TARIHIN JIHADIN SHEHU USMANU MUJADDADI, DAN FODIO.
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na huɗu.
Shehu Usmanu Dan fodio yayi godiya ga Allah bisa ni'imar da yayi masa bayan ya sauka a Gudu wurin hijirarsa, sannan ya nemi a gabato masa da gadon wa'azinsa.
Daga nan sai ya tara jama'arsa duka a wurin, sannan ya hau kan gadon wa'azinsa yana musu wa'azi.
Anan ne yace musu "Na cire sarautar dukkan wani mai sarauta sai wanda yazo mini nan"
A lokacin kuwa, Sarki Ashiru ne kaɗai yazo gareshi, don haka da akayi yakin jihadi aka barshi da sarautarsa.
Haka kuma, shehu yayi addu'a ga mutanensa cewa "Duk wanda ya fitad dani daga gidana, Allah ya fitar dashi daga nashi." Mutane suka amsa da Amin. Akayi addua aka tashi.
Daga nan sai Kaninsa Abdullahi yazo gareshi yayi masa mubaya'a (ta yin jihadi), sai kuma ɗansa Muhammad Bello shima yazo yayi sannan sai abokinsa Ummaru Alkammu, sai sauran jama'a kuma duka kowa yazo yayi.
Daga wannan rana, Shehu Usmanu da Jama'arsa suka ɗaura shirin soma yaki da sarakunan duk da basu biyo wannan tsari nasu ba.
FARA YAKIN JIHADI
Sa'ar da Shehu Usmanu da jama'arsa suka yi hijira, sai Sarkin Gobir Yumfa ya umarci sarakunan garuruwansa da cewar, su kame duk wani mai shirin zuwa ga Shehu Usmanu.
Ai kuwa sai suka shiga fitinar musulmai mabiya Shehu Usmanu da kisa, azabtarwa gami da kwace dukiya.
Da wannan hali ya k'azanta, sai musulman da sukayi hijira suka soma fita yakin jihadi izuwa garuruwa.
Ya zama suna kame kananun garuruwa a hankali har sukazo wani gari waishi Giniga, yaki kuwa yayi tsamari anan.
Ance duk da an halaka musulmai da dama a yakin, wasu manya kuma daga tawagar Shehu sunyi shahada, amma dai saida sukayi nasarar kame garin. Suka kashe na kashewa, wasu kuma aka kame su.
Daga nan suka fita yaki zuwa Matan Kari, nan ma suka ci garin da yaki, suka sake nufar wani gari mai suna Wata Alkarya, shima suka cinyeshi da yaki, sannan suka samu nasarar cinye garin K'wanni da yaki.
A wannan shekara ta farko dai, an gwabza yake-yake masu tsauri, amma cikin ikon Allah duk mutanen shehu ke samun nasara.
Akwai Yakin Kwato da akayi a shekarar, shikuwa yaki ne mafi girma wanda sai dai a Kwatantashi da Yakin Badar a tarihin kafuwar Musulunci, ko kuma yakin Daukar girma a tarihin Yakin Jihadin mutanen shehu Usmanu a Kano.
Sarkin Gobir fa sai hankalinsa ya dugunzuma, ya shiga shirin yaki haikan.
Ya aike da takardu na neman taimako izuwa sarakunan Katsina, Kano, Zazzau, Daura da Azbin, duk kuwa saida suka bashi tallafin daya nema, sannan suma suka ɗaura ɗamarar yaki da duk wani mai alaka da Shehu Usmanu a biranensu.
Daga nan Sarkin Gobir Yumfa ya fita daga garinsa, ya kwana a 'Bore, sannan yahau ya riski Gamba, yabi ta Makida, sannan ya sauka a Tsara ya kwana. Daga nan sai gashi a Janar-Sarki ya kwana biyu anan yana sauraren wasu k'arin dakaru. Bayan sun isone ya fuskanto Gudu da gagarumar runduna.
Koda Shehu da Mabiyansa suka ji Labarin yaki na gabato su, sai suka ɗau harama suma.
Wazirin Shehu, kuma kaninsa, watau Abdullahi, ya taso da rundunar mayaka izuwa gefen wasu gidaje suka sauka suna jira, har yamma tayi basuji komai ba, sai suka koma da baya.
A kwana na biyu ma suka sake yin kamar haka, amma babu abinda ya faru.
Sai a kwana na uku ne wasu 'yan uwansu fulani suka iso garesu a sukwane, suka shaida musu cewar daga cikin rundunar sarki Yumfa suka sato jiki, kuma yaki ya kusa zuwa garesu, tunda kuwa rundunar tana garin Ayame ne, tsakaninsu da garin kuwa tafiyar yini ɗaya ce..
