MALLAM AMINU KANO
Sadiq Tukir Gwarzo, RN.
An haifi marigayi jajirtaccen ɗan siyasa Mallam Aminu Kano a birnin kano,a shekarar 1920.
Mahaifinsa Mallam Yuduf, muhuti ne a kotun Alkali dake kano.
Mallam Aminu kano yayi elementare da midil ɗinsa duk a Kano, sannan ya samu gurbin karatu a kwalejin katsina, yayin da bayan gamawar karatunsa ya soma aikin koyarwa, har kuma lokacin da gwamnati ta baiwa wasu malaman makaranta a Nigeria gurbin karatu izuwa Ingila, ciki kuwa har dashi kansa.
A wannan tafiya karo karatu zuwa ingila ne suka soma haɗuwa tare da abokantaka da Sir Abubakar Tafawa Balewa, sannan bayan dawowarsa gida Nigeria ya soma karantarwa a kwalejin Bauchi, inda anan ake ganin alaka ta haɗu tsakaninsa da Marigayi Mallam Sa'adu Zungur.
Daga nan fa sai Mallam Aminu kano ya shiga rubuce-rubuce da wayar dakai dangane da karɓar yanci daga turawan mulkin mallaka da kuma sarakuna.
Ance ya zama sakataren kungiyar malamai da Tafawa Balewa ya kafa kuma yake jagoranta mai suna 'Bauchi Discussion circle'.
Ashekarar 1948, mallam Aminu Kano ya zamo shugaban Makarantar horas da malamai ta Maru dake sokoto, haka kuma ya zamo sakataren kungiyar malamai ta Arewacin Nigeria.
A wancan lokaci, yayi kokarin ɗaukaka darajar makarantun Allo na arewa don karantar da Alkurani ga Dalibai.
Haka kuma yana sokoto, ya shiga kungiyar siyasa ta Jamiyyar Mutanen Arewa, wadda daga baya ta sauya izuwa NPC.
A shekarar 1950, mallam Aminu kano ya jagoranci wasu jama'a suka sauya sheka daga Jamiyyar Mutanen Arewa izuwa kafa sabuwar jamiyyar siyasa mai suna
Northern Elements Progressive Union (NEPU).
Wannan jam'iyya ta Mallam Aminu kano, tana kunshe da malamai da sauran mutane masu ra'ayin kawo sauyi a Arewa, irinsu Magaji Dambatta, Abba Maikwaru da Bello Ijumu.
A zaɓen shekarar 1951, jamiyyar NEPU ta mallam Aminu kano ta tsaya takara a kano, kuma ta samu gagarumar nasara.
A shekara ta 1954, mallam Aminu kano ya tsaya takarar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano amma baiyi nasara ba, inda Marigayi Maitama Sule Dan masanin kano ya kayar dashi zaɓe.
Amma a Zaɓen shekara ta 1959, mallam Aminu kano ya sake yin takara kuma yaci, inda ya zamo ɗan majalisar kasa mai wakiltar gabashin kano, har kuma a majalisar ya samu mukamin mataimakin bulaliyar majalisa, a lokacin jamiyyar Nepu da NCNC sun samar da haɗin kai ga juna.
Bayan anyi juyin mulkin shekarar 1966, mallam Aminu kano ya cigaba da koyarwarsa da kuma gwagwarmaya kamar yadda ya saba, kuma bai sake rike mukamin gwamnati ba har sai da aka karɓe iko da gwamnatin Aguiy Ironsi, Janar Yakubu Gowon ya zama shugaban kasa da kakin soja, gabannin soma yakin Basasa kenan, sai aka naɗa Malla Aminu Kano kwamishinan Lafiya.
Daga nan kuma ba'a sake sahale damar yin jam'iyyun siyasa ba sai bayan shekaru 12, inda gwamnatin Soja ta bada damar kafa jamiyyu a shekar 1978, anan ne Mallam Aminu Kano da Sam Ikoku, da Edward Ikem Okeke suka kafa jamiyar 'People Redemtion Party' PRP.
A shekara ta 1979, jamiyyar PRP ta tsayar da Mallam Aminu Kano takarar shugaban kasa amma baiyi nasara ba, sai dai jamiyyar ta tsira da kujerar gwamnoni biyu.
Tun a zamanin Jamhuriya ta farko, Mallam Aminu kano a matsayinsa na jagoran NEPU, shine ya jajirce wajen yaki da takurar Sarakuna ga talakawa. Domin kuwa ada, kowanne talaka sai ya biya haraji nasa, dana 'ya'yansa maza, da kuɗin kan ɗaki, da kuɗin sana'ar duk da yake yi, sannan kuma duk da cewa an daina cinikin bayi, amma akwai duddugen bautar da talakawa a lokacin daga sarakuna.
