TARIHIN JIHADIN SHEHU USMANU MUJADDADI, DAN FODIO.
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na uku
HIJIRA DA DALILIN TA
Sa'ar da Sarakuna suka ga jama'ar Shehu Usmanu na tattalin makamai, sai suka fito da k'iyayyarsu a fili garesu.
Suka shiga hanasu yin rawani, suna hana mata lulluɓi.
Da mutanen shehu suka ga haka, sai suka kauracewa garuruwan sarakunan, izuwa wani wuri mai suna Gimbana a Kasar Kabi.
Sarkin Gobir ya aike su komo, sai suka k'i.
Sai kuwa ya aikewa shehu Usmanu Sammacin kira, nufinsa a wannan karon idan yazo ya halaka shi kota halin k'ak'a.
Shehu Usmanu Bn Fodio da k'aninsa Abdullahi, da abokinsa Ummaru Alkammu suka tafi ga fadar sarkin Gobir Yumfa.
Koda Suka shiga gareshi, sai kuwa ya harbesu da bindiga da nufin kone su da wuta, amma maimakon haka, sai wuta ta koma gareshi har ta kusa k'oneshi, ya ruga gida da gudu, sukuwa ko ɗaya cikinsu bai motsa ba.
ƁBayan ɗan lokaci ya dawo garesu, ya zauna tare dasu, sannan yace musu "Ku sani bani da wani makiyi a fili anan duniya kamar ku" Ya bayyana musu kiyayya a fili.
Su kuma suka bayyana masa cewar sam-sam basa tsoronsa. Allah zai karesu daga gareshi. Sannan suka tashi suka tafi gida ba tare da sun sanar da kowa wannan ba.
Shehu yace musu Ku ɓoye wannan abu, muyi addua kada Allah ya kuma haɗa mu da wannan kafiri. Shehu yayi addu'a suka amsa da Amin, sannan suka shafa fatiha suka koma gida.
A lokacin, sai sarkin Gobir ya haɗa runduna ya tafi yak'i da jama'ar Abdussalamu a Kabi, ya kuwa samu nasara akansu, ya kashe na kashewa, ya kama na kamawa, saura kuwa suka warwatse neman mafaka.
Wannan sai ya k'ara masa girman kai da jiji-da-kai, yana ɗagawa shi sarki ne mai cikakken iko da ɗumbin nasara.
Da yake acikin mutanen da aka kama, da yawansu mutanen shehu ne da sukayi hijira, sai mutanen Sarkin Gobir suka taso keyarsu izuwa Gobir, kuma suka biyo dasu ta garinsu shehu Usmani, ta gabas da gidansa ma.
Wannan yasa mutanen shehu suka kamu da tausayin 'yan uwansu, har suka kasa jurewa suka rufarwa dakarun sarkin Gobir tare da kuɓutar da 'yan uwansu.
Da dakarun sarkin Gobir sukaga haka, sai suka runtuma da gudu gaban sarkinsu, suka zaro kibbau daga kwarinsu, sannan suka gabatarwa da sarkin, suna masu cewa "waɗannan kibiyoyin jama'ar shehu ne da suka harbe mu suka k'wace duk binda muka tafi dashi".
Hakan kuwa sai ya fusata Sarkin Gobir Yumfa kwarrai da gaske, yace "Hakika dmsun cimma abinda suka so, amma zasu gani".
Sai kuma ya aikewa shehu Usmanu cewar ya fita dashi da iyalinsa izuwa wani wurin daban, ya rabu da jama'arsa anan.
Shehu Usmanu kuwa yace sam bazaiyi haka ba, sai dai duk abinda zai samu jama'arsa ya samesu baki ɗaya.
Shehu ya aika masa da Cewa "Ni kam bani rabuwa da jama'a ta, amma ina iya rabuwa da garuruwanka, kasar Allah yawa gareta".
Daga nan Sai Shehu ya shiga shirin yin Hijira.
Sarki Yumfa ya sake aiko masa da ɗan aike yana rarrashinsa da kada ya tashi daga inda yake. Amma sai shehu Usmanu yace "Hakika, ni bani fita daga kasarka, amma zan sauka a gefen garuruwanka"
Ai kuwa, sai Shehu Usmanu yayi hijira, yabi ta hanyar Kwarin Gezo, ya shiga ta Demba, yabi ta Kalmalo, ya shiga Farkaji, sannan ya isa Ruwa wuri, sannan ya riski wani rafi da ake kira 'Gudu' dake gefen kasar Gobir ya sauka da hijirarsa anan, a ranar alhamis 12 ga watan zulk'ida, na shekarar 1218 bayan hijirar Ma'aiki Annabi Muhammad tsiran Allah da aminci su tabbata a gareshi.
Koda ya isa wurin, ya tarar Aliyu Jedi tuni ya shirya masa masauki.
Shikuwa Agali, shine ya taho da rakuma ɗauke da littattafan shehu Usmanu...
