GASKIYA DACI GARETA
Shiri na daya (1).
LABARIN SARKI SIBANA DA GIMBIYARSA SULBANIYA
Tare da Sadiq Tukur Gwarzo
08060869978
Ance Sarki sibana wani shahararren sarki ne kuma qasaitacce daga cikin rukunin sarakunan da suka mulki Birnin Andaluz, dadaddiyar masarautar da a wani zamani can daya gabata mulkinta ya kusan game ko ina a sassan duniya.
Shidai wannan sarki, tarihi ya nuna asalinsa baiyi gadon sarauta ba, ba kuma wani Kakkarfan jarumi bane, wannan ne babban abin mamaki alokacin jahiliyya har ace wani wanda bai hada wadancan biyun ba ya zamo sarki, alhali lokacin rayuwa ce kwatankwacin ta dabbobi, mai qarfi shine a sama, sarauta da shugabanci ko wanne iri ne gida ko ace zuriya yake bi, wato idan akace wane shine shugaba kaza, tofa shekaru aru-aru masu zuwa zaka samu cewar zuriyarsa ce ke riqe wannan kambun.
Sibana dai kafin zamowarsa Sarki, ance masani ne amma fa matalauci naqin qarawa tun alokacin da sani bai wadata ba kuma arziki bai zamo ruwan dare ba, masanin dalasumai ne; wasu kalmomi da ake ta'allaqa su da wasu halittu wadanda ido baya iya gani, masanin hukunci ne, mai kamanta adalci ne, kuma gwanin tsara magana ne. Sannan kuma an haqqaqe cewar yana cikin sahun wasu mutane da akewa kallon gida-dawa a wancan lokacin, wadanda suke neman buqatunsu a wurin Allah. Idan zasuyi alqawari, bada shaida ko tawassali don samun wata buqata, sunayi ne da Allah wanda sukayi imanin al'arshinsa yana sama, duk da cewa a lokacin akwai qarancin ilimin wanene Allah.
Wata rana sibana yayi mafarki ana masa magana da wata sassanyar murya, ana cewa "ya kai wannan mutum, haqiqa Allah yayi maka baiwar ilimi da hikima, abinda tsiraru acikin bayinsa ne suke dashi. Allah ya fifita taka fiye da yawa-yawan mutanen wannan alqarya. Don haka lokaci ya gabato wanda Allah zai daukaka ka da ilimin ka, ba bisa ga abinda kayi gado ba, ba kuma bisa ga wata bajinta da kayiwa al'umma ba, sannan zai qasqantar da jahilai bisa ga abinda suka dade suna aikatawa na munanci ga Allah.
Ya kai wannan mutum, kayi shiga irin ta qasqantattun mutane kanufi Fada gobe, kasanar da sarki cewar zaka bashi amsar tambayar sa, zaka sanar dashi aikin da Allah yake aiwatarwa da hannunsa tare da qwararan hujjoji matsawar ya yarda da sharadin zai baka kayansa na sarauta, zai sanya naka, zaka hau kan karagarsa kuma dole kowa yayi maka biyayya sannan zaka fadi amsar.
Ya kai wannan mutum, kayi sani cewa daga nan mulki ya dawo gareka. Ka sanar da mutane hukuncin Allah da ikonsa wajen daukaka qasqantacce da qasqantar da daukakakke yafi ga haka, kayi mulki kuma da gaskiya da adalci. Haqiqa zaka dauwama acikib mulki, zaka samu duk cikar burikanka matsawar baka fara gaggawar yanke hukunci acikin lamurorin kaba, sannan matsawar fushi bai zamo yana tunkudaka aikata munanan aiyuka ba.." Yana zuwa nan ne ya farga afujajan.
Farkawar sa keda wuya ya samu kansa yana maimaita maganganun da aka sanar dashi. Babu abinda ya mance kai kace gar-da-gar aka sanar dashi wadannan zantuka. Tunani ya mamaye shi, ya rasa abinyi. Anan ne ma yake fahimtar ashe gari ya waye, rana ta take.
Yana cikin wannan hali ne kuma ya jiyo San kira yana shela a gari yana cewa "yaku mutanen wannan alqarya, Sarki Alkandaruz yana sanya muku albarka, yace asanar daku, bai daukewa kowa ba halartar taron daurin aurensa gobe a fada da gimbiya Sulbaniya ba, sannan yace asanar daku ya tanaji babban muqami da tarin dukiya ga duk wanda yazo masa da amsar da daddiyar tambayarsa gagara amso. Abinda kawai akeso shine, kafadi aikin da Allah yake aikatawa da hannunsa, ka kuma kawo hujjoji qwarara tare da inda ka same su."