Saboda haka, Mallam Aminu kano da gudunmuwar du Tafawa Balewa da Saadu Zungur da wasunsu, ya shiga ya fita har aka hana sarakuna yin waɗannan aikace-aikace duk kuwa da irin tsana da tsangwama da mabiyansa yan Nepu suka sha.
Hakika ba za'a taɓa mancewa da mallam Aminu kano ba matsawar ana batun baiwa mata 'yanci, da hana sarakunan mulki nuna karfi ga talakawansu da kuma kawar da bambancin kabilu tsakanin 'yan Arewa dama mutanen Nigeria baki ɗaya.
Mallam Aminu kano shine ya tsaya kai da fata don ganin Jihar kwara ta faɗo yankin Arewa, bisa yadda ya gamsar da alumma cewar tarihin asalin tafkin kwara na Arewa ne duba daular da Shehu Usmanu ɗan fodio ya kafa wadda ta tsallaka har tafkin kwara.
Daga nan kuma ya hori mabiyansa su zamo masu taskance tarihi don gudun asara a ragowar rayuwarsu, kamar yadda aka jiyo shi yana cewa
"Matukar ba muyi tarihi ba
Matukar bamu rubuta tarihi ba,
Matukar bamu zakulo mutanen mu na baya da sukayi aiki nagari ba,
Zamu kasance muna lika Lambar LENIN data MAOTETUNG".
(Lenin shugaban rasha ne na lokacin, Mao kuma shugaban China. Don haka Mallam Aminu kano na nufin idan har mutum bai kiyaye tarihin ingantattun mutane acikin al'ummar saba, da sannu zai zamo yana kaunar shugabannin wasu al'ummar daba tasa ba).
Allahu Akbar, akarshe Allah ya karɓi rayuwar Mallam Aminu kano ranar 17 ga watan afrilun shekara ta 1983, sa'ar da ake tsaka da kaunarsa. Kuma mabiyansa sun haɗu daga gsruruwa a kano, sunyi tattaki ɗauke da jan kyalle, don numa alhinimsu ga wannan rashi.
Da fatan Allah yajikansa Amin.
Sadiq Tukir Gwarzo, RN.
An haifi marigayi jajirtaccen ɗan siyasa Mallam Aminu Kano a birnin kano,a shekarar 1920.
Mahaifinsa Mallam Yuduf, muhuti ne a kotun Alkali dake kano.
Mallam Aminu kano yayi elementare da midil ɗinsa duk a Kano, sannan ya samu gurbin karatu a kwalejin katsina, yayin da bayan gamawar karatunsa ya soma aikin koyarwa, har kuma lokacin da gwamnati ta baiwa wasu malaman makaranta a Nigeria gurbin karatu izuwa Ingila, ciki kuwa har dashi kansa.
A wannan tafiya karo karatu zuwa ingila ne suka soma haɗuwa tare da abokantaka da Sir Abubakar Tafawa Balewa, sannan bayan dawowarsa gida Nigeria ya soma karantarwa a kwalejin Bauchi, inda anan ake ganin alaka ta haɗu tsakaninsa da Marigayi Mallam Sa'adu Zungur.
Daga nan fa sai Mallam Aminu kano ya shiga rubuce-rubuce da wayar dakai dangane da karɓar yanci daga turawan mulkin mallaka da kuma sarakuna.
Ance ya zama sakataren kungiyar malamai da Tafawa Balewa ya kafa kuma yake jagoranta mai suna 'Bauchi Discussion circle'.
Ashekarar 1948, mallam Aminu Kano ya zamo shugaban Makarantar horas da malamai ta Maru dake sokoto, haka kuma ya zamo sakataren kungiyar malamai ta Arewacin Nigeria.
A wancan lokaci, yayi kokarin ɗaukaka darajar makarantun Allo na arewa don karantar da Alkurani ga Dalibai.
Haka kuma yana sokoto, ya shiga kungiyar siyasa ta Jamiyyar Mutanen Arewa, wadda daga baya ta sauya izuwa NPC.
A shekarar 1950, mallam Aminu kano ya jagoranci wasu jama'a suka sauya sheka daga Jamiyyar Mutanen Arewa izuwa kafa sabuwar jamiyyar siyasa mai suna
Northern Elements Progressive Union (NEPU).
Wannan jam'iyya ta Mallam Aminu kano, tana kunshe da malamai da sauran mutane masu ra'ayin kawo sauyi a Arewa, irinsu Magaji Dambatta, Abba Maikwaru da Bello Ijumu.
