TARIHIN JIHADIN SHEHU USMANU MUJADDADI, DAN FODIO.
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na biyar.
Kashe gari, musulmai suka sake fita jiran Sarkin Gobir da tawagarsa, suka fake tsakanin wasu duwatsu da ake kira Maliba.
Can kuwa babu jimawa sai ga runduna ta iso gagaruma, sarkin Gobir na tsakiya ana buga masa tambari.
Koda rundunonin suka fuskanci juna, sai suka aukawa juna da yaki.
Yaki yayi tsamari, amma sai girgije ya haɗu a sama, aka soma zubda ruwa. Don haka kowa ya koma sansaninsa.
Da ruwa ya tsagaita, sai kowa ya sake dawowa fagen fama, aka sake abkawa faɗa gagarumi.
A wannan rana, mabiya Shehu Usmanu ne sukayi rinjaye, sune kuma harda rarakar magoya bayan Sarkin Gobir Yumfa da gudu.
Mutanen Sarkin Gobir dashi kansa suka sauka acan kusa da tafkin kwatto, Wazirin Shehu Usmanu, Abdullahi ya kwashi jama'a izuwa can, mabiyansa suka sha ruwa a tafkin kwatto sannan suka yi kabbara sau uku, suka afkawa Rundunar gobir da yaki.
Koda rundunar Sarki Yumfa taga haka, sai suma suka suka bugi tamburansu, sannan suka ce dawa aka haɗamu ba daku ba, suka nufarwa mabiya shehu Usmanu da gudu makamai a zare. Kafin kace haka wani sabon yakin ya sake ɓarkewa.
A lokacin kuwa, sai da aka yiwa Mabiya Shehu Usmanu ɗan fodio kawanya, dakaru dama da hagu, an sanya su a tsakiya, gashi kuma yakinsu yafi ga harbi, tunda dawakansu ance basufi ashirin ba. Su kuwa mabiya sarkin gobir dawakansu basa misaltuwa.
Amma dai cikin ikon Allah, sai Allah ya warwatsa rundunar Sarki Yumfa tayi ɗai-ɗai.
Sarkin da kansa yahau ingarman dokinsa ya arce zuwa garinsa, ya bar jama'arsa karkashin takubban mabiya shehu Usmanu, ya bar takalminsa da gadonsa na sarauta, da tamburansa da takobinsa da kayan goro da guzurinsa na alkaki da irinsu.
Wani mawaki yayi baitin waka akan haka da cewa:-
Yayi jifa da takardu dan Sassabtama taguwarsa.
Da guzurinsa, har ma da 'yar sanda tai.
A haka mutanen shehu Usmanu suka rabauta da gagarumar ganima a wannan waje.
A cikin wannan shekara ta ɗaya dayin Hijirar Shehu Usmanu ɗan fodio, akayi yakin Mane.
Sannan a shekarar ne Shehu Usmanu ya ɗauki tawagarsa izuwa Magabci, koda yake wasu sun ruwaito cewar kafin yabar yankin, sai da sukayi kokarin karɓe iko da Alkalawa babban birnin gobir, amma basu samu ikon haka ba, ga kuma yunwa ta damesu, don haka suka bar yankin.
Acan magabci Shehu Usmanu ya rubutawa sarakunan Kasar Hausa takardu yana mai sanar musu dalilinsa na yin yaki da sarkin Gobir, tare da neman haɗin kansu da tallafinsu wajen yaki don tabbatar da musulunci bisa turbar gaskiya da kuma kawar da bidi'o'i.
Sa'ar da Sarkin Katsina ya samu wannan takarda, sai ya keta ta. Yayi magana ta ɓatanci ga shehu da magoya bayansa.
Sa'ar da Sarkin Kano kuma ya samu wannan takarda, sai bai keta taba, amma kuma bai amshi kiran shehu Usmanu ba.
Amma sarkin Zazzau dana Rumo duk sun karɓi kira, sai dai kuma jama'arsu sun bijire a kaiwa shehu tallafi.
Shehu Usmanu ɗan fodio ya baro Magabci izuwa sifawa, sannan ya tashi izuwa Barkiya, sai kuma ya karasa Sokoto.
Daga nan suka nufi Dangeda, suka karasa Godewa duk suna yin yaki tare da samun ganima mai yawa, sannan suka isa Makada, sai kuma suka tashi izuwa Kirare.
A kirare suka haɗu da wasu jama'ar Katsina da sukayi hijira daga katsina izuwa garesu bayan sunsha matsananciyar wahalar tafiya cikin dazuka. Ance a kalla kwanaki talatin suka shafe suna tafiya daga katsina izuwa wannan wuri.