Wannan abu ya qara dagawa sibana hankali, wato dai lamarin mafarkin sa akwai wani sirri acikinsa. Sai dai abin da ke bashi tsoro shine tayaya zai iya gaskata mafarkin? Idan dai sibana bai manta ba, a shekarar data gabata, sarki ya hallaka kimanin mutane talatin wadanda suka zo da zummar amsa wannan hatsabibiyar tambaya tashi. Daman shardin tambayar kenan, duk wanda baiciba, ajalinsa yazo kenan. Idan mutum yazo da amsa, sarki zai amsa, sai kuma yace kawo hujjoji da kuma inda kasamo wannan amsa. Tofa ana ake yinta. Saboda mafiyawan mutane shaci fadi kurum sukeyi, tunda alokacin kan mutane bai waye da ilimin saukakkun littattafai ba, Allah dinma da yawa wai-wai dinsa kurum akeji.
( #Sadiq Tukur Gwarzo)
A zahiri, Sibana baiyi niyyar tunkarar Sarki Andaruz da wannan kasada ba. Sarki Andaruz fa jarumin gaske ne, yana da girman jiki, da kwarjini, gashi da qarfin fada aji. Sarakuna ma shakkar sa yake ji, don haka duk abinda yake so ko basa so, ala tilas akeyi masa. Amma kasancewar tunanika da qunci sun yiwa Sibana yawa, sai ya tsinci kansa yana mai cire son rayuwar duniya a ransa, yayi niyyar magance quncin dake ransa ta hanyar kai kansa ga halaka, wataqila zai samu sukuni idan aka hallakashi. Mafitar daya daukarwa kansa itace, zaibi umarnin da aka bashi a mafarki, in yaso sarki ya kashe shi ya huta da zullumi gami da quncin rayuwar daya ke fama dashi.
Kamar yadda aka buqata kuwa, fadar Sarki Alkandaruz tayi cikar kwari. Daman qasaitacciyar fada ce mai cike da gine-gine dogaye. Sarki yana can saman wata husumiya akan karagarsa. A qasan sa kuma manyan waziransa ne da wasu sarakuna wadanda aka gayyato domin shaida daurin auren Sarki da Gimbiya. Kasancewar Sarki yana matuqar qaunar gimbiya sulbaniya yasanya shi cikin annushuwa a wannan rana da zai aureta. Dariya kawai yakeyi, kyauta yakeyiwa bayi sai kace ruwan sama, gashi can akaraga yasha fararen tufafi masu tsada masu dauke da ado na jan jauhari da lu'u-lu'u.
(#Sadiq Tukur Gwarzo)
Kamar yadda aka tsara, za'ayi shela ne har sau uku. Idan an samu wanda yazo ya baiwa sarki amsar tambayarsa, to sai a gabatar dashi a gaban sarki. Idan kuwa ba'a samu ba, shikenan sai a daura auren sarki da gimbiya daga nan kuma ashiga sahun shagulgulan biki. Don haka mai shela ya fara shela. Yayi kira da murya kakkarfa, yayi kirari ga sarki, ya yabi gimbiya, sannan ya nemi duk wanda yazo da amsar tambaya ya matso, yana mai koda kyaututtukan da sarki yayiwa duk wanda ya dace tanaji.. Sarki zai baka babban wazirinsa, zai baka damar tattara harajin duk masarautun dake qarqashin ikon sa, zai aura masa aure da mata dari, zai bashi katafaren gida.. Dadai sauransu.
Mai shela ya qara yin shela akaro na biyu, amma wurin nan tsit kakeji. Talakawa duk sun shiga taitayinsu, kunsan ance wargi wuri yaka samu. Qwaqqwaran motsi ma bakaji, kai kace cewa akayi duk wanda ya motsa abakacin rayuwarsa ne. A karo na uku ma mai shela ya qara yin shela wanda bai rufe baki ba sai ga Sibana kwaram-kwaram yana sanye da tufafi yagaggu, ga kayan hauka nan rakwacan sanye ajikin sa. Ya nufi husumiyar Sarki kai tsaye, kwachachaf-kwachachaf kawai kaceji kai kace shine maigirma Sarkin mahaukata na duk duniya.
