamusa shima bai dhiga gidan Bakwa ba bisa wancan tsoro, sai yayi mulki a gidansa dake Unguwar kaura.
Daga nan sai Mal Abdulkarim da yazo, shi kuma ya shiga gidan Bakwa yayi sarauta, kuma a lokacinsa akace magini Muhammadu Durungu yayiwa fadar gyara na musamman.
Amma bayan mutuwar sarkin sai wanda ya gajeshi mai suna Hammade yaki shiga fadar, yayi kwanaki yana mulki ya rasu, sarakunan kabilar fulani Bare-bari suka biyo bayansa, suma sai sukayi mulkinsu a Unguwar kaura.
Abdulsalam yayi nasa mulkin a gidansa dake Unguwar Bishar.
Mal Abdullahi yayi mulki a kofar Doka.
Mal Abubakar yayi mulki ba tare daya shiga gidan ba.
Wanda akace ya komowa gidan shine Mal Sambo, kuma tun daga kansa har yanzu sarakunan zazzau na shiga domin yin sarauta.
UNGUWANNIN ZARIA DA TARIHINSU
1. Anguwar Zaria
Nan ne inda birnin zaria yake a yanzu.
Ance asalin sa fili ne babu kowa a wurin. Amma a lokacin da ake gina ganuwar birni zamanin Sarki Bakwa Turunku, sai wata ɗiyar sarki da ake kira Zaria tazo taga wannan wuri, daga nan sai ta nemi mutanen daular Zazzau da akace a lokacin cibiyar su na Turunku su dawo wannan wuri domin bada dama ga magina su kammala ginin fadar Sarki, da ganuwa, da rijiyoyi da kuma gidanta a Unguwar Magajiya.
Don haka ake ganin tun abaya wurin ya zama cibiyar daular na wani lokaci, amma ana kammalawa sai duk suka tashi izuwa sabon waje.
Tun daga nan kuma sai zaria ya zamo tsirarun mutane kaɗai ke rayuwa a wurin har zuwa karni na goma sha takwas da wajen ya haɓaka izuwa birnin zaria.
2. Unguwar Salman Duna
Ance sunan unguwar ya samo ne daga sunan wata mace mai Suna Salma, mata ga sarkin makera Duna da suka shahara a wajen.
Wasu sunce wani maharbi mai suna Bono ne ya soma sarar wajen. Shikuma ya kasance miji ne ga zariya ɗiyar sarki Bakwa Turunku.
Akace wata rana ya fita farauta sai ya riski wurin da ayau ake kira Fadamar Bono, sai ya jima yana farauta har sama da lokacin daya saba idan ya fita gida. Wannan yasa hankalin matarsa ya tashi ta biyo bayansa.
( Sai akace anan ne har taga yankin Zaria kuma ta kayatu da zama a wurin saboda ni'iamar ruwa da yake dashi, inda daga baya ta roki mahaifinta ya komo da jama'arsa wurin kafin a gama aikin gina gari. Ance jajircewar ta bisa haka yasa ake kiran wajen da sunanta)
Amma wasu sunce wannan yanki na Salmanduna sanananne tun da jimawa, domin kuwa sarkin zazzau na farko Gunguma ne ya fara sanyawa aka gyara wurin da nufin fara yin noma a yankin. Daga baya mutane suka soma zama har ya zama unguwa.
Sannan akwai wani yanki mai suna Babban dodo a jikin unguwar Salmanduna, inda akace a baya matattara ce ta bautar iskokai.
Har ma an samu ana yiwa wata iska kirari domin shaida ga bautar da akayi a wurin. Ga kirarin kamar haka:-
Duna na kar kashin kasa
Arne Na gidan Nabijari.
Ko uwanka na Tsoronka
Bakaka mushagala
Mai kallabi da hanjin yaro
Talaka baya iya ajiyeki
Ko ya ijeki me zai baki
Sai dai ya baki bargon doki.
Ba dai ya baki jini ba.
Wani mutum a wurin mai suna Mal Mahmud Aliyu, ya faɗa cewar tun a karni na goma shabiyar wajen ya haɓaka da jama'a sosai saboda waccan bauta da akeyi, kuma sai a karni na goma sha tara ragiwar mutane a wurin tayi kasa.
No comments:
Post a Comment