Daga nan kuwa, sai shehu da jama'arsa suka tashi izuwa wani wuri mai suna Tsuntsuwa.
YAKIN TSUNTSUWA
Ance anan tsuntsuwa ne wata rundunar Azbinawa da Gobirawa suka taru suka kawowa mabiya shehu hari, a lokacin kuwa kusan duk sun bar sansani izuwa neman abinci. Waɗanda suka rage kaɗai basu wuce manyan tawagar ba irinsu Shehu Usmanu da kuma wasu dakaru dake tare dasu.
Waziri Abdullahi ya fito da dakarun dake tare dashi suka afkawa wannan tawaga da yaki, shehu Usmanu shi kuma ya fita yana addu'ar neman nasara daga Allah.
Hakika a wannan rana, Allah ya jarrabi Shehu Usmanu da magoya bayansa, domin kuwa akalla dakarunsu dubu biyu ne akace sukayi shahada, kuma sunyi matukar ɓacin rai da haka.
Da yaki ya kare, sai Shehu yaja zuga izuwa Jiruwa, mil biyu ne tsakaninsa da Alkalawa daga gabas.
A wannan waje, mutanen shehu Usmanu suka rinka ribaɗi, watau suna kai hari ga garuruwan dake biyayya da sarkin Gobir jifa-jifa har dai daga baya, Sarkin Gobir ya aiko da runduna aka buga yaki dasu, batare da anci nasara akansu ba.
A wannan shekara dai, Shehu Usmanu da tawagarsa suka shiga zamfara, sukayi yaki da garuruwansu sukaci nasara akansu, wasu garuruwan kuma suka yi mubaya'a ba tare da an gwabza yaki ba.
Daga nan zamfara, sai rundunar Shehu usmanu tayi Daura, sannan suka shiga Tsingaroƴ, suka karasa Mawadaci, sukaƴyi Dumne sannan suka sake komawa zamfara, sai kuma sukayi Maraɗi.
Daga maraɗi sai kuma sukayi Dufuwar Mafara suka sauka, suka ɗanyi kwanaki a wajen, sannan sukayi Sabon Gari nan ma suka zauna suna cin garuruwa.
YAKIN ALWASA
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na biyar.
Kashe gari, musulmai suka sake fita jiran Sarkin Gobir da tawagarsa, suka fake tsakanin wasu duwatsu da ake kira Maliba.
Can kuwa babu jimawa sai ga runduna ta iso gagaruma, sarkin Gobir na tsakiya ana buga masa tambari.
Koda rundunonin suka fuskanci juna, sai suka aukawa juna da yaki.
Yaki yayi tsamari, amma sai girgije ya haɗu a sama, aka soma zubda ruwa. Don haka kowa ya koma sansaninsa.
Da ruwa ya tsagaita, sai kowa ya sake dawowa fagen fama, aka sake abkawa faɗa gagarumi.
A wannan rana, mabiya Shehu Usmanu ne sukayi rinjaye, sune kuma harda rarakar magoya bayan Sarkin Gobir Yumfa da gudu.
Mutanen Sarkin Gobir dashi kansa suka sauka acan kusa da tafkin kwatto, Wazirin Shehu Usmanu, Abdullahi ya kwashi jama'a izuwa can, mabiyansa suka sha ruwa a tafkin kwatto sannan suka yi kabbara sau uku, suka afkawa Rundunar gobir da yaki.
Koda rundunar Sarki Yumfa taga haka, sai suma suka suka bugi tamburansu, sannan suka ce dawa aka haɗamu ba daku ba, suka nufarwa mabiya shehu Usmanu da gudu makamai a zare. Kafin kace haka wani sabon yakin ya sake ɓarkewa.
A lokacin kuwa, sai da aka yiwa Mabiya Shehu Usmanu ɗan fodio kawanya, dakaru dama da hagu, an sanya su a tsakiya, gashi kuma yakinsu yafi ga harbi, tunda dawakansu ance basufi ashirin ba. Su kuwa mabiya sarkin gobir dawakansu basa misaltuwa.
Amma dai cikin ikon Allah, sai Allah ya warwatsa rundunar Sarki Yumfa tayi ɗai-ɗai.
Sarkin da kansa yahau ingarman dokinsa ya arce zuwa garinsa, ya bar jama'arsa karkashin takubban mabiya shehu Usmanu, ya bar takalminsa da gadonsa na sarauta, da tamburansa da takobinsa da kayan goro da guzurinsa na alkaki da irinsu.