Dakarun sarki sukayi kansa asukwane saboda ko ina sune dauke da takubba gayawa jini na wuce, wasu kuma riqe da kibau, harda masu majaujawa. Suka sha gabansa, babban su ya daka masa tsawa yace kai mahaukaci, a fadar Sarkin sarakuna kake ka natsu. Sibana ya daga kansa yana mai dubansa ba tare da tsoro a tare dashi ba yace "Ni ba mahaukaci bane, kuma amsa nazo nabaiwa sarki. Kayi sani cewa Karshen tababa da zubda jinin jahilai yazo, kuma lokacin da gaskiya zatayi halinta ya tabbata. Don haka ka sanar da Sarki cewa duk abinda yakeso ya sani lokacin sa yazo, zan bashi amsa ba kuma naneman abiya da da wata kyauta amma fa sai idan har zai iya cika sharuddai na guda uku dazan ambata".
Sarki ya qyaqyace da dariya, ya buga qafa qasa cikin annushuwa da qeta da yaji abinda wannan mahaukaci yazo dashi. Yace "ku matso dashi gabana, yazo ya fadi wadannan sharudda, mu kuma munyi alqawarin zamu cika su. Amma fa idan har ya kasa bada amsa, to da sannu zansa ayi gunduwa-gunduwa da sassan jikinsa". Sibana ya tsaya a gaban Sarki bayan dakaru sun gabatar dashi, sannan ya fara magana da cewa "ya kai Maigirma sarki wanda sarautarsa ta fadada, ikonsa ya shiga duniya, kai ne sarki mafi qarfin iko a duniya. Kasani cewa bana neman wata kyauta abisa amsar tambayarka dazan bayar. Sharudda kurum nakeso kacika. Na farko, zamuyi musanyen kaya dani-dakai. Na biyu zaka dawo nan inda nake, nikuma zan zauna a inda kake. Na uku kuma dakarunka zasuyi biyayya agareni. Idan har ka amince, to ina maka albishir da samun cikakkiyar biyan buqatarka agareni"
(#Sadiq Tukur Gwarzo)
Ko kadan Sarki bai dauki wadannan sharudda abisa wasu abubuwa masu sharadi ba, don haka nan take ya amince. Abinda yake hangowa kawai shine zai taya bera bari ne, wato zai qure qaryar wannan mahaukaci inyaso sai ya gallaza maza da azaba mafi muni, tayadda al'ummarsa zata qara jin tsoronsa. Da yake kuma Sarki ne wanda yake sa gabansa aduk inda yakeso, sai ya kasance babu daga cikin wazirinsa wanda yace maza kanzil akan cika wadannan sharudda.
Sibana ya zauna akan karagar sarki. A halin yanzu shine Sarki, domin kuwa duk dakarun sarki umarninsa suke jira ba umarnin Sarki Ankaldaruz ba. Sibana ya dubi taron jama'a yace "yaku jama'ar Andaluz dame nayi kama yanzu??? Mutane suka dauka gaba daya da cewa "da sarkiiiii". Ya qara cewa "wannan fa damai yayi kama?" Yana mai nuni da sarki Alkandaruz? Mutane suka qara cewa "da mahaukaci". Sai ya kalli Sarki Alkandaruz yace " wannan shine aikin da Allah mai iko ya aiwatar da hannunsa yanzu-yanzu. Sarki ya zamo mahaukaci, mahaukaci ya zamo Sabon Sarki." (#Sadiq Tukur Gwarzo)
Sarki Alkandaruz yayi tsaki, ransa ya baci saboda abin kamar yazo masa da qasqanci. Sannan ya dubi Sibana yace "to yi sauri ka cire kayannan ka dawo nan, wadannan kayan sun. Isheni da tsami. Sannan kuma idan ka kasa bani hujjar maganar ka da inda ka samo amsar na rantse sai na lahira ya fika jin dadi". Da fadin haka sai yayi kan karagar da nufin ya hankade sibana da qarfin tsiya. Ai kuwa nan take sibana ya dakawa dakaru tsawa, yace ku kama shi kuyi maza ku kai mini shi kurkuku. Ai duk wanda yake son zurfafa bincike acikin lamarin Allah hauka da qasqanci ne makomar sa" Aikuwa ala dole, suka amshi umarnin sabon sarki, tsohon sarki tun yana ashariya, har ya dawo yana magiya, amma ina, bakin alqalami ya bushe. Anan take ya fara fahimtar kuskurensa. (#Sadiq Tukur Gwarzo)
Sabon Sarki yayi jawabi mai ratsa jiki ga al'umma, yayi musu nasiha da gaskiya, adalci gami da zama lafiya. Daga nan kuma aka dauka aurensu da gimbiya Sulbaniya..