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na huɗu.
Shehu Usmanu Dan fodio yayi godiya ga Allah bisa ni'imar da yayi masa bayan ya sauka a Gudu wurin hijirarsa, sannan ya nemi a gabato masa da gadon wa'azinsa.
Daga nan sai ya tara jama'arsa duka a wurin, sannan ya hau kan gadon wa'azinsa yana musu wa'azi.
Anan ne yace musu "Na cire sarautar dukkan wani mai sarauta sai wanda yazo mini nan"
A lokacin kuwa, Sarki Ashiru ne kaɗai yazo gareshi, don haka da akayi yakin jihadi aka barshi da sarautarsa.
Haka kuma, shehu yayi addu'a ga mutanensa cewa "Duk wanda ya fitad dani daga gidana, Allah ya fitar dashi daga nashi." Mutane suka amsa da Amin. Akayi addua aka tashi.
Daga nan sai Kaninsa Abdullahi yazo gareshi yayi masa mubaya'a (ta yin jihadi), sai kuma ɗansa Muhammad Bello shima yazo yayi sannan sai abokinsa Ummaru Alkammu, sai sauran jama'a kuma duka kowa yazo yayi.
Daga wannan rana, Shehu Usmanu da Jama'arsa suka ɗaura shirin soma yaki da sarakunan duk da basu biyo wannan tsari nasu ba.
FARA YAKIN JIHADI
Sa'ar da Shehu Usmanu da jama'arsa suka yi hijira, sai Sarkin Gobir Yumfa ya umarci sarakunan garuruwansa da cewar, su kame duk wani mai shirin zuwa ga Shehu Usmanu.
Ai kuwa sai suka shiga fitinar musulmai mabiya Shehu Usmanu da kisa, azabtarwa gami da kwace dukiya.
Da wannan hali ya k'azanta, sai musulman da sukayi hijira suka soma fita yakin jihadi izuwa garuruwa.
Ya zama suna kame kananun garuruwa a hankali har sukazo wani gari waishi Giniga, yaki kuwa yayi tsamari anan.
Ance duk da an halaka musulmai da dama a yakin, wasu manya kuma daga tawagar Shehu sunyi shahada, amma dai saida sukayi nasarar kame garin. Suka kashe na kashewa, wasu kuma aka kame su.
Daga nan suka fita yaki zuwa Matan Kari, nan ma suka ci garin da yaki, suka sake nufar wani gari mai suna Wata Alkarya, shima suka cinyeshi da yaki, sannan suka samu nasarar cinye garin K'wanni da yaki.
A wannan shekara ta farko dai, an gwabza yake-yake masu tsauri, amma cikin ikon Allah duk mutanen shehu ke samun nasara.
Akwai Yakin Kwato da akayi a shekarar, shikuwa yaki ne mafi girma wanda sai dai a Kwatantashi da Yakin Badar a tarihin kafuwar Musulunci, ko kuma yakin Daukar girma a tarihin Yakin Jihadin mutanen shehu Usmanu a Kano.
Sarkin Gobir fa sai hankalinsa ya dugunzuma, ya shiga shirin yaki haikan.
Ya aike da takardu na neman taimako izuwa sarakunan Katsina, Kano, Zazzau, Daura da Azbin, duk kuwa saida suka bashi tallafin daya nema, sannan suma suka ɗaura ɗamarar yaki da duk wani mai alaka da Shehu Usmanu a biranensu.
Daga nan Sarkin Gobir Yumfa ya fita daga garinsa, ya kwana a 'Bore, sannan yahau ya riski Gamba, yabi ta Makida, sannan ya sauka a Tsara ya kwana. Daga nan sai gashi a Janar-Sarki ya kwana biyu anan yana sauraren wasu k'arin dakaru. Bayan sun isone ya fuskanto Gudu da gagarumar runduna.
Koda Shehu da Mabiyansa suka ji Labarin yaki na gabato su, sai suka ɗau harama suma.
Wazirin Shehu, kuma kaninsa, watau Abdullahi, ya taso da rundunar mayaka izuwa gefen wasu gidaje suka sauka suna jira, har yamma tayi basuji komai ba, sai suka koma da baya.
A kwana na biyu ma suka sake yin kamar haka, amma babu abinda ya faru.
Sai a kwana na uku ne wasu 'yan uwansu fulani suka iso garesu a sukwane, suka shaida musu cewar daga cikin rundunar sarki Yumfa suka sato jiki, kuma yaki ya kusa zuwa garesu, tunda kuwa rundunar tana garin Ayame ne, tsakaninsu da garin kuwa tafiyar yini ɗaya ce..
No comments:
Post a Comment