Wani mawaki yayi baitin waka akan haka da cewa:-
Yayi jifa da takardu dan Sassabtama taguwarsa.
Da guzurinsa, har ma da 'yar sanda tai.
A haka mutanen shehu Usmanu suka rabauta da gagarumar ganima a wannan waje.
A cikin wannan shekara ta ɗaya dayin Hijirar Shehu Usmanu ɗan fodio, akayi yakin Mane.
Sannan a shekarar ne Shehu Usmanu ya ɗauki tawagarsa izuwa Magabci, koda yake wasu sun ruwaito cewar kafin yabar yankin, sai da sukayi kokarin karɓe iko da Alkalawa babban birnin gobir, amma basu samu ikon haka ba, ga kuma yunwa ta damesu, don haka suka bar yankin.
Acan magabci Shehu Usmanu ya rubutawa sarakunan Kasar Hausa takardu yana mai sanar musu dalilinsa na yin yaki da sarkin Gobir, tare da neman haɗin kansu da tallafinsu wajen yaki don tabbatar da musulunci bisa turbar gaskiya da kuma kawar da bidi'o'i.
Sa'ar da Sarkin Katsina ya samu wannan takarda, sai ya keta ta. Yayi magana ta ɓatanci ga shehu da magoya bayansa.
Sa'ar da Sarkin Kano kuma ya samu wannan takarda, sai bai keta taba, amma kuma bai amshi kiran shehu Usmanu ba.
Amma sarkin Zazzau dana Rumo duk sun karɓi kira, sai dai kuma jama'arsu sun bijire a kaiwa shehu tallafi.
Shehu Usmanu ɗan fodio ya baro Magabci izuwa sifawa, sannan ya tashi izuwa Barkiya, sai kuma ya karasa Sokoto.
Daga nan suka nufi Dangeda, suka karasa Godewa duk suna yin yaki tare da samun ganima mai yawa, sannan suka isa Makada, sai kuma suka tashi izuwa Kirare.
A kirare suka haɗu da wasu jama'ar Katsina da sukayi hijira daga katsina izuwa garesu bayan sunsha matsananciyar wahalar tafiya cikin dazuka. Ance a kalla kwanaki talatin suka shafe suna tafiya daga katsina izuwa wannan wuri.
Daga nan kuwa, sai shehu da jama'arsa suka tashi izuwa wani wuri mai suna Tsuntsuwa.
YAKIN TSUNTSUWA
Ance anan tsuntsuwa ne wata rundunar Azbinawa da Gobirawa suka taru suka kawowa mabiya shehu hari, a lokacin kuwa kusan duk sun bar sansani izuwa neman abinci. Waɗanda suka rage kaɗai basu wuce manyan tawagar ba irinsu Shehu Usmanu da kuma wasu dakaru dake tare dasu.
Waziri Abdullahi ya fito da dakarun dake tare dashi suka afkawa wannan tawaga da yaki, shehu Usmanu shi kuma ya fita yana addu'ar neman nasara daga Allah.
Hakika a wannan rana, Allah ya jarrabi Shehu Usmanu da magoya bayansa, domin kuwa akalla dakarunsu dubu biyu ne akace sukayi shahada, kuma sunyi matukar ɓacin rai da haka.
Da yaki ya kare, sai Shehu yaja zuga izuwa Jiruwa, mil biyu ne tsakaninsa da Alkalawa daga gabas.
A wannan waje, mutanen shehu Usmanu suka rinka ribaɗi, watau suna kai hari ga garuruwan dake biyayya da sarkin Gobir jifa-jifa har dai daga baya, Sarkin Gobir ya aiko da runduna aka buga yaki dasu, batare da anci nasara akansu ba.
A wannan shekara dai, Shehu Usmanu da tawagarsa suka shiga zamfara, sukayi yaki da garuruwansu sukaci nasara akansu, wasu garuruwan kuma suka yi mubaya'a ba tare da an gwabza yaki ba.
Daga nan zamfara, sai rundunar Shehu usmanu tayi Daura, sannan suka shiga Tsingaroƴ, suka karasa Mawadaci, sukaƴyi Dumne sannan suka sake komawa zamfara, sai kuma sukayi Maraɗi.
Daga maraɗi sai kuma sukayi Dufuwar Mafara suka sauka, suka ɗanyi kwanaki a wajen, sannan sukayi Sabon Gari nan ma suka zauna suna cin garuruwa.
YAKIN ALWASA
No comments:
Post a Comment