Wannan shine matashiyar wannan labari..
Darussan dake shirin GASKIYA DACI GARETA na wannan lokaci sune;
*Ya kamata mutane mu qara jin tsoron Allah, haqiqa ikon da Allah yake dashi yafi gaban a misalta.
* Hakika Allah shine mai yadda yaso, kuma ina aywatar da ikon sa cikin hikima a kowanne lokaci.
* duk baiwar da Allah yayi maka, kada kayi izgila. Kada kabari karfin iko ya yaudare ka har ka shiga hurumin Allah Ta'ala, domin haqiqa Allah bazai kyale ba.
* Duk kuncin da kake ciki, ka miqa lamuranka ga Allah Ta'ala. Idan lokacin da hukuncinsa yayi, babu makawa sai ya auku.
* ya 'yanuwa, haqiqa muna zaluntar kawunanmu a wannan zamani ya yadda muke qasqanta darajar ilimi da ma'abota ilimi, muke kuma ganin dukiya da muqami sune qololuwa a rayuwa. To dai dayake ance Gaskiya daci gareta, ya kamata mu sanar da kanmu cewa wannan tunani na halaka ne. Ya kamata mu sanar da kawunan mu gaskiya tun kafin wani ya sanart mana.. Shi Ilimi ai yafi dukiya, Manyan malamai duk sun sanar da haka, don haka shi yafi buqatuwa mu nema sama da duk wata daukaka ko matsayi.
Ku tuna dai, wani masani yana cewa a waqe "Duk daukakar da ba'a sameta ta hanyar ilimi ba, qarshenta qasqanci ne. Idan shugaba ya zamo mai ilimi, ilimin na zamar masa riga qasaitatta da kuma fitila mai jagoranci."
Sai mun hadu a wani sabon shirin na GASKIYA DACI GARETA tare da Sadiq Tukur Gwarzo.
Shiri na daya (1).
LABARIN SARKI SIBANA DA GIMBIYARSA SULBANIYA
Tare da Sadiq Tukur Gwarzo
08060869978
Ance Sarki sibana wani shahararren sarki ne kuma qasaitacce daga cikin rukunin sarakunan da suka mulki Birnin Andaluz, dadaddiyar masarautar da a wani zamani can daya gabata mulkinta ya kusan game ko ina a sassan duniya.
Shidai wannan sarki, tarihi ya nuna asalinsa baiyi gadon sarauta ba, ba kuma wani Kakkarfan jarumi bane, wannan ne babban abin mamaki alokacin jahiliyya har ace wani wanda bai hada wadancan biyun ba ya zamo sarki, alhali lokacin rayuwa ce kwatankwacin ta dabbobi, mai qarfi shine a sama, sarauta da shugabanci ko wanne iri ne gida ko ace zuriya yake bi, wato idan akace wane shine shugaba kaza, tofa shekaru aru-aru masu zuwa zaka samu cewar zuriyarsa ce ke riqe wannan kambun.
Sibana dai kafin zamowarsa Sarki, ance masani ne amma fa matalauci naqin qarawa tun alokacin da sani bai wadata ba kuma arziki bai zamo ruwan dare ba, masanin dalasumai ne; wasu kalmomi da ake ta'allaqa su da wasu halittu wadanda ido baya iya gani, masanin hukunci ne, mai kamanta adalci ne, kuma gwanin tsara magana ne. Sannan kuma an haqqaqe cewar yana cikin sahun wasu mutane da akewa kallon gida-dawa a wancan lokacin, wadanda suke neman buqatunsu a wurin Allah. Idan zasuyi alqawari, bada shaida ko tawassali don samun wata buqata, sunayi ne da Allah wanda sukayi imanin al'arshinsa yana sama, duk da cewa a lokacin akwai qarancin ilimin wanene Allah.