SADIQ TUKUR GWARZO, RN.
08060869978
Kashi na uku
HIJIRA DA DALILIN TA
Sa'ar da Sarakuna suka ga jama'ar Shehu Usmanu na tattalin makamai, sai suka fito da k'iyayyarsu a fili garesu.
Suka shiga hanasu yin rawani, suna hana mata lulluɓi.
Da mutanen shehu suka ga haka, sai suka kauracewa garuruwan sarakunan, izuwa wani wuri mai suna Gimbana a Kasar Kabi.
Sarkin Gobir ya aike su komo, sai suka k'i.
Sai kuwa ya aikewa shehu Usmanu Sammacin kira, nufinsa a wannan karon idan yazo ya halaka shi kota halin k'ak'a.
Shehu Usmanu Bn Fodio da k'aninsa Abdullahi, da abokinsa Ummaru Alkammu suka tafi ga fadar sarkin Gobir Yumfa.
Koda Suka shiga gareshi, sai kuwa ya harbesu da bindiga da nufin kone su da wuta, amma maimakon haka, sai wuta ta koma gareshi har ta kusa k'oneshi, ya ruga gida da gudu, sukuwa ko ɗaya cikinsu bai motsa ba.
ƁBayan ɗan lokaci ya dawo garesu, ya zauna tare dasu, sannan yace musu "Ku sani bani da wani makiyi a fili anan duniya kamar ku" Ya bayyana musu kiyayya a fili.
Su kuma suka bayyana masa cewar sam-sam basa tsoronsa. Allah zai karesu daga gareshi. Sannan suka tashi suka tafi gida ba tare da sun sanar da kowa wannan ba.
Shehu yace musu Ku ɓoye wannan abu, muyi addua kada Allah ya kuma haɗa mu da wannan kafiri. Shehu yayi addu'a suka amsa da Amin, sannan suka shafa fatiha suka koma gida.
A lokacin, sai sarkin Gobir ya haɗa runduna ya tafi yak'i da jama'ar Abdussalamu a Kabi, ya kuwa samu nasara akansu, ya kashe na kashewa, ya kama na kamawa, saura kuwa suka warwatse neman mafaka.
Wannan sai ya k'ara masa girman kai da jiji-da-kai, yana ɗagawa shi sarki ne mai cikakken iko da ɗumbin nasara.
Da yake acikin mutanen da aka kama, da yawansu mutanen shehu ne da sukayi hijira, sai mutanen Sarkin Gobir suka taso keyarsu izuwa Gobir, kuma suka biyo dasu ta garinsu shehu Usmani, ta gabas da gidansa ma.
Wannan yasa mutanen shehu suka kamu da tausayin 'yan uwansu, har suka kasa jurewa suka rufarwa dakarun sarkin Gobir tare da kuɓutar da 'yan uwansu.
Da dakarun sarkin Gobir sukaga haka, sai suka runtuma da gudu gaban sarkinsu, suka zaro kibbau daga kwarinsu, sannan suka gabatarwa da sarkin, suna masu cewa "waɗannan kibiyoyin jama'ar shehu ne da suka harbe mu suka k'wace duk binda muka tafi dashi".
Hakan kuwa sai ya fusata Sarkin Gobir Yumfa kwarrai da gaske, yace "Hakika dmsun cimma abinda suka so, amma zasu gani".
Sai kuma ya aikewa shehu Usmanu cewar ya fita dashi da iyalinsa izuwa wani wurin daban, ya rabu da jama'arsa anan.
Shehu Usmanu kuwa yace sam bazaiyi haka ba, sai dai duk abinda zai samu jama'arsa ya samesu baki ɗaya.
Shehu ya aika masa da Cewa "Ni kam bani rabuwa da jama'a ta, amma ina iya rabuwa da garuruwanka, kasar Allah yawa gareta".
Daga nan Sai Shehu ya shiga shirin yin Hijira.
Sarki Yumfa ya sake aiko masa da ɗan aike yana rarrashinsa da kada ya tashi daga inda yake. Amma sai shehu Usmanu yace "Hakika, ni bani fita daga kasarka, amma zan sauka a gefen garuruwanka"
Ai kuwa, sai Shehu Usmanu yayi hijira, yabi ta hanyar Kwarin Gezo, ya shiga ta Demba, yabi ta Kalmalo, ya shiga Farkaji, sannan ya isa Ruwa wuri, sannan ya riski wani rafi da ake kira 'Gudu' dake gefen kasar Gobir ya sauka da hijirarsa anan, a ranar alhamis 12 ga watan zulk'ida, na shekarar 1218 bayan hijirar Ma'aiki Annabi Muhammad tsiran Allah da aminci su tabbata a gareshi.
Koda ya isa wurin, ya tarar Aliyu Jedi tuni ya shirya masa masauki.
Shikuwa Agali, shine ya taho da rakuma ɗauke da littattafan shehu Usmanu...
No comments:
Post a Comment