A zaɓen shekarar 1951, jamiyyar NEPU ta mallam Aminu kano ta tsaya takara a kano, kuma ta samu gagarumar nasara.
A shekara ta 1954, mallam Aminu kano ya tsaya takarar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano amma baiyi nasara ba, inda Marigayi Maitama Sule Dan masanin kano ya kayar dashi zaɓe.
Amma a Zaɓen shekara ta 1959, mallam Aminu kano ya sake yin takara kuma yaci, inda ya zamo ɗan majalisar kasa mai wakiltar gabashin kano, har kuma a majalisar ya samu mukamin mataimakin bulaliyar majalisa, a lokacin jamiyyar Nepu da NCNC sun samar da haɗin kai ga juna.
Bayan anyi juyin mulkin shekarar 1966, mallam Aminu kano ya cigaba da koyarwarsa da kuma gwagwarmaya kamar yadda ya saba, kuma bai sake rike mukamin gwamnati ba har sai da aka karɓe iko da gwamnatin Aguiy Ironsi, Janar Yakubu Gowon ya zama shugaban kasa da kakin soja, gabannin soma yakin Basasa kenan, sai aka naɗa Malla Aminu Kano kwamishinan Lafiya.
Daga nan kuma ba'a sake sahale damar yin jam'iyyun siyasa ba sai bayan shekaru 12, inda gwamnatin Soja ta bada damar kafa jamiyyu a shekar 1978, anan ne Mallam Aminu Kano da Sam Ikoku, da Edward Ikem Okeke suka kafa jamiyar 'People Redemtion Party' PRP.
A shekara ta 1979, jamiyyar PRP ta tsayar da Mallam Aminu Kano takarar shugaban kasa amma baiyi nasara ba, sai dai jamiyyar ta tsira da kujerar gwamnoni biyu.
Tun a zamanin Jamhuriya ta farko, Mallam Aminu kano a matsayinsa na jagoran NEPU, shine ya jajirce wajen yaki da takurar Sarakuna ga talakawa. Domin kuwa ada, kowanne talaka sai ya biya haraji nasa, dana 'ya'yansa maza, da kuɗin kan ɗaki, da kuɗin sana'ar duk da yake yi, sannan kuma duk da cewa an daina cinikin bayi, amma akwai duddugen bautar da talakawa a lokacin daga sarakuna.
Saboda haka, Mallam Aminu kano da gudunmuwar du Tafawa Balewa da Saadu Zungur da wasunsu, ya shiga ya fita har aka hana sarakuna yin waɗannan aikace-aikace duk kuwa da irin tsana da tsangwama da mabiyansa yan Nepu suka sha.
Hakika ba za'a taɓa mancewa da mallam Aminu kano ba matsawar ana batun baiwa mata 'yanci, da hana sarakunan mulki nuna karfi ga talakawansu da kuma kawar da bambancin kabilu tsakanin 'yan Arewa dama mutanen Nigeria baki ɗaya.
Mallam Aminu kano shine ya tsaya kai da fata don ganin Jihar kwara ta faɗo yankin Arewa, bisa yadda ya gamsar da alumma cewar tarihin asalin tafkin kwara na Arewa ne duba daular da Shehu Usmanu ɗan fodio ya kafa wadda ta tsallaka har tafkin kwara.
Daga nan kuma ya hori mabiyansa su zamo masu taskance tarihi don gudun asara a ragowar rayuwarsu, kamar yadda aka jiyo shi yana cewa
"Matukar ba muyi tarihi ba
Matukar bamu rubuta tarihi ba,
Matukar bamu zakulo mutanen mu na baya da sukayi aiki nagari ba,
Zamu kasance muna lika Lambar LENIN data MAOTETUNG".
(Lenin shugaban rasha ne na lokacin, Mao kuma shugaban China. Don haka Mallam Aminu kano na nufin idan har mutum bai kiyaye tarihin ingantattun mutane acikin al'ummar saba, da sannu zai zamo yana kaunar shugabannin wasu al'ummar daba tasa ba).
Allahu Akbar, akarshe Allah ya karɓi rayuwar Mallam Aminu kano ranar 17 ga watan afrilun shekara ta 1983, sa'ar da ake tsaka da kaunarsa. Kuma mabiyansa sun haɗu daga gsruruwa a kano, sunyi tattaki ɗauke da jan kyalle, don numa alhinimsu ga wannan rashi.
Da fatan Allah yajikansa Amin.
No comments:
Post a Comment