Wata rana sibana yayi mafarki ana masa magana da wata sassanyar murya, ana cewa "ya kai wannan mutum, haqiqa Allah yayi maka baiwar ilimi da hikima, abinda tsiraru acikin bayinsa ne suke dashi. Allah ya fifita taka fiye da yawa-yawan mutanen wannan alqarya. Don haka lokaci ya gabato wanda Allah zai daukaka ka da ilimin ka, ba bisa ga abinda kayi gado ba, ba kuma bisa ga wata bajinta da kayiwa al'umma ba, sannan zai qasqantar da jahilai bisa ga abinda suka dade suna aikatawa na munanci ga Allah.
Ya kai wannan mutum, kayi shiga irin ta qasqantattun mutane kanufi Fada gobe, kasanar da sarki cewar zaka bashi amsar tambayar sa, zaka sanar dashi aikin da Allah yake aiwatarwa da hannunsa tare da qwararan hujjoji matsawar ya yarda da sharadin zai baka kayansa na sarauta, zai sanya naka, zaka hau kan karagarsa kuma dole kowa yayi maka biyayya sannan zaka fadi amsar.
Ya kai wannan mutum, kayi sani cewa daga nan mulki ya dawo gareka. Ka sanar da mutane hukuncin Allah da ikonsa wajen daukaka qasqantacce da qasqantar da daukakakke yafi ga haka, kayi mulki kuma da gaskiya da adalci. Haqiqa zaka dauwama acikib mulki, zaka samu duk cikar burikanka matsawar baka fara gaggawar yanke hukunci acikin lamurorin kaba, sannan matsawar fushi bai zamo yana tunkudaka aikata munanan aiyuka ba.." Yana zuwa nan ne ya farga afujajan.
Farkawar sa keda wuya ya samu kansa yana maimaita maganganun da aka sanar dashi. Babu abinda ya mance kai kace gar-da-gar aka sanar dashi wadannan zantuka. Tunani ya mamaye shi, ya rasa abinyi. Anan ne ma yake fahimtar ashe gari ya waye, rana ta take.
Yana cikin wannan hali ne kuma ya jiyo San kira yana shela a gari yana cewa "yaku mutanen wannan alqarya, Sarki Alkandaruz yana sanya muku albarka, yace asanar daku, bai daukewa kowa ba halartar taron daurin aurensa gobe a fada da gimbiya Sulbaniya ba, sannan yace asanar daku ya tanaji babban muqami da tarin dukiya ga duk wanda yazo masa da amsar da daddiyar tambayarsa gagara amso. Abinda kawai akeso shine, kafadi aikin da Allah yake aikatawa da hannunsa, ka kuma kawo hujjoji qwarara tare da inda ka same su."
Wannan abu ya qara dagawa sibana hankali, wato dai lamarin mafarkin sa akwai wani sirri acikinsa. Sai dai abin da ke bashi tsoro shine tayaya zai iya gaskata mafarkin? Idan dai sibana bai manta ba, a shekarar data gabata, sarki ya hallaka kimanin mutane talatin wadanda suka zo da zummar amsa wannan hatsabibiyar tambaya tashi. Daman shardin tambayar kenan, duk wanda baiciba, ajalinsa yazo kenan. Idan mutum yazo da amsa, sarki zai amsa, sai kuma yace kawo hujjoji da kuma inda kasamo wannan amsa. Tofa ana ake yinta. Saboda mafiyawan mutane shaci fadi kurum sukeyi, tunda alokacin kan mutane bai waye da ilimin saukakkun littattafai ba, Allah dinma da yawa wai-wai dinsa kurum akeji.
( #Sadiq Tukur Gwarzo)
A zahiri, Sibana baiyi niyyar tunkarar Sarki Andaruz da wannan kasada ba. Sarki Andaruz fa jarumin gaske ne, yana da girman jiki, da kwarjini, gashi da qarfin fada aji. Sarakuna ma shakkar sa yake ji, don haka duk abinda yake so ko basa so, ala tilas akeyi masa. Amma kasancewar tunanika da qunci sun yiwa Sibana yawa, sai ya tsinci kansa yana mai cire son rayuwar duniya a ransa, yayi niyyar magance quncin dake ransa ta hanyar kai kansa ga halaka, wataqila zai samu sukuni idan aka hallakashi. Mafitar daya daukarwa kansa itace, zaibi umarnin da aka bashi a mafarki, in yaso sarki ya kashe shi ya huta da zullumi gami da quncin rayuwar daya ke fama dashi.
