7. SIR. ABUBAKAR TAFAWA BALEWA
Daga Sadiq Tukur Gwarzo, RN.
An haifi marigayi firimiyan ƁNigeria na farko watau Abubakar Tafawa Balewa a garin Tafawa Balewa na Bauchi, a shekarar 1912.
Mahaifinsa Yakubu ɗan Zala ya fito me daga kabilar Bagire, kuma shine dagacin Lere.
Tafawa Balewa ya soma karatun alkur'ani dana boko a Bauchi, koda yake ance yaje katsina karatu, daga bisani ya samu gurbin karatu a Kwalejin Barewa ta zaria, yana kammalawa kuwa aka bashi shaidar malinta inda ya dawo Makarantar Midil ta Bauchi ya soma koyarwa.
Tafawa Balewa ya samu gurbin tafiya Ingila karo karatu tare dasu Mallam Aminu kano, inda ya samo shaidar Malanta na koyar da Tarihi acan, sannan ya dawo gida.
Da dawowarsa kuwa sai ya zamo wakilin turawan mulki masu kula da makarantu, alokacin kuma an ruwaito yana cewa ya gano yadda rayuwa take tafiya a turai cikin 'yanci da walwala, kuma ya haɗu da mutane masu bin doka ba tare da tsoron komai ba, don haka yana kallon Nigeria da wani yanayi na daban.
A lokacin ne ya soma kafa kungiyar malamai ta Bauchi, inda suke tattauna hanyoyin samar da cigaba, daga bisani kuma ya tsaya takara kuma yaci zaɓen ɗan majalisar wakilai na Arewa a shekarar 1946.
A majalisar Arewa suka haɗu da Ahmadu Bello har kuma suka kafa jamiyyar 'Northern People's Congres' watau NPC.
A shekarar 1952 tafawa Balewa ya zama ministan aiyuka, daga baya kuma ministan sufuri.
A shekarar 1957 aka naɗa shi babban minista, sannan kuma bisa haɗin guiwar jamiyyarsa ta NPC da jam'iyyar Nnamdi Azikwe, Tafawa Balewa ya zamo Firimiyan Nigeria na farko bayan karɓar 'yancin kai a shekarar 1960. Kuma ya sake tsayawa takara a shekarar 1964 ya lashe zaɓe.
Ana yiwa Tafawa Balewa lakabi da 'Golden Voice', saboda nasibinsa wurin iya zance da gamsar da mutane. Kuma a wancan lokacin, ya zamo fuskar Afirka, domin yayi aiki tukuru wajen haɗa alaka tsakanin Nigeria da kasashen Afirka, da kuma warware matsaloli tsakanin Kasashen Afirka. Sannan ya cusa 'yan Arewa da dama acikin kunshin mukaman Gwamnatin tarayya.
Akarshe, lokacin Juyin mulkin 17 ga watan janairu na shekarar 1966, ance wasu sojoji su biyar sun kutsa kai gidan sa inda suka sace shi.. Daga baya kuma aka tsinci gawar sa.
Da fatan Allah yajiqansa Amin.
Daga Sadiq Tukur Gwarzo, RN.
An haifi marigayi firimiyan ƁNigeria na farko watau Abubakar Tafawa Balewa a garin Tafawa Balewa na Bauchi, a shekarar 1912.
Mahaifinsa Yakubu ɗan Zala ya fito me daga kabilar Bagire, kuma shine dagacin Lere.
Tafawa Balewa ya soma karatun alkur'ani dana boko a Bauchi, koda yake ance yaje katsina karatu, daga bisani ya samu gurbin karatu a Kwalejin Barewa ta zaria, yana kammalawa kuwa aka bashi shaidar malinta inda ya dawo Makarantar Midil ta Bauchi ya soma koyarwa.
Tafawa Balewa ya samu gurbin tafiya Ingila karo karatu tare dasu Mallam Aminu kano, inda ya samo shaidar Malanta na koyar da Tarihi acan, sannan ya dawo gida.
Da dawowarsa kuwa sai ya zamo wakilin turawan mulki masu kula da makarantu, alokacin kuma an ruwaito yana cewa ya gano yadda rayuwa take tafiya a turai cikin 'yanci da walwala, kuma ya haɗu da mutane masu bin doka ba tare da tsoron komai ba, don haka yana kallon Nigeria da wani yanayi na daban.
A lokacin ne ya soma kafa kungiyar malamai ta Bauchi, inda suke tattauna hanyoyin samar da cigaba, daga bisani kuma ya tsaya takara kuma yaci zaɓen ɗan majalisar wakilai na Arewa a shekarar 1946.
A majalisar Arewa suka haɗu da Ahmadu Bello har kuma suka kafa jamiyyar 'Northern People's Congres' watau NPC.
A shekarar 1952 tafawa Balewa ya zama ministan aiyuka, daga baya kuma ministan sufuri.
A shekarar 1957 aka naɗa shi babban minista, sannan kuma bisa haɗin guiwar jamiyyarsa ta NPC da jam'iyyar Nnamdi Azikwe, Tafawa Balewa ya zamo Firimiyan Nigeria na farko bayan karɓar 'yancin kai a shekarar 1960. Kuma ya sake tsayawa takara a shekarar 1964 ya lashe zaɓe.
Ana yiwa Tafawa Balewa lakabi da 'Golden Voice', saboda nasibinsa wurin iya zance da gamsar da mutane. Kuma a wancan lokacin, ya zamo fuskar Afirka, domin yayi aiki tukuru wajen haɗa alaka tsakanin Nigeria da kasashen Afirka, da kuma warware matsaloli tsakanin Kasashen Afirka. Sannan ya cusa 'yan Arewa da dama acikin kunshin mukaman Gwamnatin tarayya.
Akarshe, lokacin Juyin mulkin 17 ga watan janairu na shekarar 1966, ance wasu sojoji su biyar sun kutsa kai gidan sa inda suka sace shi.. Daga baya kuma aka tsinci gawar sa.
Da fatan Allah yajiqansa Amin.
No comments:
Post a Comment