1. Mai Idris Alooma
Sarkin Borno Mai Idris Alooma shahararren sarki ne wanda sunan sa bazai shafuba a tarihin sarakunan duniya ballantana wannan yanki na Arewa.
Ance ko dai yayi mulki tsakanin shakara ta 1571-1603 ko 1580-1616, ko kuma wasu shekaru kusa da haka.
Haka kuma, ana cewar shine sarkin Borno na 15, yayi yakuna sama da guda dubu ɗaya a tsawon rayuwar sa ta mulki, a ciki ya samu nasara a yakuna 330 kamar yadda tarihin wasu yakunan yazo a littafin 'Gazwatu Borno' na marubucin sarkin mai suna Ahmad Al Furtu.
Mai Idris Shine wanda ya soma samarwa da dakarunsa hulunan sulke na bakin karfe domin yin yaki kamar yadda manyan masarautu irinsu misira da girka suka daɗe dayi.
Haka kuma, ya horas da dakarunsa da dabaru kala kala, domin kuwa ya ware dakaru masu kai farmaki a jirgir ruwa, ya ware dakaru masu kai harin sari-ka-noke, sannan ya ware rundunar dakaru 'yan lifida.
Ance a lokacin mulkinsane aka turo wakilai ɗari biyu daga masarautar Ottoman ta Turkiya izuwa babban birnin Borno da yake a Ngazargamu a wancan lokaci domin kulla alaka tsakanin masarautun biyu.
Haka kuma kasancewar sa musulmi, babban abinda yayiwa daular Borno a musulunce shine masallatai daya gina domin haɓaka ibada da kuma koyar da addini.
Sannan Hakika, Mai Idris Alooma ya haɓaka tattalin arzikin daular borno, ya haɓaka kasuwanci, tunda ance har kasashen larabawa ake turawa da goro, siliki, da auduga da sauran kayayyaki daga masarautar borno.
Sannan ya samar da tsaro, yayi yaki domin faɗaɗa masarautarsa, kuma hakika ya samu nasara gagaruma a zamaninsa.
A zamanin mulkinsa, daular Borno ta faɗaɗa har izuwa Fezzan ta kasar Libya daga Arewa, sannan ta shigo kasar Hausa daga Yamma, hakanan yacinye kabilun Bulala da wasu masarautu a Gabas.
A karshe, ance ya rasu a wurin yaki bayan anyi masa jina-jina a gefen wani tafki mai suna Alao. Acan kuma akace an binneshi, don haka ake tsammanin Alooma ya samo asali ne daga inda kabarinsa yake.
No comments:
Post a Comment