Kamar yadda aka buqata kuwa, fadar Sarki Alkandaruz tayi cikar kwari. Daman qasaitacciyar fada ce mai cike da gine-gine dogaye. Sarki yana can saman wata husumiya akan karagarsa. A qasan sa kuma manyan waziransa ne da wasu sarakuna wadanda aka gayyato domin shaida daurin auren Sarki da Gimbiya. Kasancewar Sarki yana matuqar qaunar gimbiya sulbaniya yasanya shi cikin annushuwa a wannan rana da zai aureta. Dariya kawai yakeyi, kyauta yakeyiwa bayi sai kace ruwan sama, gashi can akaraga yasha fararen tufafi masu tsada masu dauke da ado na jan jauhari da lu'u-lu'u.
(#Sadiq Tukur Gwarzo)
Kamar yadda aka tsara, za'ayi shela ne har sau uku. Idan an samu wanda yazo ya baiwa sarki amsar tambayarsa, to sai a gabatar dashi a gaban sarki. Idan kuwa ba'a samu ba, shikenan sai a daura auren sarki da gimbiya daga nan kuma ashiga sahun shagulgulan biki. Don haka mai shela ya fara shela. Yayi kira da murya kakkarfa, yayi kirari ga sarki, ya yabi gimbiya, sannan ya nemi duk wanda yazo da amsar tambaya ya matso, yana mai koda kyaututtukan da sarki yayiwa duk wanda ya dace tanaji.. Sarki zai baka babban wazirinsa, zai baka damar tattara harajin duk masarautun dake qarqashin ikon sa, zai aura masa aure da mata dari, zai bashi katafaren gida.. Dadai sauransu.
Mai shela ya qara yin shela akaro na biyu, amma wurin nan tsit kakeji. Talakawa duk sun shiga taitayinsu, kunsan ance wargi wuri yaka samu. Qwaqqwaran motsi ma bakaji, kai kace cewa akayi duk wanda ya motsa abakacin rayuwarsa ne. A karo na uku ma mai shela ya qara yin shela wanda bai rufe baki ba sai ga Sibana kwaram-kwaram yana sanye da tufafi yagaggu, ga kayan hauka nan rakwacan sanye ajikin sa. Ya nufi husumiyar Sarki kai tsaye, kwachachaf-kwachachaf kawai kaceji kai kace shine maigirma Sarkin mahaukata na duk duniya.
Dakarun sarki sukayi kansa asukwane saboda ko ina sune dauke da takubba gayawa jini na wuce, wasu kuma riqe da kibau, harda masu majaujawa. Suka sha gabansa, babban su ya daka masa tsawa yace kai mahaukaci, a fadar Sarkin sarakuna kake ka natsu. Sibana ya daga kansa yana mai dubansa ba tare da tsoro a tare dashi ba yace "Ni ba mahaukaci bane, kuma amsa nazo nabaiwa sarki. Kayi sani cewa Karshen tababa da zubda jinin jahilai yazo, kuma lokacin da gaskiya zatayi halinta ya tabbata. Don haka ka sanar da Sarki cewa duk abinda yakeso ya sani lokacin sa yazo, zan bashi amsa ba kuma naneman abiya da da wata kyauta amma fa sai idan har zai iya cika sharuddai na guda uku dazan ambata".
Sarki ya qyaqyace da dariya, ya buga qafa qasa cikin annushuwa da qeta da yaji abinda wannan mahaukaci yazo dashi. Yace "ku matso dashi gabana, yazo ya fadi wadannan sharudda, mu kuma munyi alqawarin zamu cika su. Amma fa idan har ya kasa bada amsa, to da sannu zansa ayi gunduwa-gunduwa da sassan jikinsa". Sibana ya tsaya a gaban Sarki bayan dakaru sun gabatar dashi, sannan ya fara magana da cewa "ya kai Maigirma sarki wanda sarautarsa ta fadada, ikonsa ya shiga duniya, kai ne sarki mafi qarfin iko a duniya. Kasani cewa bana neman wata kyauta abisa amsar tambayarka dazan bayar. Sharudda kurum nakeso kacika. Na farko, zamuyi musanyen kaya dani-dakai. Na biyu zaka dawo nan inda nake, nikuma zan zauna a inda kake. Na uku kuma dakarunka zasuyi biyayya agareni. Idan har ka amince, to ina maka albishir da samun cikakkiyar biyan buqatarka agareni"
(#Sadiq Tukur Gwarzo)
Ko kadan Sarki bai dauki wadannan sharudda abisa wasu abubuwa masu sharadi ba, don haka nan take ya amince. Abinda yake hangowa kawai shine zai taya bera bari ne, wato zai qure qaryar wannan mahaukaci inyaso sai ya gallaza maza da azaba mafi muni, tayadda al'ummarsa zata qara jin tsoronsa. Da yake kuma Sarki ne wanda yake sa gabansa aduk inda yakeso, sai ya kasance babu daga cikin wazirinsa wanda yace maza kanzil akan cika wadannan sharudda.
Sibana ya zauna akan karagar sarki. A halin yanzu shine Sarki, domin kuwa duk dakarun sarki umarninsa suke jira ba umarnin Sarki Ankaldaruz ba. Sibana ya dubi taron jama'a yace "yaku jama'ar Andaluz dame nayi kama yanzu??? Mutane suka dauka gaba daya da cewa "da sarkiiiii". Ya qara cewa "wannan fa damai yayi kama?" Yana mai nuni da sarki Alkandaruz? Mutane suka qara cewa "da mahaukaci". Sai ya kalli Sarki Alkandaruz yace " wannan shine aikin da Allah mai iko ya aiwatar da hannunsa yanzu-yanzu. Sarki ya zamo mahaukaci, mahaukaci ya zamo Sabon Sarki." (#Sadiq Tukur Gwarzo)
Sarki Alkandaruz yayi tsaki, ransa ya baci saboda abin kamar yazo masa da qasqanci. Sannan ya dubi Sibana yace "to yi sauri ka cire kayannan ka dawo nan, wadannan kayan sun. Isheni da tsami. Sannan kuma idan ka kasa bani hujjar maganar ka da inda ka samo amsar na rantse sai na lahira ya fika jin dadi". Da fadin haka sai yayi kan karagar da nufin ya hankade sibana da qarfin tsiya. Ai kuwa nan take sibana ya dakawa dakaru tsawa, yace ku kama shi kuyi maza ku kai mini shi kurkuku. Ai duk wanda yake son zurfafa bincike acikin lamarin Allah hauka da qasqanci ne makomar sa" Aikuwa ala dole, suka amshi umarnin sabon sarki, tsohon sarki tun yana ashariya, har ya dawo yana magiya, amma ina, bakin alqalami ya bushe. Anan take ya fara fahimtar kuskurensa. (#Sadiq Tukur Gwarzo)
Sabon Sarki yayi jawabi mai ratsa jiki ga al'umma, yayi musu nasiha da gaskiya, adalci gami da zama lafiya. Daga nan kuma aka dauka aurensu da gimbiya Sulbaniya..
Wannan shine matashiyar wannan labari..
Darussan dake shirin GASKIYA DACI GARETA na wannan lokaci sune;
*Ya kamata mutane mu qara jin tsoron Allah, haqiqa ikon da Allah yake dashi yafi gaban a misalta.
* Hakika Allah shine mai yadda yaso, kuma ina aywatar da ikon sa cikin hikima a kowanne lokaci.
* duk baiwar da Allah yayi maka, kada kayi izgila. Kada kabari karfin iko ya yaudare ka har ka shiga hurumin Allah Ta'ala, domin haqiqa Allah bazai kyale ba.
* Duk kuncin da kake ciki, ka miqa lamuranka ga Allah Ta'ala. Idan lokacin da hukuncinsa yayi, babu makawa sai ya auku.
* ya 'yanuwa, haqiqa muna zaluntar kawunanmu a wannan zamani ya yadda muke qasqanta darajar ilimi da ma'abota ilimi, muke kuma ganin dukiya da muqami sune qololuwa a rayuwa. To dai dayake ance Gaskiya daci gareta, ya kamata mu sanar da kanmu cewa wannan tunani na halaka ne. Ya kamata mu sanar da kawunan mu gaskiya tun kafin wani ya sanart mana.. Shi Ilimi ai yafi dukiya, Manyan malamai duk sun sanar da haka, don haka shi yafi buqatuwa mu nema sama da duk wata daukaka ko matsayi.
Ku tuna dai, wani masani yana cewa a waqe "Duk daukakar da ba'a sameta ta hanyar ilimi ba, qarshenta qasqanci ne. Idan shugaba ya zamo mai ilimi, ilimin na zamar masa riga qasaitatta da kuma fitila mai jagoranci."
Sai mun hadu a wani sabon shirin na GASKIYA DACI GARETA tare da Sadiq Tukur Gwarzo.
No comments:
Post a Comment